• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

byRabi'u Ali Indabawa
2 months ago
Jamb

Hukumar Shirya Jarabawar Shiga Makarantun Gaba da Sakandire (JAMB) ta kaddamar da wani kwamitin musamman domin bincikar al’amuran amfani da fasaha wajen yin magudin jarabawa da aka gano a yayin jarabawar UTME ta 2025.

Yayin kaddamar da Kwamitin Musamman Mai Mambobi 23 Kan Laifukan Jarabawa a ranar Litinin a Abuja, Shugaban JAMB, Farfesa Ishak Oloyede, ya nuna damuwa kan kara kwarewar masu magudin jarabawa, inda ya bayyana cewa sakamakon dalibai 6,458 na nan karkashin bincike bisa zargin shiga cikin magudin zamani na fasaha.

  • EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo
  • Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

“Wannan shekarar mun gamu da abubuwa masu ban mamaki da dama, kuma mun ji zai fi kyau idan muka fadada hanyoyinmu. Muna kuma da yakinin cewa Allah ya albarkaci wannan kasa da tarin albarkatu da za mu iya amfana da su,” in ji Oloyede.

Oloyede ya jaddada cewa akwai bukatar daukar gaggawar mataki domin kare ingancin jarabawa.

“Magudin jarabawa wani abu ne da dole mu yi yaki da shi da kowace digon jinin da ke jikimmu,” in ji shi, yana gargadin cewa idan ba a shawo kan wannan matsala ba, zai iya lalata fannoni da dama tare da bata sunan Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

Oloyede ya bayyana cewa an tura al’amuran “na al’ada” guda 141 na magudin jarabawa zuwa ga kwamitin ladabtarwa na JAMB, yana mai kara da cewa wannan sabon kwamiti zai yi aiki da “laifuka na musamman,” irin su hada hotuna (image blending), kirkirar rashin kwayar halitta (albinism falsification), hada yatsu (finger pairing), da kuma kokarin karya tsarin sadarwar Local Area Network na wasu cibiyoyin CBT.

Ya jera ayyukan da aka dora wa kwamitin, wanda suka hada da binciken dukkan al’amuran hada hotuna (image blending), hada yatsu (finger blending), karya da’awar rashin kwayar halitta (albinism) da kuma kirkirar sakamako a jarabawar 2025.

Haka kuma, gano hanyoyi, dabaru, kayan aiki da fasahohin da aka yi amfani da su wajen aikata wadannan laifuka, nazarin manufofin jarabawa da na rajista na yanzu da kuma bayar da shawarwari kan inganta su.

Bugu da kari, an dora wa kwamitin alhakin tantance ko wadanda ake zargi dalibai 6,458, ban da wadanda ke cikin rukuni na albinism, suna da hannu ko a’a, saboda sakamakonsu na nan a dakace.

Kwamitin zai kuma “ba da shawarar hukunci ko ladabtarwa da suka dace ga duk wani mutum ko rukuni da aka samu da laifi.”

“Ku gabatar da tsari mai wayewa domin gano, dakile da kuma hana magudin jarabawa da fasaha ta zamani ke taimakawa a nan gaba.

“Kuma ku yi la’akari ku bayar da shawara kan duk wata matsala da ta shafi wadannan al’amura,” in ji shi.

Kwamitin na da makonni uku bayan kaddamarwa don gabatar da rahoton aikinsa.

“Mun zabi makonni uku ne saboda an ce adalci da aka jinkirta tamkar adalci da aka hana ne.

“A cikin kusan makonni hudu, za a rufe karbar dalibai. Kuma muna ganin wadanda ba a same su da laifi ba su sami damar su,” in ji Oloyede.

Shugaban Kwamitin, Dakta Jake Epele, ya yaba da jagorancin Oloyede tare da yin alkawarin cewa kwamitin zai yi aiki tukuru wajen cika wannan aiki.

Mambobin kwamitin sun hada da Farfesa Muhammad Bello, Farfesa Samuel Odewummi, Farfesa Chinedum Nwajiuba, Farfesa Tanko Ishaya, Farfesa Ibe Ifeakandu, Tsohon Kwamishinan ‘Yansanda Fatai Owoseni, Dakta Chuks Okpaka na Microsoft Africa, da Shugaban Kungiyar Daliban Nijeriya (NANS), tare da wasu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

A Kama Wani Likitan Bogi A Neja
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno
Labarai

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Next Post
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version