• English
  • Business News
Monday, June 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jami’ar Tarayya Ta FUGA Ta Kirkiro Da Injin Kyankyasar ‘Yan Tsaki

by Sulaiman
1 month ago
in Labarai
0
Jami’ar Tarayya Ta FUGA Ta Kirkiro Da Injin Kyankyasar ‘Yan Tsaki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jami’ar Tarayya ta garin Gashua (FUGA), ta samu gagarumar nasara a kokarin da take yi na bunkasa fannin aikin noma.

 

Ta samu wannan nasara ce, biyo bayan sashen bunkasa kimiyyar dabbobi ta Jami’ar ya samu nasarar kaddamar da injin kyankyasar ‘yan Tsaki na zamani.

  • Tanzaniya Ta Yi Maraba Da Zuwan Tawagogin Yawon Shakatawa Na Sin
  • Har Yanzu Manyan ‘Yan Wasa Suna Son Buga Wasa A Manchester United – Amorim

A cikin sanarwar da shugaban sashen samar da bayanai na Jami’ar, Mallam Asamu Saleh ya fitar ya bayyana cewa; kaddamar da injin kyankyasar, tamkar ya bude wani sabon babi ne ga sashen na bunkasa kimiyyar dabbobi na Jami’ar.

 

Labarai Masu Nasaba

Shugabannin Duniya Za Su Gudanar Da Taron Sanya Hannun Jarin Bunƙasa Ƙudurorin Muradun Ƙarni A Sifaniya

Matatar Dangote Za Ta Fara Dakon Man Fetur Da Dizal Kyauta A Fadin Nijeriya

Saleh ya ce, kaddamar da injin kyankyasar, musamman saboda jajircewar ma’aikatan sashen kan wannan aiki, tuni Jami’ar ta fara ganin sakamako mai kyau.

 

Ya kara da cewa, samar da wannan inji, ya kara nuna irin mayar da hankali da Jami’ar ta yi, wajen habaka fannin aikin noma ta hanyar amfani da kimiyyar zamani da kuma samar wa daliban fannin kimiyyar Jami’ar kayan aikin zamani da za su rika gudanar da ilimin yin gwaje-gwaje da kuma bayar da gudunmawa wajen kara samar da wadataccen abinci a kasar.

 

Kazalika, wannan nasara ta kuma nuna a zahiri irin kyakkyawan shugabancin Shugabar Jami’ar, Farfesa Maimuna Waziri, duba da irin kokarinta na dora Jami’ar a kan turba mai dorewa, musamman a bangaren samar da fasahar kirkire-kirkire a fannin aikin noma.

 

Shi kuwa, a nasa martanin, shugaban sashen bunkasa kimiyyar dabbobi na Jami’ar, Dakta Lawan Adamu ya bayyana cewa; an faro aikin samar da injin kyankyasar ‘yan Tsakin ne, a lokacin shugabancin Tsohon Shugaban Jami’ar, Farfesa Andrew Haruna.

 

Ya sanar da cewa, sai dai ba a fara amfani da injin ba, sai a lokacin shugabancin Shugabar Jami’ar ta yanzu, Farfesa Maimuna Waziri, wadda kuma ta kara mayar da hankali wajen ganin an kammala aikin injin, domin amfanin daliban sashen bunkasa kimiyyar dabbobin, domin su fara gudanar da gwaje-gwaje a kanta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ambaliya: Yankunan Da Ba Za Su Yi Noma A Kakar Bana Ba A Jihar Neja

Next Post

Dakataccen Gwamnan Ribas Ya Dawo Daga Hutun Makonni Biyu A Kasar Waje

Related

Shugabannin Duniya Za Su Gudanar Da Taron Sanya Hannun Jarin Bunƙasa Ƙudurorin Muradun Ƙarni A Sifaniya
Labarai

Shugabannin Duniya Za Su Gudanar Da Taron Sanya Hannun Jarin Bunƙasa Ƙudurorin Muradun Ƙarni A Sifaniya

33 minutes ago
Gwamnati Za Ta Fara Sayar Wa Ɗangote Ɗanyen Mai Da Naira A Watan Oktoba
Labarai

