• English
  • Business News
Friday, November 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jihohi 21 Na Neman Bashin Naira Tiriliyan 1.65 Duk Da Ƙarin Kuɗaɗen Shiga

by Khalid Idris Doya and Abdullahi Muh'd Sheka
1 year ago
Tiriliyan

Jihohi 21 da suke fadin Nijeriyar suna neman ciwo rancen kudi da yawansa ya kai naira tiriliyan 1.65 domin cike gibin kasafinsu na 2024 duk da cewa sun samu tulin karin kason kudade daga asusun hadaka na tarayya (FAAC) a shekarar da ta gabata.

Daga watan Yunin 2023 zuwa Yunin 2024, dukkanin jihohin da suke fadin Nijeriya gami da kananan hukumomi 774 sun karbi adadin kudin da ya kai naira tiriliyan 7.6 daga asusun FAAC. Wannan karin sama da kaso 40 cikin 100 da suka samu na kudin shiga, shi ne irinsa na farko mafi yawa kuma an samu nasarar hakan ne sakamakon cire tallafin mai da gwamnatin tarayya ta yi a ranar 29 ga watan Mayun 2023.

  • Darajar Naira: Tsohon Dan Majalisa Da Ya Ci Bashin Karatu N1,200 A Shekaru 47, Yanzu Ya Biya Da Fiye Da Naira Miliyan 3
  • Bayan Fafatawa, Ƴan Ƙauye Sun Hallaka Ƴan Bindiga 37 A Zamfara

Binciken da aka gudanar ya nuna cewa an tsara jihohi 36 za su amshi naira tiriliyan 5.54 daga FAAC a wannan shekarar sabanin tiriliyan 3.3 da aka raba musu a shekarar da ta gabata.

A ranar 11 ga watan Yuli ne babban kotun koli ta yanke hukuncin bai wa kananan hukumomi 774 cikakken ‘yancin gashin kansu ta yadda za suke amsar kasonsu daga lalitar gwamnatin tarayya zuwa ga asusunsu kai tsaye, sabanin yadda yake zuwa hannun gwamnonin jihohi da suke yin yadda suka ga dama da kudaden.

A binciken da aka gudanar, ya nuna cewa jihohi 21 da suka nuna aniyarsu na ciyo bashin naira tiliyan 1.650 daga kafofin samun bashi na cikin gida da waje domin cike kowace gibin da ke cikin kasafin 2024. Sauran jihohi 15 kuma zuwa yanzu ba su shigar da tsarinsu na neman ciwo bashin ba.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

A cikakken tsarin lafto basukan da aka fitar, Jihar Adamawa ta yunkura domin ciwo bashin naira biliyan 68.46; Anambra naira biliyan 245; Bauchi naira biliyan 59.08; Bayelsa naira biliyan 64; Benuwai naira biliyan 34.69; Borno naira biliyan 41.71; Ebonyi naira biliyan 20.5; Edo naira biliyan 42.71 da kuma Ekiti da za ta ciwo bashin naira biliyan 27.15.

Sauran jihohin sun su ne Jigawa naira biliyan 1.78; Kaduna naira biliyan 150.1; Kebbi naira biliyan 36.7; Katsina naira biliyan 163.87; Kogi naira biliyan 37.08; Kwara naira biliyan 30.76; Osun naira biliyan 12.36; Oyo naira biliyan 133.4; Nasarawa naira biliyan 32.93; Gombe naira biliyan 73.75; Inugu naira biliyan 103, yayin da Imo ta shirya kinkimo bashin naira biliyan 271.34.

Sai dai masana sun fito sun ce akwai bukatar tabbatar da gaskiya da adalci kan makudan kudaden da jihohi suka karba balle a je ga maganar sake ciwo basuka.

Babban daraktan cibiyar wanzar da gaskiya da adalci a tsarin kasafi (CFTPI), Umar Yakubu, ya ce, akwai bukatar jihohi su fito su yi bayanin yadda suka kashe kudaden da suka amsa daga asusun gwamnatin tarayya domin wanzar da gaskiya da adalci.

Ya ce, cire tallafin mai ya janyo gwamnoni sun samu karin kudin shiga mafi tsoka, don haka da bukatar a gano yadda suka tafiyar da karin kudaden da suka samu na jihohi da na kananan hukumomi.

Shi ma wani kwararre, Bictor Agi, ya ce, muddin ba a wanzar da gaskiya wajen tafiyar da kudaden da suke shiga hannun gwamnatoci ba, to tabbas matsalolin da ake fuskanta za ma su ci gaba da karuwa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

November 6, 2025
Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 
Manyan Labarai

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

November 6, 2025
Gwamnatin tarayya
Labarai

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

November 6, 2025
Next Post
BUA Ya Soki Manyan Diloli Kan Dakile Shirin Sayar Da Siminti A Kan Farashi Mai Sauki

BUA Ya Soki Manyan Diloli Kan Dakile Shirin Sayar Da Siminti A Kan Farashi Mai Sauki

LABARAI MASU NASABA

An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an

An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an

November 6, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

November 6, 2025
Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

November 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

November 6, 2025
Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

November 6, 2025
Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

November 6, 2025
Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

November 6, 2025
A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

November 6, 2025
Gwamnatin tarayya

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

November 6, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

November 6, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.