• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jami’ar Edo Ta Kori Ma’aikata 5, Wasu 21 Na Fuskantar Bincike Kan Aikata Manyan Laifuka

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Jami’ar Edo Ta Kori Ma’aikata 5, Wasu 21 Na Fuskantar Bincike Kan Aikata Manyan Laifuka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Gudanarwar Jami’ar Edo mallakin gwamnatin jihar, Ambrose Alli University (AAU), Ekpoma, ta kori ma’aikata guda biyar yayin da wasu 21 suke kan fuskantar bincike kan zargin aikata manyan laifuka daban-daban.

Mamba a kwamitin musamman (SIT), Austin Osakure, yayin da ke mika rahoton ayyukan SIT ga gwamna Godwin Obaseki a gidan gwamnati da ke Benin, ya shaida cewar ma’aikatan an koresu ne bisa la’akari da rahoton kwamitin da’a da ladaftarwa ta jami’ar.

  • Hazikan Daliban Kano Za Su Samu Gurbin Karatu Kyauta A Jami’ar CCU – Dakta Salwa

Osakure, ya bukaci gwamnatin Edo da ta kafa majalisar koli ta gudanarwar jami’ar AAU, tare da daukan manyan jami’ai na jami’ar, ya lura kan cewa zuwa yanzu ba a yabawa ko gamsuwa da ayyukan kwamitin SIT, sai ya ce, ko kuma a sabunta ko yin nazari kan dokokin jami’ar domin kyautata lamuranta.

Ya shaida cewar jami’ar AAU ta bi umarnin gwamnatin jihar Edo wajen shiga cikin taimakekeniyar kiwon lafiya da ya fara aiki a ranar 1 ga watan Agustan 2023.

Mamban ya ce, “Dukkanin ma’aikatan jami’ar AAU da suke da sauran shekaru bakwai su kammala aiki an barsu ba su cikin shirin.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

“Tsarin inshuran kiwon lafiya ta Edo na gudana yadda ya dace saboda ana biyan kudin ne kai tsaye ta asusun EdoHIS, domin tabbatar da gaskiya da adalci.

“Dalibai 998 sun shiga shirin, da sama da naira miliyan 15, da kuma ma’aikata 1,800 da sama da naira miliyan 31.

“Jami’ar ta gano kesa-kesai sama da 30 na dalibai ‘yan kasashen waje a cikin shekaru kasa da biyu, sun zana jarabawa har ma an yayesu. Ma’aikata da shugabannin tsangayoyin da suke da hannu a wannan lamarin an mika su ga jami’an hukumar tsaro ta farin kaya DSS da ICPC domin daukan mataki na gaba.”

Mamban ya bayyana wa gwamnan cewar akwai tsare-tsare da dama wadanda suke tafiya a jami’ar da suke bukatar gaggawan kawo dauki da sauyi domin bunkasa harkokin jami’ar.

A jawabinsa, gwamnan jihar, Godwin Obaseki, ya ce, gwamnatinsa za ta tabbatar da dawo da martaba da kimar jami’ar AAU, kuma nan kusa za a samu sauye-sauye masu matukar fa’ida.

Obaseki ya ce, “Muna son mu magance matsalolin makarantar,” ya tabbatar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ranar Yaki Da Cizon Sauro: Majalisa Ta Bukaci Gwamnati Ta Ayyana Dokar Ta-baci Kan Malaria

Next Post

Dandalin Kafofin Watsa Labarai Na BRICS Karo Na 6 Ya Yi Kira Da A Karfafa Muryoyin Kasashe Masu Tasowa

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

2 hours ago
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna
Labarai

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

3 hours ago
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu
Manyan Labarai

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

4 hours ago
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya
Labarai

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

5 hours ago
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF
Manyan Labarai

Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

7 hours ago
Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike
Manyan Labarai

Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

9 hours ago
Next Post
Dandalin Kafofin Watsa Labarai Na BRICS Karo Na 6 Ya Yi Kira Da A Karfafa Muryoyin Kasashe Masu Tasowa

Dandalin Kafofin Watsa Labarai Na BRICS Karo Na 6 Ya Yi Kira Da A Karfafa Muryoyin Kasashe Masu Tasowa

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.