ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jihohi 21 Na Neman Bashin Naira Tiriliyan 1.65 Duk Da Ƙarin Kuɗaɗen Shiga

by Khalid Idris Doya and Abdullahi Muh'd Sheka
2 years ago
Tiriliyan

Jihohi 21 da suke fadin Nijeriyar suna neman ciwo rancen kudi da yawansa ya kai naira tiriliyan 1.65 domin cike gibin kasafinsu na 2024 duk da cewa sun samu tulin karin kason kudade daga asusun hadaka na tarayya (FAAC) a shekarar da ta gabata.

Daga watan Yunin 2023 zuwa Yunin 2024, dukkanin jihohin da suke fadin Nijeriya gami da kananan hukumomi 774 sun karbi adadin kudin da ya kai naira tiriliyan 7.6 daga asusun FAAC. Wannan karin sama da kaso 40 cikin 100 da suka samu na kudin shiga, shi ne irinsa na farko mafi yawa kuma an samu nasarar hakan ne sakamakon cire tallafin mai da gwamnatin tarayya ta yi a ranar 29 ga watan Mayun 2023.

  • Darajar Naira: Tsohon Dan Majalisa Da Ya Ci Bashin Karatu N1,200 A Shekaru 47, Yanzu Ya Biya Da Fiye Da Naira Miliyan 3
  • Bayan Fafatawa, Ƴan Ƙauye Sun Hallaka Ƴan Bindiga 37 A Zamfara

Binciken da aka gudanar ya nuna cewa an tsara jihohi 36 za su amshi naira tiriliyan 5.54 daga FAAC a wannan shekarar sabanin tiriliyan 3.3 da aka raba musu a shekarar da ta gabata.

ADVERTISEMENT

A ranar 11 ga watan Yuli ne babban kotun koli ta yanke hukuncin bai wa kananan hukumomi 774 cikakken ‘yancin gashin kansu ta yadda za suke amsar kasonsu daga lalitar gwamnatin tarayya zuwa ga asusunsu kai tsaye, sabanin yadda yake zuwa hannun gwamnonin jihohi da suke yin yadda suka ga dama da kudaden.

A binciken da aka gudanar, ya nuna cewa jihohi 21 da suka nuna aniyarsu na ciyo bashin naira tiliyan 1.650 daga kafofin samun bashi na cikin gida da waje domin cike kowace gibin da ke cikin kasafin 2024. Sauran jihohi 15 kuma zuwa yanzu ba su shigar da tsarinsu na neman ciwo bashin ba.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

A cikakken tsarin lafto basukan da aka fitar, Jihar Adamawa ta yunkura domin ciwo bashin naira biliyan 68.46; Anambra naira biliyan 245; Bauchi naira biliyan 59.08; Bayelsa naira biliyan 64; Benuwai naira biliyan 34.69; Borno naira biliyan 41.71; Ebonyi naira biliyan 20.5; Edo naira biliyan 42.71 da kuma Ekiti da za ta ciwo bashin naira biliyan 27.15.

Sauran jihohin sun su ne Jigawa naira biliyan 1.78; Kaduna naira biliyan 150.1; Kebbi naira biliyan 36.7; Katsina naira biliyan 163.87; Kogi naira biliyan 37.08; Kwara naira biliyan 30.76; Osun naira biliyan 12.36; Oyo naira biliyan 133.4; Nasarawa naira biliyan 32.93; Gombe naira biliyan 73.75; Inugu naira biliyan 103, yayin da Imo ta shirya kinkimo bashin naira biliyan 271.34.

Sai dai masana sun fito sun ce akwai bukatar tabbatar da gaskiya da adalci kan makudan kudaden da jihohi suka karba balle a je ga maganar sake ciwo basuka.

Babban daraktan cibiyar wanzar da gaskiya da adalci a tsarin kasafi (CFTPI), Umar Yakubu, ya ce, akwai bukatar jihohi su fito su yi bayanin yadda suka kashe kudaden da suka amsa daga asusun gwamnatin tarayya domin wanzar da gaskiya da adalci.

Ya ce, cire tallafin mai ya janyo gwamnoni sun samu karin kudin shiga mafi tsoka, don haka da bukatar a gano yadda suka tafiyar da karin kudaden da suka samu na jihohi da na kananan hukumomi.

Shi ma wani kwararre, Bictor Agi, ya ce, muddin ba a wanzar da gaskiya wajen tafiyar da kudaden da suke shiga hannun gwamnatoci ba, to tabbas matsalolin da ake fuskanta za ma su ci gaba da karuwa.

Tiriliyan
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ‘Yansanda Sun Cafke Tsoho Mai Shekara 70 Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 8 Fyaɗe A Bauchi
Tiriliyan
Abdullahi Muh'd Sheka
+ posts Bio
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Sakamakon Matsin Lambar Jami’an Tsaro, ‘Yan Ta’adda Na Fuskantar Ƙarancin Abinci
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Kisan Gillar Mutum 7 A Kano: Sarakuna Da Malamai Da Iyaye Sun Nemi A Gaggauta Yanke Wa Waɗanda Ake Zargi Hukunci
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    MACBAN Ta Nemi Amurka Ta Cire Sunanta Daga Jerin Waɗanda Ta Ƙaƙabawa Takunkumi
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Faɗace-Faɗacen Daba Da Ƙwacen Waya A Kano Ya Ɗauki Sabon Salo

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
BUA Ya Soki Manyan Diloli Kan Dakile Shirin Sayar Da Siminti A Kan Farashi Mai Sauki

BUA Ya Soki Manyan Diloli Kan Dakile Shirin Sayar Da Siminti A Kan Farashi Mai Sauki

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.