• English
  • Business News
Friday, October 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jajircewa Ce Sirrin Samun Daukakata A Masana’antar Kannywood -Sadik Sani Sadik

by Rabilu Sanusi Bena and Sulaiman
7 months ago
Sadik Sani

Daya daga cikin jaruman fina-finan da ludayinsu ke kan dawo Sadik Sani Sadik ya bayyana batutuwa game da rayuwarshi ta yau da kullum da kuma ta fim, inda ya ce bayan harkar fim ya na ware wani lokaci da yake motsa jiki musamman taka leda, don kamar yadda yace dole ne jarumin fim ya kasance ya na motsa jiki domin samun lsashshiyar lafiya da za ta taimaka mashi.

Sadik wanda ya kasance jarumin masana’antar Kannywood tsawon lokaci, ya yi waiwaye dangane da gwagwarmayar da yayi kafin ya zamo abinda ya zama a halin yanzu, inda ya ce daga cikin sana’oin da ya yi kafin yanzu akwai bunburutu, kwadago da sauran tallace-tallace domin kawai a rufawa kai asiri.

  • Halayen Kirki 14 Da Ake Bukata Daga Malamin Makaranta (3)
  • Nazarin CGTN: Kasar Sin Na Bayar Da Gudunmuwa Wajen Warware Batun Nukiliyar Iran

Harkar fim ta yi mani riga da wando saboda ta sanadinta na samu alherai da dama, wanda yanzu nafi karfin abubuwa da dama kama daga abin da zan ci, tufafin da zan saka, motar da zan hau da gidan da zan zauna duka na mallake su sakamakon wannan harka ta fim, haka ya sa nike matukar alfahari da ita in ji Sadik a wata hira da ya yi da DW Hausa.

Da yake amsa tambaya a kan yadda yake mayar da martani a matsayinsa na jarumi a shafukan sada zumunta yayin da wasu su ka yi mashi abin da ya sosa mashi zuciya, jarumin ya ce galibi idan na dora wani abu a shafukana na sada zumunta ba lallai ba ne in koma kan abinda mutane ke fadi, muddin sakon da nike son in isar ya tafi inda nike bukata to shikenan bukata ta biya.

Akan burin da yake fatan cimma a rayuwa, jarumin dan asalin birnin Jos ta jahar Filato ya ce kowane dan adam yanada burika da yake son cimma kafin mutuwa, to amma shi dai ya cika wasu daga cikin burikansa na rayuwa duk da cewar zuwa gaba idan da hali ya na fatan watarana zai shiga siyasa har ma ya fito takarar gwamnan Jihar Filato.

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Aike Da Ɗan TikTok Gidan Gyaran Hali Kan Bidiyon Batsa A Kano

An Nada Adamar Kamaye Sarautar Jakadiya A Kasar Ghana

Abinda ya sa nike fatan ganin na zama gwamna shi ne saboda banida wani burin da ya wuce in ga cewar matsalar tsaro ta kau a Nijeriya musamman Arewacin kasar inda wasu ke wasa da rayukan al’umma saboda wata bukata ta kashin kansu, wasu tsiraru na amfani da rayukan mutane a matsayin kasuwanci ko kuma don neman daukaka ya kara da cewa.

A ci gaba da hirar Sadik ya amsa tambayar da aka yi mashi a kan fina-finan da yayi da kuma wadanda yake kallo a matsayin wanda yafi so a cikinsu, inda ya ce daga cikin fina-finan da ya fito wadanda kuma yafi so, akwai Mati Da Lado sai kuma wani fim mai suna Dan Marayan Zaki.

Abinda ya sa nafi son wadannan fina finai shi ne ba don komai ba sai don kawai su na daya daga cikin ayyukan da nafi wahala kuma na kara samun gogewa a wannan sana’a tawa, hakazalika su ne fina-finan da aka fara sanina dasu kuma aka fara sanin wanene Sadik Sani Sadik da kuma abinda zan iya yi idan aka dora mani kyamara.

Daga karshe Sadik ya bayyana sirrin samun daukakarshi a masana’antar Kannywood, da cewa ba komai bane ya sa ya samu daukaka illa addu’ar iyaye da kuma jajircewa saboda na dauki harkar fim a matsayin babbar sana’ar da na dogara da ita yanzu, kuma nike rufawa kaina asiri.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kotu Ta Aike Da Ɗan TikTok Gidan Gyaran Hali Kan Bidiyon Batsa A Kano
Nishadi

Kotu Ta Aike Da Ɗan TikTok Gidan Gyaran Hali Kan Bidiyon Batsa A Kano

October 6, 2025
An Nada Adamar Kamaye Sarautar Jakadiya A Kasar Ghana
Nishadi

An Nada Adamar Kamaye Sarautar Jakadiya A Kasar Ghana

October 4, 2025
Daga Kallon Fina-finan Indiya Na Samu Sha’awar Fadawa Kannywood – Kamalu Mijinyawa
Nishadi

Daga Kallon Fina-finan Indiya Na Samu Sha’awar Fadawa Kannywood – Kamalu Mijinyawa

September 28, 2025
Next Post
majalisar kasa

Nijeriyar Jiya Da Yau: Kiki-Kakar Sabgar 'Yan Majalisu

LABARAI MASU NASABA

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

October 9, 2025
Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

October 9, 2025
‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

October 9, 2025
Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza

Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza

October 9, 2025
TCN

Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

October 9, 2025
An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

October 9, 2025
Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

October 9, 2025
Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

October 9, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Batun Umarnin Kotu Na Kama Tsohon Shugaban INEC Ƙage Ne Kawai – Shugaban Jam’iyyar AA 

October 9, 2025
An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

October 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.