ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jiga-jigan APC Da Ke Tsammanin Samun Mukamin Siyasa A Gwamnatin Tinubu Sun Shiga Rudani

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
APC

Jiga-jigan jam’iyyar APC da ke tsammanin samun mukaman siyasa, musamman wadanda suka yi aiki wajen zaben Shugaban kasa Bola Tinubu sun shiga rudani, inda suka kaji da jiran gawon shanu har yau ba su sami mukami ba a wannan gwamnatin.

Daya daga cikin jiga-jigan wanda ya nemi a sakaye sunansa ya bayyana damuwarsa kan yadda gwamnatin Tinubu take bai wa wadanda ba ‘yan siyasa manyan mukamai masu gwabi tare da yin watsi da ‘yan siyasan da suka wahala wajen kafa wannnan gwamnati.

  • Bikin Sallah: Ministan Yaɗa Labarai Ya Nemi ‘Yan Nijeriya Su Dawo Da Kyawawan Dabi’un Da Suka Jingine
  • Yadda Jami’in Tsaro Ya Bindige Wani Mutum Ana Tsaka Da Sallar Idi A Zamfara

“Ina mai tabbatar da cewa mutane sun damu kwai da gaske. A lokacin yakin neman zabe, mafi yawancin wadanda ke samun manyan mukaman ba su yarda da manufar shugaban kasa ba. Yawancinsu sun yaki manufofin jam’iyyarmu.

ADVERTISEMENT

“Amma yanzu ana ce mana su kadai ne za su iya rike wasu bangarori masu maiko. Amma babu wani dan siyasan da bai kware a wani bangare ba. Hasali ma, mun kwararru ne a fannoni daban-daban,” in ji shi.

Wasu rahotanni sun nuna cewa fadar shugaban kasa ta bukaci kungiyoyi daban-daban su mika sunayensu domin samun mukamai a shekarar da ta gabata, sai dai an bayyana cewa da yawan jiga-jigan APC an cire sunayensu.

LABARAI MASU NASABA

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

Wata majiya ta bayyana cewa tuni dai wasu daga cikin jiga-jigan sun hakura ganin yadda gwamnatin ta kusan shafe shekara daya babu wani labari.

“Abun dariya ne a cewa har yanzu mutanenmu suna jiran a fitar da sunayensu, wanda a yanzu an doshi shekara guda. Mafi yawancinmu ana bayyana mana cewa fadar shugaban kasa ba ta manta da duk wadanda suka taimaka mata ba, amma mutanenmu sun fara hakura,” in ji wata majiya.

Wasu da dama suna tunanin cewa za su sami mukami domin kuwa suna da masaniyar cewa sunayensu suna gaban mai girma shugaban kasa, ta hanayar wadanda suke da fada-a-ji musamma ma wadanda suke dasawa da shi a watannin baya.

Bincike ya nuna cewa fadar shugaban kasa na nan na aiki a kan nade-naden mukamai a hukumomin gudanarwa na ma’aikatu da cibiyoyin gwamnati tare da jakadun kasashe mabambanta.

A shekarar da ta gabata shugaban kasa ya kafa wani kwamiti da suka hada shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, Hon Femi Gbajabiamila da sakataren gwamnatin Tarayya, Senator George Akume domin su yi aiki a kan nade-naden mukamai, sai dai har yanzu ba a kara jin wani abu ba daga wannan batu.

Wata majiya da ke kusa da gwamnati, ta bayyana cewa batun rahoton Oron-Saye ya kawo tsaiko game da nade-naden mukmai wanda har yanzu ba a kammala ba.

“Gwamnati tana yin nazari a kan yadda za ta aiwatar da rahoton Orosaye domin duba mai yiwuwa a nade-naden mukamai ga mutane a ma’aikatu da aka hadesu ko kuma aka rage su. Wannan shi ne makasudin da ya sa aka samu tsaiko,” in ji wata majiya daga gwamnati.

Haka kuma nade-naden da aka yin a shugabannin gudanarwa a jami’o’in gwamnatin tarayya ya haifar da wasu matsaloli hukumomin gudanarwa na wasu jami’o’I da dama.

APC
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Hukuncin Kotu Na Barazana Ga Zaben 2027 —INEC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana

MASU ALAKA

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Tambarin Dimokuradiyya

Zaben Fitar Da Gwani Na APC: Tinubu Zai Shiga Tsakani Wajen Warware Rikicin Jam’iyyar

June 5, 2026
Next Post
Shugaban Kungiyar Maharba Usman Tola Ya Rasu

Shugaban Kungiyar Maharba Usman Tola Ya Rasu

LABARAI MASU NASABA

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.