• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jirgin Sojoji Ya Yi Wa ‘Yan Ta’adda Luguden Wuta A Zamfara

by Abubakar Abba
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Jirgin Sojoji Ya Yi Wa ‘Yan Ta’adda Luguden Wuta A Zamfara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sama da ‘yan bindiga 100 aka ruwaito cewa, an kashe a yayin da sojin rundunar sama ta Operation Hadarin Daji suka yi luguden wuta ta jirgin yaki a karamar hukumar Maru a jihar Zamfara. 

An ruwaito cewa, luguden wutar wanda aka yi a ranar Talata, sojin sun yi shi ne a yayin da dandazon ‘yan bindigar suke shirin ficewa daga wani daji a jihar Zamfara zuwa jihar Kebbi, bisa nufin kai hare-hare a wasu kauyuka da ke a yankin.

  • Kungiya Ta Yi Allah Wadai Da Wallafa Hoton Gwamna Uba Sani A Cece-ku-cen Rabon Mukaman Siyasa
  • Kungiyar Kasashen Larabawa Ta Yi Taro Kan Rikicin Isra’ila da Falasdinu

Kazalika, wata babbar majiyar soji ta tabbatar da cewa, ‘yan bindigar sun samu bayanan cewa sojin na kan hanyar, wanda hakan ya tilsata su, dakatar da kudurinsu na zuwa kauyukan kai hare-haren, inda suka koma da baya zuwa hanyar Dansadau zuwa Maru.

Wannan ya bai wa sojin damar samun lago akan ‘yan binidar suka samu nasarar hallaka ‘yan bindigar sama da 100 ta hanyar luguden wuta ta sama tare da kone baburansu, inda kuma wasunsu, suka samu raunuka.

Bugu da kari, an ruwaito cewa, an birne gawarwakinsu a cikin kabari daya a dajin Sangeko na jihar Neja wasu kuma a Babban Doka a Maru a jihar Zamfara.

Labarai Masu Nasaba

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

Mai magana da yawun rundunar ta sojin sama ta Operation Hadarin Daji Kaftin Yahaya Ibrahim, ya tabbatar da yin luguden wutar, sai dai, ba a tabbatar da adadin ‘yan bindigar da suka mutu.

Bugu da kari, Daraktan yada labarai na rundunar sojin saman Nijeriya (DOPRI), Kwamando Edward Gabkwet, shi ma ya tabbatar da luguden wutar akan ‘yan bindigar a Zamfara, amma bai tabbatar da adadin ‘yan bindigar da aka kashe ba.

Zamfara dai, na daya daga cikin jihohi a arewacin kasar nan da ke ci gaba da fama da kalubalen hare-haren ‘yan bindiga, inda suma jihohin Nija, Kaduna, Sokoto, Kebbi da kuma Katsina, ke ci gaba da fuskantar wannan kalubalen.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ina Bukatar Hutu Kafin Na Ci Gaba Da Aikin Horaswa – Conte

Next Post

Ina Son Ci Gaba Da Zama Kyaftin Din Ingila Har Zuwa 2028 – Harry Kane

Related

Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

9 hours ago
An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja
Manyan Labarai

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

16 hours ago
Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?
Manyan Labarai

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

18 hours ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Bukatar Farfado Da Cibiyoyin Bincike Don Bunkasa Kasa

19 hours ago
EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo
Manyan Labarai

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

1 day ago
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu
Manyan Labarai

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

1 day ago
Next Post
Ina Son Ci Gaba Da Zama Kyaftin Din Ingila Har Zuwa 2028 – Harry Kane

Ina Son Ci Gaba Da Zama Kyaftin Din Ingila Har Zuwa 2028 - Harry Kane

LABARAI MASU NASABA

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

August 22, 2025
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

August 22, 2025
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

August 22, 2025
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

August 22, 2025
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

August 22, 2025
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

August 22, 2025
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

August 22, 2025
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

August 22, 2025
Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.