• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jarin Waje Na Kai Tsaye Dake Shigowa Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 1.04 Cikin Watanni 11 Na Farkon Bana

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Jarin Waje Na Kai Tsaye Dake Shigowa Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 1.04 Cikin Watanni 11 Na Farkon Bana
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ma’aikatar cinikayya ta kasar Sin, ta ce jarin waje na kai tsaye dake shigowa Sin wato FDI, ya kai yuan tiriliyan 1.04 cikin watanni 11 na farkon shekarar bana.

Alkaluman ma’aikatar ya nuna cewa, jarin na FDI da ake amfani da shi a babban yankin kasar ya kai yuan tiriliyan 1.04, kwatankwacin dalar Amurka biliyan 146.45 cikin watannin 11, wanda ya yi kasa da na shekarar da ta gabata da kaso 10 bisa dari.

  • Sin Ta Tsara Kyawawan Sharuddan Janyo Jarin Waje
  • Sin Ta Bayyana Matukar Adawa Ga Amurka Game Da Batun Sayarwa Taiwan Makamai

Tsakanin watannin 11, sabbin kamfanoni masu zuba jarin kai tsaye 48,078 ne suka bude hada hada a kasar ta Sin, adadin da ya karu da kaso 36.2 bisa dari a shekara.

Har ila yau, a cewar ma’aikatar, alkaluman FDI a fannin kamfanonin manyan fasahohi ya daga da kaso 1.8 bisa dari a shekara, yayin da na fannin samar da kayayyakin bukata a fannin kiwon lafiya ya daga da kaso 27.6 bisa dari, sai kuma na fannin sadarwa da ya karu da kaso 5.5 bisa dari.

Kaza lika, a tsakanin wannan wa’adi, FDI daga kasashen Birtaniya ya kasu da kaso 93.9, daga Faransa ya karu da kaso 93.2, sai na Netherlands da ya karu da kaso 34.1 bisa dari.

Labarai Masu Nasaba

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Game da halin tattalin arziki da kasar Sin ke ciki, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Wang Wenbin, ya bayyana yayin taron manema labarai na Alhamis din nan cewa, ci gaban kasar Sin na fuskantar karin yanayi mai inganci, sama da nau’o’in kalubalen da yake fuskanta, kuma muhimman matakan da kasar ke aiwatarwa, na farfadowa da inganta tattalin arziki a tsawon lokaci ba su sauya ba, kana dukkanin ginshikai dake goya baya ga samar da ci gaba mai inganci, na haifar da karin kyautatuwar yanayi a fannin.

Kafin hakan, yayin wata ganawa da manema labarai, wakilin asusun ba da lamuni na duniya IMF Steven Alan Barnett, ya ce a shekarar bana, Sin za ta samar da gudummawar kaso 1 bisa 3 na karfin bunkasar tattalin arzikin duniya. Barnett ya yi hasashen cewa, tattalin arzikin Sin zai ci gaba da bunkasa a shekarar 2024.

Game da hakan, Wang Wenbin ya ce cibiyoyin kasa da kasa masu yawa, ciki har da IMF, da hukumar bunkasa hadin gwiwar raya tattalin arziki da samar da ci gaba, a baya bayan nan sun daga mizanin hasashen su na ci gaban tattalin arzikin Sin, a shekarar nan ta bana, da ma shekarar dake tafe. Hakan a cewarsa na nuna cewa, Sin ta zama babban jigo dake ingiza ci gaban tattalin arzikin duniya. (Mai fassara: Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Har Kullum Sin Na Nacewa Manufar Tallafawa Abokan Tafiya Kasashe Masu Tasowa

Next Post

Bayan Zantawa Da Sin Lokaci Ya Yi Da Philippines Ta Gane Kuskurenta

Related

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa
Daga Birnin Sin

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

11 hours ago
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

12 hours ago
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

13 hours ago
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci
Daga Birnin Sin

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

14 hours ago
Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu
Daga Birnin Sin

Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

16 hours ago
Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo
Daga Birnin Sin

Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo

1 day ago
Next Post
Bayan Zantawa Da Sin Lokaci Ya Yi Da Philippines Ta Gane Kuskurenta

Bayan Zantawa Da Sin Lokaci Ya Yi Da Philippines Ta Gane Kuskurenta

LABARAI MASU NASABA

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.