ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 21, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

by Rabi'u Ali Indabawa
10 months ago
Jamb

Hukumar Shirya Jarabawar Shiga Makarantun Gaba da Sakandire (JAMB) ta kaddamar da wani kwamitin musamman domin bincikar al’amuran amfani da fasaha wajen yin magudin jarabawa da aka gano a yayin jarabawar UTME ta 2025.

Yayin kaddamar da Kwamitin Musamman Mai Mambobi 23 Kan Laifukan Jarabawa a ranar Litinin a Abuja, Shugaban JAMB, Farfesa Ishak Oloyede, ya nuna damuwa kan kara kwarewar masu magudin jarabawa, inda ya bayyana cewa sakamakon dalibai 6,458 na nan karkashin bincike bisa zargin shiga cikin magudin zamani na fasaha.

  • EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo
  • Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

“Wannan shekarar mun gamu da abubuwa masu ban mamaki da dama, kuma mun ji zai fi kyau idan muka fadada hanyoyinmu. Muna kuma da yakinin cewa Allah ya albarkaci wannan kasa da tarin albarkatu da za mu iya amfana da su,” in ji Oloyede.

ADVERTISEMENT

Oloyede ya jaddada cewa akwai bukatar daukar gaggawar mataki domin kare ingancin jarabawa.

“Magudin jarabawa wani abu ne da dole mu yi yaki da shi da kowace digon jinin da ke jikimmu,” in ji shi, yana gargadin cewa idan ba a shawo kan wannan matsala ba, zai iya lalata fannoni da dama tare da bata sunan Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Hijira: Malaman Musulunci Sun Buƙaci  Musulmi Su Yi Riƙo Da Gaskiya Da Adalci

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

Oloyede ya bayyana cewa an tura al’amuran “na al’ada” guda 141 na magudin jarabawa zuwa ga kwamitin ladabtarwa na JAMB, yana mai kara da cewa wannan sabon kwamiti zai yi aiki da “laifuka na musamman,” irin su hada hotuna (image blending), kirkirar rashin kwayar halitta (albinism falsification), hada yatsu (finger pairing), da kuma kokarin karya tsarin sadarwar Local Area Network na wasu cibiyoyin CBT.

Ya jera ayyukan da aka dora wa kwamitin, wanda suka hada da binciken dukkan al’amuran hada hotuna (image blending), hada yatsu (finger blending), karya da’awar rashin kwayar halitta (albinism) da kuma kirkirar sakamako a jarabawar 2025.

Haka kuma, gano hanyoyi, dabaru, kayan aiki da fasahohin da aka yi amfani da su wajen aikata wadannan laifuka, nazarin manufofin jarabawa da na rajista na yanzu da kuma bayar da shawarwari kan inganta su.

Bugu da kari, an dora wa kwamitin alhakin tantance ko wadanda ake zargi dalibai 6,458, ban da wadanda ke cikin rukuni na albinism, suna da hannu ko a’a, saboda sakamakonsu na nan a dakace.

Kwamitin zai kuma “ba da shawarar hukunci ko ladabtarwa da suka dace ga duk wani mutum ko rukuni da aka samu da laifi.”

“Ku gabatar da tsari mai wayewa domin gano, dakile da kuma hana magudin jarabawa da fasaha ta zamani ke taimakawa a nan gaba.

“Kuma ku yi la’akari ku bayar da shawara kan duk wata matsala da ta shafi wadannan al’amura,” in ji shi.

Kwamitin na da makonni uku bayan kaddamarwa don gabatar da rahoton aikinsa.

“Mun zabi makonni uku ne saboda an ce adalci da aka jinkirta tamkar adalci da aka hana ne.

“A cikin kusan makonni hudu, za a rufe karbar dalibai. Kuma muna ganin wadanda ba a same su da laifi ba su sami damar su,” in ji Oloyede.

Shugaban Kwamitin, Dakta Jake Epele, ya yaba da jagorancin Oloyede tare da yin alkawarin cewa kwamitin zai yi aiki tukuru wajen cika wannan aiki.

Mambobin kwamitin sun hada da Farfesa Muhammad Bello, Farfesa Samuel Odewummi, Farfesa Chinedum Nwajiuba, Farfesa Tanko Ishaya, Farfesa Ibe Ifeakandu, Tsohon Kwamishinan ‘Yansanda Fatai Owoseni, Dakta Chuks Okpaka na Microsoft Africa, da Shugaban Kungiyar Daliban Nijeriya (NANS), tare da wasu.

Jamb
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    ‘Ƴan Bindiga Sun Hana Manoman Sakkwato Zuwa Gonakinsu, Sun Ƙaƙaba Sabbin Haraji
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Matsalar Tsaro:Kashi 60 Na Masana’antu A Arewa Maso Gabas Sun Durƙushe

MASU ALAKA

Darussan Da Suka Fi Dacewa A Fahimta Daga Alkur’ani A Wannan Zamanin (2)
Labarai

Hijira: Malaman Musulunci Sun Buƙaci  Musulmi Su Yi Riƙo Da Gaskiya Da Adalci

June 20, 2026
Nijeriya
Rahotonni

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Sojoji Sun Kashe Mayakan Boko Haram 6, Sun Kama Wasu A Borno
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Mutane 22 A Jihar Sakkwato

June 20, 2026
Next Post
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Wasa 23 Da Eric Chelle Ya Gayyata Domin Buga Wasannin Sada Zumunci 

Duk Da Rashin Halartar ‘Super Eagles’ Gasar Kofin Duniya, Nijeriya Ba Ta Rasa Wakilai Ba

June 20, 2026
Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin

Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin

June 20, 2026
Darussan Da Suka Fi Dacewa A Fahimta Daga Alkur’ani A Wannan Zamanin (2)

Hijira: Malaman Musulunci Sun Buƙaci  Musulmi Su Yi Riƙo Da Gaskiya Da Adalci

June 20, 2026
Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire

Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire

June 20, 2026
Nijeriya

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Sin Na Kira Ga Al’ummun Kasa Da Kasa Da Su Himmatu Wajen Tallafawa Ayyukan Jin kai

Sin Na Kira Ga Al’ummun Kasa Da Kasa Da Su Himmatu Wajen Tallafawa Ayyukan Jin kai

June 20, 2026
Sojoji Sun Kashe Mayakan Boko Haram 6, Sun Kama Wasu A Borno

Sojoji Sun Ceto Mutane 22 A Jihar Sakkwato

June 20, 2026
A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki

A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki

June 20, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

June 20, 2026
IMF

Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

June 20, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.