Matatar Dangote Za Ta Fara Dakon Man Fetur Da Dizal Kyauta A Fadin Nijeriya

2 hours ago
IGP Ya Sake Bayar Da Umarnin Cafko Masa Mai Magana Da Yawun Gwamnan Kano Kan Bata Wa Ganduje 
Labarai

IGP Ya Sake Bayar Da Umarnin Cafko Masa Mai Magana Da Yawun Gwamnan Kano Kan Bata Wa Ganduje 

4 hours ago
Rundunar Sojin Ruwa Ta Nijeriya Ta Lalata Haramtattun Matatun Mai 5 A Ribas
Manyan Labarai

Rundunar Sojin Ruwa Ta Nijeriya Ta Lalata Haramtattun Matatun Mai 5 A Ribas

5 hours ago
Matatar Dangote Zata Fara Rarraba Man Fetur Da Dizal A Nijeriya
Manyan Labarai

Matatar Dangote Zata Fara Rarraba Man Fetur Da Dizal A Nijeriya

15 hours ago
Yansanda Sun Fara Tsananta Daukar Mataki Kan Yan Daba A Kano
Labarai

Yansanda Sun Fara Tsananta Daukar Mataki Kan Yan Daba A Kano

18 hours ago
Next Post
Dakataccen Gwamnan Ribas Ya Dawo Daga Hutun Makonni Biyu A Kasar Waje

Dakataccen Gwamnan Ribas Ya Dawo Daga Hutun Makonni Biyu A Kasar Waje

LABARAI MASU NASABA

Shugabannin Duniya Za Su Gudanar Da Taron Sanya Hannun Jarin Bunƙasa Ƙudurorin Muradun Ƙarni A Sifaniya

Shugabannin Duniya Za Su Gudanar Da Taron Sanya Hannun Jarin Bunƙasa Ƙudurorin Muradun Ƙarni A Sifaniya

June 16, 2025
Dan Nijeriya Lookman Na Kan Gaba Wajen Lashe Kyautar Gwarzon Kwallon Kafa Na Afrika Ta Bana

Atalanta Na Neman Yuro Miliyan 50 Daga Duk Kungiyar Da Ke Son Daukar Lookman

June 16, 2025
Gwamnati Za Ta Fara Sayar Wa Ɗangote Ɗanyen Mai Da Naira A Watan Oktoba

Matatar Dangote Za Ta Fara Dakon Man Fetur Da Dizal Kyauta A Fadin Nijeriya

June 16, 2025
IGP Ya Sake Bayar Da Umarnin Cafko Masa Mai Magana Da Yawun Gwamnan Kano Kan Bata Wa Ganduje 

IGP Ya Sake Bayar Da Umarnin Cafko Masa Mai Magana Da Yawun Gwamnan Kano Kan Bata Wa Ganduje 

June 16, 2025
Rundunar Sojin Ruwa Ta Nijeriya Ta Lalata Haramtattun Matatun Mai 5 A Ribas

Rundunar Sojin Ruwa Ta Nijeriya Ta Lalata Haramtattun Matatun Mai 5 A Ribas

June 16, 2025
Matatar Dangote Zata Fara Rarraba Man Fetur Da Dizal A Nijeriya

Matatar Dangote Zata Fara Rarraba Man Fetur Da Dizal A Nijeriya

June 15, 2025
Wata Sabuwa: Malaman Jami’ar Tarayya A Kano Sun ƙi Amince Wa Da Zaɓen Sabon VC

Wata Sabuwa: Malaman Jami’ar Tarayya A Kano Sun ƙi Amince Wa Da Zaɓen Sabon VC

June 15, 2025
PLA Reshen Kudancin Kasar Ta Yi Sintiri Na Hadin Gwiwa A Tekun Kudancin Sin

PLA Reshen Kudancin Kasar Ta Yi Sintiri Na Hadin Gwiwa A Tekun Kudancin Sin

June 15, 2025
An Bude Bikin Fina-Finai Na Kasa Da Kasa Karo Na 27 Na Shanghai

An Bude Bikin Fina-Finai Na Kasa Da Kasa Karo Na 27 Na Shanghai

June 15, 2025
Yansanda Sun Fara Tsananta Daukar Mataki Kan Yan Daba A Kano

Yansanda Sun Fara Tsananta Daukar Mataki Kan Yan Daba A Kano

June 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.