• English
  • Business News
Friday, May 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jiga-jigan APC Da Ke Tsammanin Samun Mukamin Siyasa A Gwamnatin Tinubu Sun Shiga Rudani

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Babu Wani Shiri Na Kwaso ‘Yan Nijeriya Daga Falasdin Ko Isra’ila –Gwamnatin Tarayya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jiga-jigan jam’iyyar APC da ke tsammanin samun mukaman siyasa, musamman wadanda suka yi aiki wajen zaben Shugaban kasa Bola Tinubu sun shiga rudani, inda suka kaji da jiran gawon shanu har yau ba su sami mukami ba a wannan gwamnatin.

Daya daga cikin jiga-jigan wanda ya nemi a sakaye sunansa ya bayyana damuwarsa kan yadda gwamnatin Tinubu take bai wa wadanda ba ‘yan siyasa manyan mukamai masu gwabi tare da yin watsi da ‘yan siyasan da suka wahala wajen kafa wannnan gwamnati.

  • Bikin Sallah: Ministan Yaɗa Labarai Ya Nemi ‘Yan Nijeriya Su Dawo Da Kyawawan Dabi’un Da Suka Jingine
  • Yadda Jami’in Tsaro Ya Bindige Wani Mutum Ana Tsaka Da Sallar Idi A Zamfara

“Ina mai tabbatar da cewa mutane sun damu kwai da gaske. A lokacin yakin neman zabe, mafi yawancin wadanda ke samun manyan mukaman ba su yarda da manufar shugaban kasa ba. Yawancinsu sun yaki manufofin jam’iyyarmu.

“Amma yanzu ana ce mana su kadai ne za su iya rike wasu bangarori masu maiko. Amma babu wani dan siyasan da bai kware a wani bangare ba. Hasali ma, mun kwararru ne a fannoni daban-daban,” in ji shi.

Wasu rahotanni sun nuna cewa fadar shugaban kasa ta bukaci kungiyoyi daban-daban su mika sunayensu domin samun mukamai a shekarar da ta gabata, sai dai an bayyana cewa da yawan jiga-jigan APC an cire sunayensu.

Labarai Masu Nasaba

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

Wata majiya ta bayyana cewa tuni dai wasu daga cikin jiga-jigan sun hakura ganin yadda gwamnatin ta kusan shafe shekara daya babu wani labari.

“Abun dariya ne a cewa har yanzu mutanenmu suna jiran a fitar da sunayensu, wanda a yanzu an doshi shekara guda. Mafi yawancinmu ana bayyana mana cewa fadar shugaban kasa ba ta manta da duk wadanda suka taimaka mata ba, amma mutanenmu sun fara hakura,” in ji wata majiya.

Wasu da dama suna tunanin cewa za su sami mukami domin kuwa suna da masaniyar cewa sunayensu suna gaban mai girma shugaban kasa, ta hanayar wadanda suke da fada-a-ji musamma ma wadanda suke dasawa da shi a watannin baya.

Bincike ya nuna cewa fadar shugaban kasa na nan na aiki a kan nade-naden mukamai a hukumomin gudanarwa na ma’aikatu da cibiyoyin gwamnati tare da jakadun kasashe mabambanta.

A shekarar da ta gabata shugaban kasa ya kafa wani kwamiti da suka hada shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, Hon Femi Gbajabiamila da sakataren gwamnatin Tarayya, Senator George Akume domin su yi aiki a kan nade-naden mukamai, sai dai har yanzu ba a kara jin wani abu ba daga wannan batu.

Wata majiya da ke kusa da gwamnati, ta bayyana cewa batun rahoton Oron-Saye ya kawo tsaiko game da nade-naden mukmai wanda har yanzu ba a kammala ba.

“Gwamnati tana yin nazari a kan yadda za ta aiwatar da rahoton Orosaye domin duba mai yiwuwa a nade-naden mukamai ga mutane a ma’aikatu da aka hadesu ko kuma aka rage su. Wannan shi ne makasudin da ya sa aka samu tsaiko,” in ji wata majiya daga gwamnati.

Haka kuma nade-naden da aka yin a shugabannin gudanarwa a jami’o’in gwamnatin tarayya ya haifar da wasu matsaloli hukumomin gudanarwa na wasu jami’o’I da dama.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Rabon Hatsi Tan 42,000

Next Post

Shugaban Kungiyar Maharba Usman Tola Ya Rasu

Related

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

2 weeks ago
APC
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

2 weeks ago
‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa

2 weeks ago
Gwamnoni 9 Da Har Yanzu Ba Su Babe Da Iyayen Gidansu Ba
Tambarin Dimokuradiyya

Jihohi Sun Samu Naira Tiriliyan 1 Na Kudaden Kananan Hukumomi A Zango Na Daya

3 weeks ago
2027: Baba-Ahmed Ya Bukaci Tinubu Ya Janye, Ya Bar Matasa Su Yi Takara 
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Babu Dan Takarar Da Zai Iya Cin Zabe Ba Tare Da Goyon Bayan Arewa Ba – Baba Ahmed

3 weeks ago
arewa
Tambarin Dimokuradiyya

Kawunan Shugabannin Arewa Sun Rabu Kan Siyasar 2027

3 weeks ago
Next Post
Shugaban Kungiyar Maharba Usman Tola Ya Rasu

Shugaban Kungiyar Maharba Usman Tola Ya Rasu

LABARAI MASU NASABA

GORON JUMA’A 16/05/2025

GORON JUMA’A 16/05/2025

May 16, 2025
Zargin Cin Zarafi: Gaskiyar Halin Da Ake Ciki A Gidan Yarin Goron Dutse

Zargin Cin Zarafi: Gaskiyar Halin Da Ake Ciki A Gidan Yarin Goron Dutse

May 16, 2025
Nijeriya Na Bukatar Dala Biliyan 10 Kowace Shekara Domin Samun Ingantacciyar Wutar Lantarki — Minista

Nijeriya Na Bukatar Dala Biliyan 10 Kowace Shekara Domin Samun Ingantacciyar Wutar Lantarki — Minista

May 16, 2025
Masu Garkuwa Sun Nemi Miliyan ₦30 Don Sako Shugaban APC A Ondo

Masu Garkuwa Sun Nemi Miliyan ₦30 Don Sako Shugaban APC A Ondo

May 16, 2025
Dalilin Tsame Daya Cikin Uku Na Ma’aikatan Ƙasar Nan A Tsarin Sauye-sauyen Biyan Haraji – Czar

Dalilin Tsame Daya Cikin Uku Na Ma’aikatan Ƙasar Nan A Tsarin Sauye-sauyen Biyan Haraji – Czar

May 16, 2025
Abubuwan Da Aka Haramta Wa Mahajjaci

Abubuwan Da Aka Haramta Wa Mahajjaci

May 16, 2025
Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci

Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci

May 16, 2025
Abin  Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (1)

Abin  Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (1)

May 16, 2025
Rashin Tsaro Da Raba Wa Manoma Kayan Aiki Kan Lokaci Na Baraza Ga Wadata Kasa Da Abinci

Rashin Tsaro Da Raba Wa Manoma Kayan Aiki Kan Lokaci Na Baraza Ga Wadata Kasa Da Abinci

May 16, 2025
Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana

Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.