• English
  • Business News
Saturday, August 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jiga-jigan APC Da Ke Tsammanin Samun Mukamin Siyasa A Gwamnatin Tinubu Sun Shiga Rudani

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Babu Wani Shiri Na Kwaso ‘Yan Nijeriya Daga Falasdin Ko Isra’ila –Gwamnatin Tarayya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jiga-jigan jam’iyyar APC da ke tsammanin samun mukaman siyasa, musamman wadanda suka yi aiki wajen zaben Shugaban kasa Bola Tinubu sun shiga rudani, inda suka kaji da jiran gawon shanu har yau ba su sami mukami ba a wannan gwamnatin.

Daya daga cikin jiga-jigan wanda ya nemi a sakaye sunansa ya bayyana damuwarsa kan yadda gwamnatin Tinubu take bai wa wadanda ba ‘yan siyasa manyan mukamai masu gwabi tare da yin watsi da ‘yan siyasan da suka wahala wajen kafa wannnan gwamnati.

  • Bikin Sallah: Ministan Yaɗa Labarai Ya Nemi ‘Yan Nijeriya Su Dawo Da Kyawawan Dabi’un Da Suka Jingine
  • Yadda Jami’in Tsaro Ya Bindige Wani Mutum Ana Tsaka Da Sallar Idi A Zamfara

“Ina mai tabbatar da cewa mutane sun damu kwai da gaske. A lokacin yakin neman zabe, mafi yawancin wadanda ke samun manyan mukaman ba su yarda da manufar shugaban kasa ba. Yawancinsu sun yaki manufofin jam’iyyarmu.

“Amma yanzu ana ce mana su kadai ne za su iya rike wasu bangarori masu maiko. Amma babu wani dan siyasan da bai kware a wani bangare ba. Hasali ma, mun kwararru ne a fannoni daban-daban,” in ji shi.

Wasu rahotanni sun nuna cewa fadar shugaban kasa ta bukaci kungiyoyi daban-daban su mika sunayensu domin samun mukamai a shekarar da ta gabata, sai dai an bayyana cewa da yawan jiga-jigan APC an cire sunayensu.

Labarai Masu Nasaba

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

Wata majiya ta bayyana cewa tuni dai wasu daga cikin jiga-jigan sun hakura ganin yadda gwamnatin ta kusan shafe shekara daya babu wani labari.

“Abun dariya ne a cewa har yanzu mutanenmu suna jiran a fitar da sunayensu, wanda a yanzu an doshi shekara guda. Mafi yawancinmu ana bayyana mana cewa fadar shugaban kasa ba ta manta da duk wadanda suka taimaka mata ba, amma mutanenmu sun fara hakura,” in ji wata majiya.

Wasu da dama suna tunanin cewa za su sami mukami domin kuwa suna da masaniyar cewa sunayensu suna gaban mai girma shugaban kasa, ta hanayar wadanda suke da fada-a-ji musamma ma wadanda suke dasawa da shi a watannin baya.

Bincike ya nuna cewa fadar shugaban kasa na nan na aiki a kan nade-naden mukamai a hukumomin gudanarwa na ma’aikatu da cibiyoyin gwamnati tare da jakadun kasashe mabambanta.

A shekarar da ta gabata shugaban kasa ya kafa wani kwamiti da suka hada shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, Hon Femi Gbajabiamila da sakataren gwamnatin Tarayya, Senator George Akume domin su yi aiki a kan nade-naden mukamai, sai dai har yanzu ba a kara jin wani abu ba daga wannan batu.

Wata majiya da ke kusa da gwamnati, ta bayyana cewa batun rahoton Oron-Saye ya kawo tsaiko game da nade-naden mukmai wanda har yanzu ba a kammala ba.

“Gwamnati tana yin nazari a kan yadda za ta aiwatar da rahoton Orosaye domin duba mai yiwuwa a nade-naden mukamai ga mutane a ma’aikatu da aka hadesu ko kuma aka rage su. Wannan shi ne makasudin da ya sa aka samu tsaiko,” in ji wata majiya daga gwamnati.

Haka kuma nade-naden da aka yin a shugabannin gudanarwa a jami’o’in gwamnatin tarayya ya haifar da wasu matsaloli hukumomin gudanarwa na wasu jami’o’I da dama.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Rabon Hatsi Tan 42,000

Next Post

Shugaban Kungiyar Maharba Usman Tola Ya Rasu

Related

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

1 week ago
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 
Tambarin Dimokuradiyya

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

1 week ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

1 week ago
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2 weeks ago
majalisar kasa
Tambarin Dimokuradiyya

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

2 weeks ago
Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari
Rahotonni

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

3 weeks ago
Next Post
Shugaban Kungiyar Maharba Usman Tola Ya Rasu

Shugaban Kungiyar Maharba Usman Tola Ya Rasu

LABARAI MASU NASABA

Kwamitin Tantance Makarantun Gaba da Sakandire Na Bogi Ya Yi Wa Yankin Funtua Dirar Mikiya

Kwamitin Tantance Makarantun Gaba da Sakandire Na Bogi Ya Yi Wa Yankin Funtua Dirar Mikiya

August 2, 2025
Yarjejeniyar Dala Biliyan Ɗaya Da Ƙasar Brazil Za Ta Haɓaka Fannin Noma A Nijeriya —Tinubu

Yarjejeniyar Dala Biliyan Ɗaya Da Ƙasar Brazil Za Ta Haɓaka Fannin Noma A Nijeriya —Tinubu

August 2, 2025
ADC Za Ta Kayar Da Tinubu A 2027 – Dino Melaye

ADC Za Ta Kayar Da Tinubu A 2027 – Dino Melaye

August 2, 2025
Ƴansanda Sun Ƙwato Mota Da Aka Sace, Gami Da Cafke Dillalan Ƙwayoyi A Jigawa

Ƴansanda Sun Ƙwato Mota Da Aka Sace, Gami Da Cafke Dillalan Ƙwayoyi A Jigawa

August 2, 2025
Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa

Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa

August 1, 2025
Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

August 1, 2025
2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

August 1, 2025
Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

August 1, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

August 1, 2025
Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

August 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.