• English
  • Business News
Friday, October 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jakadan Kasar Sin Ya Bayyana Damuwa Kan Yadda Ake Nuna Bambanci Ga ‘Yan Kananan Kabilu Yayin Da Ake Aiwatar Da Doka A Wasu Kasashe

by CMG Hausa
3 years ago
Kasar Sin

Jiya Talata 4 ga wata, an yi babbar muharawa dangane da batutuwan wariyar launin fata, da nuna kiyayya ga baki, da rashin hakuri, a yayin taron kwamitin kare hakkin dan Adam na MDD karo na 51.

A yayin muhawarar, zaunannen wakilin kasar Sin a ofishin MDD a Geneva da sauran kungiyoyin kasa da kasa a kasar Switzerland Jakada Chen Xu, ya yi jawabi a madadin kasashen da ke da ra’ayi kusan iri daya da na kasar Sin, inda ya nuna matukar damuwa kan yadda ake nuna bambanci, ga ‘yan kananan kabilu, yayin da ake aiwatar da doka a wasu kasashe, ya kuma bukaci kasashe masu ruwa da tsaki da su kalli kansu yadda ya kamata, a fannin mummunar matsalar wariyar launin fata, su yi cikakken bincike, da kyautata hukumominsu, da dokokinsu, da manufofinsu, da matakansu masu nasaba da wariyar launin fata, a kokarin aiwatar da “sanarwa da tsarin ayyuka na Durban” yadda ya kamata.

  • Yadda Wasu Mata 2 Suka Haifi Jarirai Shida-Shida A Yobe

A cikin jawabinsa, Chen Xu ya yi nuni da cewa, yadda hukumomin aiwatar da doka suke nuna bambancin launin fata, da yin amfani da karfin tuwo yayin da suke aiki, sakamako ne da wadannan kasashe suka samu, saboda sun dade suna fama da matsalar wariyar launin fata, da rashin daidaito cikin zamantakewar al’umma bisa tsari, kana matsala ce da ya zuwa yanzu ba su warware ta ba, tun bayan cinikin bayi da mulkin mallaka.

A cikin wadannan kasashe, an dade ana nuna wa ‘yan asalin Afirka, da Asiya, da musulmai, da sauran ‘yan kananan kabilu bambanci, da daukar su mutane marasa muhimmanci, ana kuma keta dokokinsu, kuma ko da yaushe suna fuskantar barazanar cin zarafi.

Cikin jawabinsa, Chen Xu ya yi kira ga kwamitin kare hakkin dan Adam na MDD, da ofishin babbar jami’ar kula da hakkin dan Adam na MDD, da su kara mai da hankali kan batutuwa masu nasaba da wariyar launin fata, da tashin hankali da aka ambato, tare da daukar matakan da suka wajaba na magance hakan. (Tasallah Yuan)

LABARAI MASU NASABA

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo

Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo

October 30, 2025
Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma 
Daga Birnin Sin

Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma 

October 30, 2025
Babban Daraktan Sakatariyar APEC: Sin Tana Ba Da Gudummawar Ba Da Jagoranci A APEC
Daga Birnin Sin

Babban Daraktan Sakatariyar APEC: Sin Tana Ba Da Gudummawar Ba Da Jagoranci A APEC

October 30, 2025
Next Post
Ranar Malamai ta Duniya: Atiku Ya Bukaci A Yi Wa Ilimi Tagomashi

Ranar Malamai ta Duniya: Atiku Ya Bukaci A Yi Wa Ilimi Tagomashi

LABARAI MASU NASABA

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo

October 30, 2025
An Yi Wa Yara Sama Da Miliyan Biyu Allurar Rigakafin Mashaƙo Da Sankarau A Zamfara

An Yi Wa Yara Sama Da Miliyan Biyu Allurar Rigakafin Mashaƙo Da Sankarau A Zamfara

October 30, 2025
Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma 

Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma 

October 30, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Ceto Mutum Ɗaya, Sun Kama Mace Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Dajin Kwara 

October 30, 2025
Babban Daraktan Sakatariyar APEC: Sin Tana Ba Da Gudummawar Ba Da Jagoranci A APEC

Babban Daraktan Sakatariyar APEC: Sin Tana Ba Da Gudummawar Ba Da Jagoranci A APEC

October 30, 2025
Barcelona Na Shirin Ɗauko Victor Osimhen Na Galatasaray

Barcelona Na Shirin Ɗauko Victor Osimhen Na Galatasaray

October 30, 2025
Kasar Sin Ce Ke Da Sama Da Rabin Muhimman Makaloli Na Duniya

Kasar Sin Ce Ke Da Sama Da Rabin Muhimman Makaloli Na Duniya

October 30, 2025
Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai

Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai

October 30, 2025
Bunkasar Fannin Kirkire-Kirkiren Fasahohi Na Sin Alheri Ne Ga Dukkanin Duniya Ba Barazana Ba

Bunkasar Fannin Kirkire-Kirkiren Fasahohi Na Sin Alheri Ne Ga Dukkanin Duniya Ba Barazana Ba

October 30, 2025
Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

October 30, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.