ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jiga-jigan APC Da Ke Tsammanin Samun Mukamin Siyasa A Gwamnatin Tinubu Sun Shiga Rudani

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
APC

Jiga-jigan jam’iyyar APC da ke tsammanin samun mukaman siyasa, musamman wadanda suka yi aiki wajen zaben Shugaban kasa Bola Tinubu sun shiga rudani, inda suka kaji da jiran gawon shanu har yau ba su sami mukami ba a wannan gwamnatin.

Daya daga cikin jiga-jigan wanda ya nemi a sakaye sunansa ya bayyana damuwarsa kan yadda gwamnatin Tinubu take bai wa wadanda ba ‘yan siyasa manyan mukamai masu gwabi tare da yin watsi da ‘yan siyasan da suka wahala wajen kafa wannnan gwamnati.

  • Bikin Sallah: Ministan Yaɗa Labarai Ya Nemi ‘Yan Nijeriya Su Dawo Da Kyawawan Dabi’un Da Suka Jingine
  • Yadda Jami’in Tsaro Ya Bindige Wani Mutum Ana Tsaka Da Sallar Idi A Zamfara

“Ina mai tabbatar da cewa mutane sun damu kwai da gaske. A lokacin yakin neman zabe, mafi yawancin wadanda ke samun manyan mukaman ba su yarda da manufar shugaban kasa ba. Yawancinsu sun yaki manufofin jam’iyyarmu.

ADVERTISEMENT

“Amma yanzu ana ce mana su kadai ne za su iya rike wasu bangarori masu maiko. Amma babu wani dan siyasan da bai kware a wani bangare ba. Hasali ma, mun kwararru ne a fannoni daban-daban,” in ji shi.

Wasu rahotanni sun nuna cewa fadar shugaban kasa ta bukaci kungiyoyi daban-daban su mika sunayensu domin samun mukamai a shekarar da ta gabata, sai dai an bayyana cewa da yawan jiga-jigan APC an cire sunayensu.

LABARAI MASU NASABA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

Wata majiya ta bayyana cewa tuni dai wasu daga cikin jiga-jigan sun hakura ganin yadda gwamnatin ta kusan shafe shekara daya babu wani labari.

“Abun dariya ne a cewa har yanzu mutanenmu suna jiran a fitar da sunayensu, wanda a yanzu an doshi shekara guda. Mafi yawancinmu ana bayyana mana cewa fadar shugaban kasa ba ta manta da duk wadanda suka taimaka mata ba, amma mutanenmu sun fara hakura,” in ji wata majiya.

Wasu da dama suna tunanin cewa za su sami mukami domin kuwa suna da masaniyar cewa sunayensu suna gaban mai girma shugaban kasa, ta hanayar wadanda suke da fada-a-ji musamma ma wadanda suke dasawa da shi a watannin baya.

Bincike ya nuna cewa fadar shugaban kasa na nan na aiki a kan nade-naden mukamai a hukumomin gudanarwa na ma’aikatu da cibiyoyin gwamnati tare da jakadun kasashe mabambanta.

A shekarar da ta gabata shugaban kasa ya kafa wani kwamiti da suka hada shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, Hon Femi Gbajabiamila da sakataren gwamnatin Tarayya, Senator George Akume domin su yi aiki a kan nade-naden mukamai, sai dai har yanzu ba a kara jin wani abu ba daga wannan batu.

Wata majiya da ke kusa da gwamnati, ta bayyana cewa batun rahoton Oron-Saye ya kawo tsaiko game da nade-naden mukmai wanda har yanzu ba a kammala ba.

“Gwamnati tana yin nazari a kan yadda za ta aiwatar da rahoton Orosaye domin duba mai yiwuwa a nade-naden mukamai ga mutane a ma’aikatu da aka hadesu ko kuma aka rage su. Wannan shi ne makasudin da ya sa aka samu tsaiko,” in ji wata majiya daga gwamnati.

Haka kuma nade-naden da aka yin a shugabannin gudanarwa a jami’o’in gwamnatin tarayya ya haifar da wasu matsaloli hukumomin gudanarwa na wasu jami’o’I da dama.

APC
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa

MASU ALAKA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
Tambarin Dimokuradiyya

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

September 5, 2026
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

September 4, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027

August 28, 2026
Next Post
Shugaban Kungiyar Maharba Usman Tola Ya Rasu

Shugaban Kungiyar Maharba Usman Tola Ya Rasu

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026
“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.