ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, December 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

ISWAP Ta Kashe Jami’ai 8 A Wani Sabon Hari A Borno

by Sulaiman
1 month ago
ISWAP

An kashe akalla jami’ai hudu na rundunar hadin gwiwa ta farar hula (CJTF) da ma’aikata hudu da ke aiki a Ma’aikatar Gine-gine, Gyara da Matsugunni ta Jihar Borno (RRR) a wani sabon hari mai muni da ‘yan ta’addan Boko Haram/ISWAP suka kai a garin Mayenti da ke karamar hukumar Bama a jihar.

 

LEADERSHIP ta ruwaito cewa, harin ya faru ne a ranar Litinin, sa’o’i bayan da Babban Hafsan Sojan Sama (CAS), Air Marshal Sunday Kelvin Aneke, ya ziyarci Maiduguri a rangadin aikinsa na farko zuwa sansanin ayyukan yaki da ta’addanci na a arewa maso gabas na rundunar sajin sama.

ADVERTISEMENT

 

An kashe sojoji biyu da jami’ai biyu na CJTF a ranar Juma’a lokacin da ‘yan ta’addan suka yi wa sojojin rundunar hadin gwiwa ta ‘Operation Hadin Kai’ kwanton ɓauna a wani sintiri da rundunar ke yi a kullum a Wajiroko da ke Azir Multe a karamar hukumar Damboa ta jihar Borno.

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

 

Mayenti, inda harin ya faru, yana da nisan kilomita kaɗan daga Darajamal da ke Bama inda ‘yan ta’addan, watanni da suka gabata, suka kashe mutane sama da 60, ciki har da sojoji biyar tare da kone gidaje da dama.

 

Majiyoyin leƙen asiri masu inganci sun ce ‘yan ta’addan sun kai hari kan al’umma da babura da motocin yaƙi a wani yunƙuri na mamaye sansanin sojojin da ke wurin.

 

Majiyoyin sun ce, duk da cewa sojoji sun yi nasarar dakile maharan, amma artabun ya yi sanadiyyar mutuwar jami’an tsaro huɗu na sa kai waɗanda ke gadin garin.

 

Haka kuma, an ruwaito cewa sojoji huɗu sun ɓace a lokacin harin, kuma har yanzu ba a san inda suke ba.

 

‘Yan ta’addan, yayin da suke guduwa da gawarwakin mayakansu a cewar majiyar, sun ƙone manyan motoci biyu mallakar Ma’aikatar RRR, sannan suka kashe ma’aikata huɗu da ke aiki a yankin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja
Manyan Labarai

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta
Manyan Labarai

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Next Post
Babban Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Yaki Na Fujian Ya Gudanar Da Atisayen Dakaru Na Farko A Teku

Babban Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Yaki Na Fujian Ya Gudanar Da Atisayen Dakaru Na Farko A Teku

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.