• English
  • Business News
Sunday, May 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jam’iyyar NNPP Ta Dakatar Da Kwankwaso Na Wata 6 Kan Mata Zagon Kasa

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Rusa Majalisar Zartarwa: Shugabannin NNPP Sun Yi Wa Kwankwaso Tutsu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Majalisar amintattu (BoT) ta jam’iyyar NNPP ta dakatar da dan takararta na shugaban kasa a zaben 2023, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso na tsawon watanni shida daga shiga harkokin jam’iyyar bisa zarginsa da kasance cikin masu yi wa Jam’iyyar zagon kasa (anti-party). 

 

BoT ta zargi Kwankwaso da rabar shugaban kasa Bola Tinubu, PDP da dan takararta, Atiku Abubakar, da dan takarar shugaban kasa na LP Peter Obi, ba tare da amincewar majalisar ba.

  • NNPP Ta Maka Kwankwaso A Kotu Kan Zargin Yi Wa Jam’iyya Makarkashiya

Kazalika, majalisar ta kuma warware wa Kwankwaso kambun kasancewa jigon jam’iyyar na kasa da na jiha.

 

Labarai Masu Nasaba

Yara Miliyan 2.9 A Nijeriya Ke Fama Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki – UNICEF

Budurwa ƴar shekara 15 Ta Jefar Da Jariri A Sansanin Ƴan Gudun Hijira A Borno 

Kazalika, ta rushe dukkanin mambobin ayyuka (NWC) na jam’iyyar tare da nada sabbi a matsayin na riko karkashin jagorancin Dr. Agbo Major, da Kwamared Ogini Olaposi a matsayin sakataren riko tare da wasu jagorori 18 na jam’iyyar a matakin kasa.

 

Majalisar ta ce ta rushe tsohowar NWC dinta ne saboda rashin iyawa da gazawa da aka samu daga mambobin kwamitin ayyukan.

 

A jawabin bayan taron da suka gudanar a ranar Talata a Apapa, Legas da shugaban BoT na jam’iyyar, Temitope Aluko, ya fitar ya ce, “An yi ta kwaskwarima wa kundun tsarin mulkin NNPP ba tare da bin matakan da suka dace ba, kawai wasu daidaiku ne ke dagula lamura.”

 

Kazalika, majalisar ta gargadi Alhaji Buba Galadima da ya daina nuna kansa da cewa shine sakataten amintattu na jam’iyyar daga yanzu.

 

A jawabinsa na karbar mulki a matsayin shugaban riko, Dr. Major ya yi alkawarin tafiyar da harkokin jam’iyyar bisa doka kuma ya sha alwashin cewa ba zai bai wa majalisar kunya ba.

Kwankwaso dai shi ne dan takarar Jam’iyyar NNPP a zaben 2023 da ya gudana.

Jam’iyyar ta kasance cikin rikici tun bayan kammala babban zaben 2023 inda bangarori daban-daban ke ta zargin juna a cikinsu.

 

Rikicin na cikin gida ya haifar da dakatar da jigon Jam’iyyar Sanata Rabiu Musa Kwankwaso na tsawon watanni shida.

 

Idan za a tuna dai NWC na jam’iyyar a ranar Alhamis 24 ga watan Agustan ya dakakatar da wanda ya kafa jam’iyyar Dr Boniface Aniebonam da babban sakataren watsa labarai na Jam’iyyar da wasu tun da farko, sai dai majalisar amintattu Jam’iyyar ya ki amincewa da dakatarwar da aka yi musu


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Shirya Taron Tattauna Kan Tsaron Sin Da Afirka Karo Na 3 A Beijing

Next Post

Daga watan Janairu zuwa Yuli, kudaden shigar kasuwancin software na kasar Sin ya karu da 13.6%

Related

Yara Miliyan 2.9 A Nijeriya Ke Fama Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki – UNICEF
Labarai

Yara Miliyan 2.9 A Nijeriya Ke Fama Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki – UNICEF

10 hours ago
Budurwa ƴar shekara 15 Ta Jefar Da Jariri A Sansanin Ƴan Gudun Hijira A Borno 
Labarai

Budurwa ƴar shekara 15 Ta Jefar Da Jariri A Sansanin Ƴan Gudun Hijira A Borno 

16 hours ago
NNPCL Ta Rufe Matatar Mai Ta Fatakwal
Labarai

NNPCL Ta Rufe Matatar Mai Ta Fatakwal

16 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mazauna Kauyuka 4 A Taraba Bayan Taron Zuba Jari
Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mazauna Kauyuka 4 A Taraba Bayan Taron Zuba Jari

17 hours ago
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

20 hours ago
Za Mu Ci Gaba Da Aikin Neman Man Fetur Arewacin Nijeriya — Ojulari
Labarai

Za Mu Ci Gaba Da Aikin Neman Man Fetur Arewacin Nijeriya — Ojulari

23 hours ago
Next Post
NNPP

Daga watan Janairu zuwa Yuli, kudaden shigar kasuwancin software na kasar Sin ya karu da 13.6%

LABARAI MASU NASABA

An Gano Kofin Gasar Zakarun Turai Na Mata Bayan Sace Shi Da Aka Yi

An Gano Kofin Gasar Zakarun Turai Na Mata Bayan Sace Shi Da Aka Yi

May 24, 2025
Firaministan Sin Ya Sauka A Indonesia Domin Ziyarar Aiki

Firaministan Sin Ya Sauka A Indonesia Domin Ziyarar Aiki

May 24, 2025
Tawagar MDD Da Majalisar Shugabancin Libya Sun Kafa Kwamitin Tsagaita Bude Wuta

Tawagar MDD Da Majalisar Shugabancin Libya Sun Kafa Kwamitin Tsagaita Bude Wuta

May 24, 2025
Firaministan Sin Ya Shugabanci Taro Kan Masana’antu Masu Amfani Da Makamashi Mai Tsafta Da Kare Muhalli 

Firaministan Sin Ya Shugabanci Taro Kan Masana’antu Masu Amfani Da Makamashi Mai Tsafta Da Kare Muhalli 

May 24, 2025
Yara Miliyan 2.9 A Nijeriya Ke Fama Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki – UNICEF

Yara Miliyan 2.9 A Nijeriya Ke Fama Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki – UNICEF

May 24, 2025
CHINADA Ta Nuna Matukar Adawa Da Gasar Wasannin Da Aka Amince Da Kwayoyin Kara Kuzari

CHINADA Ta Nuna Matukar Adawa Da Gasar Wasannin Da Aka Amince Da Kwayoyin Kara Kuzari

May 24, 2025

Tsokaci Kan Yadda Wasu Matasa Ke Yin Aure Ba Tare Da Sana’a Ba

May 24, 2025
Sin Ta Jaddada Da Muhimmancin Tsagaita Bude Wuta A Zirin Gaza

Sin Ta Jaddada Da Muhimmancin Tsagaita Bude Wuta A Zirin Gaza

May 24, 2025
An Kaddamar Da Bikin Baje Kolin Aikin Gona Na Kasa Da Kasa Na Cote d’Ivoire

An Kaddamar Da Bikin Baje Kolin Aikin Gona Na Kasa Da Kasa Na Cote d’Ivoire

May 24, 2025
Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

May 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.