ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bayan Zantawa Da Sin Lokaci Ya Yi Da Philippines Ta Gane Kuskurenta

by CGTN Hausa
2 years ago
Sin

A jiya Laraba 20 ga watan nan na Disamba, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya zanta da takwaransa na Philippine Enrique A. Manalo ta wayar tarho.

A gabar da alakar Sin da Philippines ta shiga wani yanayi mai sarkakiya, don gane da batun tekun kudancin Sin, tattaunawar da manyan jami’an biyu suka yi ta tarho, ta janyo hankulan sassan kasa da kasa. Yayin zantawar, bangaren Sin ya fayyace cewa, Philippines ta sauya matsayar ta, ta janye daga alkawuran da ta dauka, tana kuma ci gaba da takalar rigima a yankin teku, wanda hakan keta halastattun hakkokin Sin ne da moriyar ta bisa doka.

  • Firaministan Sin Ya Jaddada Bukatar Kyautata Yanayin Kasuwanci Da Kara Habaka Kasuwanni
  • Sin Ta Kara Tallafin Kudi Don Maido Da Wuraren Kiyaye Ruwa A Yankunan Da Girgizar Kasar Ta Shafa

Tun daga farkon wannan shekara, rahotanni na nuna yadda Philippines ta rika tura jiragen ruwan gwamnati, da na yaki, suna yin kutse a sassan ruwan dake daura da Ren’ai Jiao na tsibiran Nansha na kasar Sin, kana Philippines din ta rika aikewa da kayan gine gine zuwa ga jiragen dakon kaya na sojin ta da aka jibge ba bisa ka’ida ba, a wani mataki na wanzar da mamaya a yankin ruwan na Ren’ai Jiao.

ADVERTISEMENT

Abun tambaya a nan shi ne, mene ne ya sa gwamnatin Philippine din aikata hakan? Masharhanta na ganin a daya bangaren, akwai murya mai karfi a Philippines dake ingiza batun tekun kudancin Sin, kuma shugaban Philippine na son amfani da hakan wajen karfafa karbuwarsa, ta hanyar nuna matsayin sa na rikau. A daya bangaren kuwa, yayin da hadin gwiwar Amurka da Philippines a fannin tsaro da sauran sassa ke kankama, manufofin waje na Philippines din sun fara karkara ga ra’ayoyin Amurka.

A fannin dangantakar Sin da Philippines, cikin shekarun baya bayan nan, Sin ta nuna halin dattaku, da hakuri wajen warware rashin fahimta game da batun tekun kudancin Sin tare da Philippines. To sai dai kuma hakan ba ya nuna cewa Sin za ta sadaukar da wani hakkin mulkin yankunan ta. Tun farkon wannan shekara ta bana, Sin ta rika daukar jerin hakikanin matakai na kare hakkokin ta.

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Yayin tattaunawar manyan jami’an, bangaren Sin ya fayyace matsayarsa ga Philippine, wadda ta kuskurewa gaskiyar lamarin, ta yi gaban kan ta, har ma ta yi hadin kai da wasu sassa na waje, wadanda ba sa ga maciji da juna da Sin. Philippine ta ci gaba da aiwatar da matakan tada husuma, sai dai a na ta bangare, Sin za ta yi duk mai yiwuwa, wajen kare hakkokin ta kamar yadda doka ta tanada, tare da maida martani idan akwai bukatar hakan. Wannan wani gargadi ne a fayyace, wanda muke fatan zai sanya Philippines fahimta, da lura da halin da ake ciki, kana ta tsaya kan gaskiya a kalamanta da matakan da take aiwatarwa. (Mai fassara: Saminu Alhassan)

Sin
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

MASU ALAKA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
Daga Birnin Sin

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
Daga Birnin Sin

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
Daga Birnin Sin

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Next Post
Yadda Hakar Ma’adanai Ba Bisa Ka’ida Ba Ke Ruruta Ayyukan Ta’addanci

Yadda Hakar Ma’adanai Ba Bisa Ka’ida Ba Ke Ruruta Ayyukan Ta’addanci

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.