Kwamitin kasa mai lura da kasuwancin Amurka da Sin ko USCBC, ya gudanar da liyafar murna ta shekarar 2025, a ranar Laraba 18 ga wata a birnin Washington na Amurka, liyafar da jakadan kasar Sin a Amurka Xie Feng ya halarta tare da gabatar da jawabi.
Cikin jawabin nasa jakada Xie ya ce cimma moriya da nasara tare, muhimman ginshikai ne na ci gaba mai dorewa na hadin-gwiwar Sin da Amurka ta fuskar raya tattalin arziki da kasuwanci, inda dukkan bangarorin biyu gami da duniya ke cin gajiya. A halin yanzu, habakar tattalin arzikin duniya na tafiyar hawainiya, kuma kara hada kai ita ce mafita daya tilo ta shawo kan hakan. Ya ce ci gaban kasar Sin zarafi ne ga dukkanin duniya baki daya, wato yarda da kasar Sin tamkar yarda da kyakkyawar makoma ne, kuma zuba jari a kasar zai haifar da babbar nasara a nan gaba.
Jakadan ya kara da cewa, dangantakar Sin da Amurka na cikin wani muhimmin lokaci, kana, neman hada kai don cimma moriya tare, ko kuma nuna wa juna kiyayya, hanyoyi ne mabambanta dake gabansu. Don haka ya dace kasashen biyu su tsaya bisa jagorancin shugabanninsu kan manyan tsare-tsare, da aiwatar da muhimman ra’ayoyi iri daya da suka cimma a zahiri. Har kullum kasar Sin na nuna sahihanci amma mai kunshe da sharadi, wato kiyaye cikakken yankin kasa, gami da muradun neman ci gaba, tamkar jan layi ne da ba za a iya tsallakewa ba, yayin da girmama juna, da kiyaye zaman lafiya da samun moriya tare cikin hadin-gwiwa, suka zamo babbar ka’ida da dole a mutunta ta. (Murtala Zhang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp