• English
  • Business News
Friday, May 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jihohi 21 Na Neman Bashin Naira Tiriliyan 1.65 Duk Da Ƙarin Kuɗaɗen Shiga

by Khalid Idris Doya and Abdullahi Muh'd Sheka
9 months ago
in Labarai
0
Jihohi 21 Na Neman Bashin Naira Tiriliyan 1.65 Duk Da Ƙarin Kuɗaɗen Shiga
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jihohi 21 da suke fadin Nijeriyar suna neman ciwo rancen kudi da yawansa ya kai naira tiriliyan 1.65 domin cike gibin kasafinsu na 2024 duk da cewa sun samu tulin karin kason kudade daga asusun hadaka na tarayya (FAAC) a shekarar da ta gabata.

Daga watan Yunin 2023 zuwa Yunin 2024, dukkanin jihohin da suke fadin Nijeriya gami da kananan hukumomi 774 sun karbi adadin kudin da ya kai naira tiriliyan 7.6 daga asusun FAAC. Wannan karin sama da kaso 40 cikin 100 da suka samu na kudin shiga, shi ne irinsa na farko mafi yawa kuma an samu nasarar hakan ne sakamakon cire tallafin mai da gwamnatin tarayya ta yi a ranar 29 ga watan Mayun 2023.

  • Darajar Naira: Tsohon Dan Majalisa Da Ya Ci Bashin Karatu N1,200 A Shekaru 47, Yanzu Ya Biya Da Fiye Da Naira Miliyan 3
  • Bayan Fafatawa, Ƴan Ƙauye Sun Hallaka Ƴan Bindiga 37 A Zamfara

Binciken da aka gudanar ya nuna cewa an tsara jihohi 36 za su amshi naira tiriliyan 5.54 daga FAAC a wannan shekarar sabanin tiriliyan 3.3 da aka raba musu a shekarar da ta gabata.

A ranar 11 ga watan Yuli ne babban kotun koli ta yanke hukuncin bai wa kananan hukumomi 774 cikakken ‘yancin gashin kansu ta yadda za suke amsar kasonsu daga lalitar gwamnatin tarayya zuwa ga asusunsu kai tsaye, sabanin yadda yake zuwa hannun gwamnonin jihohi da suke yin yadda suka ga dama da kudaden.

A binciken da aka gudanar, ya nuna cewa jihohi 21 da suka nuna aniyarsu na ciyo bashin naira tiliyan 1.650 daga kafofin samun bashi na cikin gida da waje domin cike kowace gibin da ke cikin kasafin 2024. Sauran jihohi 15 kuma zuwa yanzu ba su shigar da tsarinsu na neman ciwo bashin ba.

Labarai Masu Nasaba

‘Yan PDP Na Komawa APC Ne Saboda Jam’iyyarsu Na Jin ƙamshin Mutuwa – Ganduje

Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 

A cikakken tsarin lafto basukan da aka fitar, Jihar Adamawa ta yunkura domin ciwo bashin naira biliyan 68.46; Anambra naira biliyan 245; Bauchi naira biliyan 59.08; Bayelsa naira biliyan 64; Benuwai naira biliyan 34.69; Borno naira biliyan 41.71; Ebonyi naira biliyan 20.5; Edo naira biliyan 42.71 da kuma Ekiti da za ta ciwo bashin naira biliyan 27.15.

Sauran jihohin sun su ne Jigawa naira biliyan 1.78; Kaduna naira biliyan 150.1; Kebbi naira biliyan 36.7; Katsina naira biliyan 163.87; Kogi naira biliyan 37.08; Kwara naira biliyan 30.76; Osun naira biliyan 12.36; Oyo naira biliyan 133.4; Nasarawa naira biliyan 32.93; Gombe naira biliyan 73.75; Inugu naira biliyan 103, yayin da Imo ta shirya kinkimo bashin naira biliyan 271.34.

Sai dai masana sun fito sun ce akwai bukatar tabbatar da gaskiya da adalci kan makudan kudaden da jihohi suka karba balle a je ga maganar sake ciwo basuka.

Babban daraktan cibiyar wanzar da gaskiya da adalci a tsarin kasafi (CFTPI), Umar Yakubu, ya ce, akwai bukatar jihohi su fito su yi bayanin yadda suka kashe kudaden da suka amsa daga asusun gwamnatin tarayya domin wanzar da gaskiya da adalci.

Ya ce, cire tallafin mai ya janyo gwamnoni sun samu karin kudin shiga mafi tsoka, don haka da bukatar a gano yadda suka tafiyar da karin kudaden da suka samu na jihohi da na kananan hukumomi.

Shi ma wani kwararre, Bictor Agi, ya ce, muddin ba a wanzar da gaskiya wajen tafiyar da kudaden da suke shiga hannun gwamnatoci ba, to tabbas matsalolin da ake fuskanta za ma su ci gaba da karuwa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BashiCreditLoanRevenue
ShareTweetSendShare
Previous Post

GORON JUMA’A 30-08-2024

Next Post

BUA Ya Soki Manyan Diloli Kan Dakile Shirin Sayar Da Siminti A Kan Farashi Mai Sauki

Related

Ganduje Ya Zargi Gwamna Yusuf Da Ɗaukar Nauyin Zanga-zanga A Kano
Labarai

‘Yan PDP Na Komawa APC Ne Saboda Jam’iyyarsu Na Jin ƙamshin Mutuwa – Ganduje

6 hours ago
Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 
Labarai

Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 

8 hours ago
Ƙungiyar ’yan Majalisar Dokokin Ƙasa Ta APC Ta Amince Da Takarar Tinubu A Zaɓen 2027 
Manyan Labarai

Ƙungiyar ’yan Majalisar Dokokin Ƙasa Ta APC Ta Amince Da Takarar Tinubu A Zaɓen 2027 

9 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

INEC Ta Samar Da Sashen Ƙirƙirarriyar Basira Domin Inganta Harkokin Zaɓe 

11 hours ago
Ingancin Tattalin Arzikin Sin Mai Bude Kofa Na Bayyana Sosai Duba Da Yawan Zuwan Baki Masu Sayayya
Ra'ayi Riga

Ingancin Tattalin Arzikin Sin Mai Bude Kofa Na Bayyana Sosai Duba Da Yawan Zuwan Baki Masu Sayayya

11 hours ago
Sanata Adamu Aliero Ya Ƙaddamar Da Rabon Kayan Tallafi Ga Ƙananan Hukumomi Takwas A Kebbi
Labarai

Sanata Adamu Aliero Ya Ƙaddamar Da Rabon Kayan Tallafi Ga Ƙananan Hukumomi Takwas A Kebbi

12 hours ago
Next Post
BUA Ya Soki Manyan Diloli Kan Dakile Shirin Sayar Da Siminti A Kan Farashi Mai Sauki

BUA Ya Soki Manyan Diloli Kan Dakile Shirin Sayar Da Siminti A Kan Farashi Mai Sauki

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Sama Jannatin Shenzhou-20 Sun Kammala Aiki A Wajen Tashar Sararin Samaniyar Kasar Sin

‘Yan Sama Jannatin Shenzhou-20 Sun Kammala Aiki A Wajen Tashar Sararin Samaniyar Kasar Sin

May 22, 2025
Ba Zai Yiwu Amurka Ta Kafawa Chips Kirar Kasar Sin Wani Shinge Ba

Ba Zai Yiwu Amurka Ta Kafawa Chips Kirar Kasar Sin Wani Shinge Ba

May 22, 2025
Ganduje Ya Zargi Gwamna Yusuf Da Ɗaukar Nauyin Zanga-zanga A Kano

‘Yan PDP Na Komawa APC Ne Saboda Jam’iyyarsu Na Jin ƙamshin Mutuwa – Ganduje

May 22, 2025
Masanan Najeriya Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwar Afirka Da Sin A Fannin Tinkarar Kalubalen Harajin Kwastam Na Amurka

Masanan Najeriya Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwar Afirka Da Sin A Fannin Tinkarar Kalubalen Harajin Kwastam Na Amurka

May 22, 2025
Modric Zai Bar Real Madrid Bayan Kammala Gasar Cin Kofin Duniya Na Kungiyoyi

Modric Zai Bar Real Madrid Bayan Kammala Gasar Cin Kofin Duniya Na Kungiyoyi

May 22, 2025
Yawan Wutar Lantarkin Da Sin Ke Iya Samar Ta Amfani Da Karfin Ruwa Ta Kai Matsayin Koli A Duniya

Yawan Wutar Lantarkin Da Sin Ke Iya Samar Ta Amfani Da Karfin Ruwa Ta Kai Matsayin Koli A Duniya

May 22, 2025
Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 

Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 

May 22, 2025
Darussan Koyi Daga Salon Bunkasa Kasa Na Sin

Darussan Koyi Daga Salon Bunkasa Kasa Na Sin

May 22, 2025
Ƙungiyar ’yan Majalisar Dokokin Ƙasa Ta APC Ta Amince Da Takarar Tinubu A Zaɓen 2027 

Ƙungiyar ’yan Majalisar Dokokin Ƙasa Ta APC Ta Amince Da Takarar Tinubu A Zaɓen 2027 

May 22, 2025
Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Faransa

Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Faransa

May 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.