ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bayan Zantawa Da Sin Lokaci Ya Yi Da Philippines Ta Gane Kuskurenta

by CGTN Hausa
3 years ago
Sin

A jiya Laraba 20 ga watan nan na Disamba, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya zanta da takwaransa na Philippine Enrique A. Manalo ta wayar tarho.

A gabar da alakar Sin da Philippines ta shiga wani yanayi mai sarkakiya, don gane da batun tekun kudancin Sin, tattaunawar da manyan jami’an biyu suka yi ta tarho, ta janyo hankulan sassan kasa da kasa. Yayin zantawar, bangaren Sin ya fayyace cewa, Philippines ta sauya matsayar ta, ta janye daga alkawuran da ta dauka, tana kuma ci gaba da takalar rigima a yankin teku, wanda hakan keta halastattun hakkokin Sin ne da moriyar ta bisa doka.

  • Firaministan Sin Ya Jaddada Bukatar Kyautata Yanayin Kasuwanci Da Kara Habaka Kasuwanni
  • Sin Ta Kara Tallafin Kudi Don Maido Da Wuraren Kiyaye Ruwa A Yankunan Da Girgizar Kasar Ta Shafa

Tun daga farkon wannan shekara, rahotanni na nuna yadda Philippines ta rika tura jiragen ruwan gwamnati, da na yaki, suna yin kutse a sassan ruwan dake daura da Ren’ai Jiao na tsibiran Nansha na kasar Sin, kana Philippines din ta rika aikewa da kayan gine gine zuwa ga jiragen dakon kaya na sojin ta da aka jibge ba bisa ka’ida ba, a wani mataki na wanzar da mamaya a yankin ruwan na Ren’ai Jiao.

ADVERTISEMENT

Abun tambaya a nan shi ne, mene ne ya sa gwamnatin Philippine din aikata hakan? Masharhanta na ganin a daya bangaren, akwai murya mai karfi a Philippines dake ingiza batun tekun kudancin Sin, kuma shugaban Philippine na son amfani da hakan wajen karfafa karbuwarsa, ta hanyar nuna matsayin sa na rikau. A daya bangaren kuwa, yayin da hadin gwiwar Amurka da Philippines a fannin tsaro da sauran sassa ke kankama, manufofin waje na Philippines din sun fara karkara ga ra’ayoyin Amurka.

A fannin dangantakar Sin da Philippines, cikin shekarun baya bayan nan, Sin ta nuna halin dattaku, da hakuri wajen warware rashin fahimta game da batun tekun kudancin Sin tare da Philippines. To sai dai kuma hakan ba ya nuna cewa Sin za ta sadaukar da wani hakkin mulkin yankunan ta. Tun farkon wannan shekara ta bana, Sin ta rika daukar jerin hakikanin matakai na kare hakkokin ta.

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Yayin tattaunawar manyan jami’an, bangaren Sin ya fayyace matsayarsa ga Philippine, wadda ta kuskurewa gaskiyar lamarin, ta yi gaban kan ta, har ma ta yi hadin kai da wasu sassa na waje, wadanda ba sa ga maciji da juna da Sin. Philippine ta ci gaba da aiwatar da matakan tada husuma, sai dai a na ta bangare, Sin za ta yi duk mai yiwuwa, wajen kare hakkokin ta kamar yadda doka ta tanada, tare da maida martani idan akwai bukatar hakan. Wannan wani gargadi ne a fayyace, wanda muke fatan zai sanya Philippines fahimta, da lura da halin da ake ciki, kana ta tsaya kan gaskiya a kalamanta da matakan da take aiwatarwa. (Mai fassara: Saminu Alhassan)

Sin
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

MASU ALAKA

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje
Daga Birnin Sin

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Next Post
Yadda Hakar Ma’adanai Ba Bisa Ka’ida Ba Ke Ruruta Ayyukan Ta’addanci

Yadda Hakar Ma’adanai Ba Bisa Ka’ida Ba Ke Ruruta Ayyukan Ta’addanci

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.