ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bayan Zantawa Da Sin Lokaci Ya Yi Da Philippines Ta Gane Kuskurenta

by CGTN Hausa
3 years ago
Sin

A jiya Laraba 20 ga watan nan na Disamba, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya zanta da takwaransa na Philippine Enrique A. Manalo ta wayar tarho.

A gabar da alakar Sin da Philippines ta shiga wani yanayi mai sarkakiya, don gane da batun tekun kudancin Sin, tattaunawar da manyan jami’an biyu suka yi ta tarho, ta janyo hankulan sassan kasa da kasa. Yayin zantawar, bangaren Sin ya fayyace cewa, Philippines ta sauya matsayar ta, ta janye daga alkawuran da ta dauka, tana kuma ci gaba da takalar rigima a yankin teku, wanda hakan keta halastattun hakkokin Sin ne da moriyar ta bisa doka.

  • Firaministan Sin Ya Jaddada Bukatar Kyautata Yanayin Kasuwanci Da Kara Habaka Kasuwanni
  • Sin Ta Kara Tallafin Kudi Don Maido Da Wuraren Kiyaye Ruwa A Yankunan Da Girgizar Kasar Ta Shafa

Tun daga farkon wannan shekara, rahotanni na nuna yadda Philippines ta rika tura jiragen ruwan gwamnati, da na yaki, suna yin kutse a sassan ruwan dake daura da Ren’ai Jiao na tsibiran Nansha na kasar Sin, kana Philippines din ta rika aikewa da kayan gine gine zuwa ga jiragen dakon kaya na sojin ta da aka jibge ba bisa ka’ida ba, a wani mataki na wanzar da mamaya a yankin ruwan na Ren’ai Jiao.

ADVERTISEMENT

Abun tambaya a nan shi ne, mene ne ya sa gwamnatin Philippine din aikata hakan? Masharhanta na ganin a daya bangaren, akwai murya mai karfi a Philippines dake ingiza batun tekun kudancin Sin, kuma shugaban Philippine na son amfani da hakan wajen karfafa karbuwarsa, ta hanyar nuna matsayin sa na rikau. A daya bangaren kuwa, yayin da hadin gwiwar Amurka da Philippines a fannin tsaro da sauran sassa ke kankama, manufofin waje na Philippines din sun fara karkara ga ra’ayoyin Amurka.

A fannin dangantakar Sin da Philippines, cikin shekarun baya bayan nan, Sin ta nuna halin dattaku, da hakuri wajen warware rashin fahimta game da batun tekun kudancin Sin tare da Philippines. To sai dai kuma hakan ba ya nuna cewa Sin za ta sadaukar da wani hakkin mulkin yankunan ta. Tun farkon wannan shekara ta bana, Sin ta rika daukar jerin hakikanin matakai na kare hakkokin ta.

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Yayin tattaunawar manyan jami’an, bangaren Sin ya fayyace matsayarsa ga Philippine, wadda ta kuskurewa gaskiyar lamarin, ta yi gaban kan ta, har ma ta yi hadin kai da wasu sassa na waje, wadanda ba sa ga maciji da juna da Sin. Philippine ta ci gaba da aiwatar da matakan tada husuma, sai dai a na ta bangare, Sin za ta yi duk mai yiwuwa, wajen kare hakkokin ta kamar yadda doka ta tanada, tare da maida martani idan akwai bukatar hakan. Wannan wani gargadi ne a fayyace, wanda muke fatan zai sanya Philippines fahimta, da lura da halin da ake ciki, kana ta tsaya kan gaskiya a kalamanta da matakan da take aiwatarwa. (Mai fassara: Saminu Alhassan)

Sin
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Jinping Ya Taya Kim Jong-Un Murnar Cika Shekaru 78 Da Kafuwar Koriya Ta Arewa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
Daga Birnin Sin

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba
Daga Birnin Sin

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa
Daga Birnin Sin

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Next Post
Yadda Hakar Ma’adanai Ba Bisa Ka’ida Ba Ke Ruruta Ayyukan Ta’addanci

Yadda Hakar Ma’adanai Ba Bisa Ka’ida Ba Ke Ruruta Ayyukan Ta’addanci

LABARAI MASU NASABA

Sin

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Sin

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.