• English
  • Business News
Wednesday, June 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jarin Waje Na Kai Tsaye Dake Shigowa Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 1.04 Cikin Watanni 11 Na Farkon Bana

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Jarin Waje Na Kai Tsaye Dake Shigowa Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 1.04 Cikin Watanni 11 Na Farkon Bana
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ma’aikatar cinikayya ta kasar Sin, ta ce jarin waje na kai tsaye dake shigowa Sin wato FDI, ya kai yuan tiriliyan 1.04 cikin watanni 11 na farkon shekarar bana.

Alkaluman ma’aikatar ya nuna cewa, jarin na FDI da ake amfani da shi a babban yankin kasar ya kai yuan tiriliyan 1.04, kwatankwacin dalar Amurka biliyan 146.45 cikin watannin 11, wanda ya yi kasa da na shekarar da ta gabata da kaso 10 bisa dari.

  • Sin Ta Tsara Kyawawan Sharuddan Janyo Jarin Waje
  • Sin Ta Bayyana Matukar Adawa Ga Amurka Game Da Batun Sayarwa Taiwan Makamai

Tsakanin watannin 11, sabbin kamfanoni masu zuba jarin kai tsaye 48,078 ne suka bude hada hada a kasar ta Sin, adadin da ya karu da kaso 36.2 bisa dari a shekara.

Har ila yau, a cewar ma’aikatar, alkaluman FDI a fannin kamfanonin manyan fasahohi ya daga da kaso 1.8 bisa dari a shekara, yayin da na fannin samar da kayayyakin bukata a fannin kiwon lafiya ya daga da kaso 27.6 bisa dari, sai kuma na fannin sadarwa da ya karu da kaso 5.5 bisa dari.

Kaza lika, a tsakanin wannan wa’adi, FDI daga kasashen Birtaniya ya kasu da kaso 93.9, daga Faransa ya karu da kaso 93.2, sai na Netherlands da ya karu da kaso 34.1 bisa dari.

Labarai Masu Nasaba

Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

Game da halin tattalin arziki da kasar Sin ke ciki, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Wang Wenbin, ya bayyana yayin taron manema labarai na Alhamis din nan cewa, ci gaban kasar Sin na fuskantar karin yanayi mai inganci, sama da nau’o’in kalubalen da yake fuskanta, kuma muhimman matakan da kasar ke aiwatarwa, na farfadowa da inganta tattalin arziki a tsawon lokaci ba su sauya ba, kana dukkanin ginshikai dake goya baya ga samar da ci gaba mai inganci, na haifar da karin kyautatuwar yanayi a fannin.

Kafin hakan, yayin wata ganawa da manema labarai, wakilin asusun ba da lamuni na duniya IMF Steven Alan Barnett, ya ce a shekarar bana, Sin za ta samar da gudummawar kaso 1 bisa 3 na karfin bunkasar tattalin arzikin duniya. Barnett ya yi hasashen cewa, tattalin arzikin Sin zai ci gaba da bunkasa a shekarar 2024.

Game da hakan, Wang Wenbin ya ce cibiyoyin kasa da kasa masu yawa, ciki har da IMF, da hukumar bunkasa hadin gwiwar raya tattalin arziki da samar da ci gaba, a baya bayan nan sun daga mizanin hasashen su na ci gaban tattalin arzikin Sin, a shekarar nan ta bana, da ma shekarar dake tafe. Hakan a cewarsa na nuna cewa, Sin ta zama babban jigo dake ingiza ci gaban tattalin arzikin duniya. (Mai fassara: Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Har Kullum Sin Na Nacewa Manufar Tallafawa Abokan Tafiya Kasashe Masu Tasowa

Next Post

Bayan Zantawa Da Sin Lokaci Ya Yi Da Philippines Ta Gane Kuskurenta

Related

Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?
Daga Birnin Sin

Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

11 hours ago
Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

13 hours ago
Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba
Daga Birnin Sin

Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba

14 hours ago
Sin Da Kasashen Musulmi Za Su Kara Zurfafa Dangantakarsu
Daga Birnin Sin

Sin Da Kasashen Musulmi Za Su Kara Zurfafa Dangantakarsu

17 hours ago
Sabuwar Shugabar Kwamitin Wasannin Olympics Na Duniya Na Fatan Sake Ziyartar Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Sabuwar Shugabar Kwamitin Wasannin Olympics Na Duniya Na Fatan Sake Ziyartar Kasar Sin

1 day ago
Xi Jinping Zai Halarci Bikin Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Jinin Harin Sojojin Japan Da Yakin Kin Tafarkin Murdiya
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Zai Halarci Bikin Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Jinin Harin Sojojin Japan Da Yakin Kin Tafarkin Murdiya

1 day ago
Next Post
Bayan Zantawa Da Sin Lokaci Ya Yi Da Philippines Ta Gane Kuskurenta

Bayan Zantawa Da Sin Lokaci Ya Yi Da Philippines Ta Gane Kuskurenta

LABARAI MASU NASABA

KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan Ɗaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano

KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan Ɗaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano

June 25, 2025
‘Yan Bindiga Sun Kashe Ɗan Kasuwa da Ɗan Banga A Kwara

‘Yan Bindiga Sun Kashe Ɗan Kasuwa da Ɗan Banga A Kwara

June 25, 2025
Bilicin: NAFDAC Ta Kama Mutane 6, Ta Rufe Shaguna A Kano

Bilicin: NAFDAC Ta Kama Mutane 6, Ta Rufe Shaguna A Kano

June 25, 2025
Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

June 24, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

June 24, 2025
Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

June 24, 2025
Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

June 24, 2025
Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba

Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba

June 24, 2025
Barau Ya Nisanta Kansa Daga Kiraye-kirayen Ya Zama Mataimakin Tinubu A Zaben 2027

Barau Ya Nisanta Kansa Daga Kiraye-kirayen Ya Zama Mataimakin Tinubu A Zaben 2027

June 24, 2025
Shugabannin PDP Sun Ziyarci INEC Kan Neman Sanin Ka’idojinta

Shugabannin PDP Sun Ziyarci INEC Kan Neman Sanin Ka’idojinta

June 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.