• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jam’iyyar NNPP Ta Dakatar Da Kwankwaso Na Wata 6 Kan Mata Zagon Kasa

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
2 years ago
NNPP

Majalisar amintattu (BoT) ta jam’iyyar NNPP ta dakatar da dan takararta na shugaban kasa a zaben 2023, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso na tsawon watanni shida daga shiga harkokin jam’iyyar bisa zarginsa da kasance cikin masu yi wa Jam’iyyar zagon kasa (anti-party). 

 

BoT ta zargi Kwankwaso da rabar shugaban kasa Bola Tinubu, PDP da dan takararta, Atiku Abubakar, da dan takarar shugaban kasa na LP Peter Obi, ba tare da amincewar majalisar ba.

  • NNPP Ta Maka Kwankwaso A Kotu Kan Zargin Yi Wa Jam’iyya Makarkashiya

Kazalika, majalisar ta kuma warware wa Kwankwaso kambun kasancewa jigon jam’iyyar na kasa da na jiha.

 

LABARAI MASU NASABA

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

Kazalika, ta rushe dukkanin mambobin ayyuka (NWC) na jam’iyyar tare da nada sabbi a matsayin na riko karkashin jagorancin Dr. Agbo Major, da Kwamared Ogini Olaposi a matsayin sakataren riko tare da wasu jagorori 18 na jam’iyyar a matakin kasa.

 

Majalisar ta ce ta rushe tsohowar NWC dinta ne saboda rashin iyawa da gazawa da aka samu daga mambobin kwamitin ayyukan.

 

A jawabin bayan taron da suka gudanar a ranar Talata a Apapa, Legas da shugaban BoT na jam’iyyar, Temitope Aluko, ya fitar ya ce, “An yi ta kwaskwarima wa kundun tsarin mulkin NNPP ba tare da bin matakan da suka dace ba, kawai wasu daidaiku ne ke dagula lamura.”

 

Kazalika, majalisar ta gargadi Alhaji Buba Galadima da ya daina nuna kansa da cewa shine sakataten amintattu na jam’iyyar daga yanzu.

 

A jawabinsa na karbar mulki a matsayin shugaban riko, Dr. Major ya yi alkawarin tafiyar da harkokin jam’iyyar bisa doka kuma ya sha alwashin cewa ba zai bai wa majalisar kunya ba.

Kwankwaso dai shi ne dan takarar Jam’iyyar NNPP a zaben 2023 da ya gudana.

Jam’iyyar ta kasance cikin rikici tun bayan kammala babban zaben 2023 inda bangarori daban-daban ke ta zargin juna a cikinsu.

 

Rikicin na cikin gida ya haifar da dakatar da jigon Jam’iyyar Sanata Rabiu Musa Kwankwaso na tsawon watanni shida.

 

Idan za a tuna dai NWC na jam’iyyar a ranar Alhamis 24 ga watan Agustan ya dakakatar da wanda ya kafa jam’iyyar Dr Boniface Aniebonam da babban sakataren watsa labarai na Jam’iyyar da wasu tun da farko, sai dai majalisar amintattu Jam’iyyar ya ki amincewa da dakatarwar da aka yi musu

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami
Manyan Labarai

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

November 1, 2025
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

November 1, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

November 1, 2025
Next Post
NNPP

Daga watan Janairu zuwa Yuli, kudaden shigar kasuwancin software na kasar Sin ya karu da 13.6%

LABARAI MASU NASABA

Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

November 1, 2025
Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

November 1, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar

November 1, 2025
Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

November 1, 2025
Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

November 1, 2025
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

November 1, 2025
Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?

Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?

November 1, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

November 1, 2025
Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

November 1, 2025
An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

November 1, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.