ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, December 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jam’iyyar NNPP Ta Dakatar Da Kwankwaso Na Wata 6 Kan Mata Zagon Kasa

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
2 years ago
NNPP

Majalisar amintattu (BoT) ta jam’iyyar NNPP ta dakatar da dan takararta na shugaban kasa a zaben 2023, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso na tsawon watanni shida daga shiga harkokin jam’iyyar bisa zarginsa da kasance cikin masu yi wa Jam’iyyar zagon kasa (anti-party). 

 

BoT ta zargi Kwankwaso da rabar shugaban kasa Bola Tinubu, PDP da dan takararta, Atiku Abubakar, da dan takarar shugaban kasa na LP Peter Obi, ba tare da amincewar majalisar ba.

ADVERTISEMENT
  • NNPP Ta Maka Kwankwaso A Kotu Kan Zargin Yi Wa Jam’iyya Makarkashiya

Kazalika, majalisar ta kuma warware wa Kwankwaso kambun kasancewa jigon jam’iyyar na kasa da na jiha.

 

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Kazalika, ta rushe dukkanin mambobin ayyuka (NWC) na jam’iyyar tare da nada sabbi a matsayin na riko karkashin jagorancin Dr. Agbo Major, da Kwamared Ogini Olaposi a matsayin sakataren riko tare da wasu jagorori 18 na jam’iyyar a matakin kasa.

 

Majalisar ta ce ta rushe tsohowar NWC dinta ne saboda rashin iyawa da gazawa da aka samu daga mambobin kwamitin ayyukan.

 

A jawabin bayan taron da suka gudanar a ranar Talata a Apapa, Legas da shugaban BoT na jam’iyyar, Temitope Aluko, ya fitar ya ce, “An yi ta kwaskwarima wa kundun tsarin mulkin NNPP ba tare da bin matakan da suka dace ba, kawai wasu daidaiku ne ke dagula lamura.”

 

Kazalika, majalisar ta gargadi Alhaji Buba Galadima da ya daina nuna kansa da cewa shine sakataten amintattu na jam’iyyar daga yanzu.

 

A jawabinsa na karbar mulki a matsayin shugaban riko, Dr. Major ya yi alkawarin tafiyar da harkokin jam’iyyar bisa doka kuma ya sha alwashin cewa ba zai bai wa majalisar kunya ba.

Kwankwaso dai shi ne dan takarar Jam’iyyar NNPP a zaben 2023 da ya gudana.

Jam’iyyar ta kasance cikin rikici tun bayan kammala babban zaben 2023 inda bangarori daban-daban ke ta zargin juna a cikinsu.

 

Rikicin na cikin gida ya haifar da dakatar da jigon Jam’iyyar Sanata Rabiu Musa Kwankwaso na tsawon watanni shida.

 

Idan za a tuna dai NWC na jam’iyyar a ranar Alhamis 24 ga watan Agustan ya dakakatar da wanda ya kafa jam’iyyar Dr Boniface Aniebonam da babban sakataren watsa labarai na Jam’iyyar da wasu tun da farko, sai dai majalisar amintattu Jam’iyyar ya ki amincewa da dakatarwar da aka yi musu

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja
Manyan Labarai

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta
Manyan Labarai

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Next Post
NNPP

Daga watan Janairu zuwa Yuli, kudaden shigar kasuwancin software na kasar Sin ya karu da 13.6%

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.