ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 18, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jirgin Sojoji Ya Yi Wa ‘Yan Ta’adda Luguden Wuta A Zamfara

by Abubakar Abba
3 years ago
Zamfara

Sama da ‘yan bindiga 100 aka ruwaito cewa, an kashe a yayin da sojin rundunar sama ta Operation Hadarin Daji suka yi luguden wuta ta jirgin yaki a karamar hukumar Maru a jihar Zamfara. 

An ruwaito cewa, luguden wutar wanda aka yi a ranar Talata, sojin sun yi shi ne a yayin da dandazon ‘yan bindigar suke shirin ficewa daga wani daji a jihar Zamfara zuwa jihar Kebbi, bisa nufin kai hare-hare a wasu kauyuka da ke a yankin.

  • Kungiya Ta Yi Allah Wadai Da Wallafa Hoton Gwamna Uba Sani A Cece-ku-cen Rabon Mukaman Siyasa
  • Kungiyar Kasashen Larabawa Ta Yi Taro Kan Rikicin Isra’ila da Falasdinu

Kazalika, wata babbar majiyar soji ta tabbatar da cewa, ‘yan bindigar sun samu bayanan cewa sojin na kan hanyar, wanda hakan ya tilsata su, dakatar da kudurinsu na zuwa kauyukan kai hare-haren, inda suka koma da baya zuwa hanyar Dansadau zuwa Maru.

ADVERTISEMENT

Wannan ya bai wa sojin damar samun lago akan ‘yan binidar suka samu nasarar hallaka ‘yan bindigar sama da 100 ta hanyar luguden wuta ta sama tare da kone baburansu, inda kuma wasunsu, suka samu raunuka.

Bugu da kari, an ruwaito cewa, an birne gawarwakinsu a cikin kabari daya a dajin Sangeko na jihar Neja wasu kuma a Babban Doka a Maru a jihar Zamfara.

LABARAI MASU NASABA

Kotu A Birtaniya Ta Wanke Diezani Daga Zargin Cin Hanci

‘Yan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gwande A Jihar Filato

Mai magana da yawun rundunar ta sojin sama ta Operation Hadarin Daji Kaftin Yahaya Ibrahim, ya tabbatar da yin luguden wutar, sai dai, ba a tabbatar da adadin ‘yan bindigar da suka mutu.

Bugu da kari, Daraktan yada labarai na rundunar sojin saman Nijeriya (DOPRI), Kwamando Edward Gabkwet, shi ma ya tabbatar da luguden wutar akan ‘yan bindigar a Zamfara, amma bai tabbatar da adadin ‘yan bindigar da aka kashe ba.

Zamfara dai, na daya daga cikin jihohi a arewacin kasar nan da ke ci gaba da fama da kalubalen hare-haren ‘yan bindiga, inda suma jihohin Nija, Kaduna, Sokoto, Kebbi da kuma Katsina, ke ci gaba da fuskantar wannan kalubalen.

Zamfara
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoma 67 Suka Amfana Da Horon Cibiyar  NIHORT
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilan Da Suka Sa Fannin Kiwo Ke Fuskantar Kalubale A Nijeriya —Gwamnatin Tarayya

MASU ALAKA

Kotu A Birtaniya Ta Wanke Diezani Daga Zargin Cin Hanci
Manyan Labarai

Kotu A Birtaniya Ta Wanke Diezani Daga Zargin Cin Hanci

June 18, 2026
’Yan Bindiga Sun Kashe Mutum Ɗaya, Sun Sace Limami Da Wasu Mutane 7 A Filato
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gwande A Jihar Filato

June 18, 2026
Matsalar Tsaro: Davido Ya Mayar Wa Rarara Martani Kan Rashin Tsaro
Manyan Labarai

Matsalar Tsaro: Davido Ya Mayar Wa Rarara Martani Kan Rashin Tsaro

June 18, 2026
Next Post
Ina Son Ci Gaba Da Zama Kyaftin Din Ingila Har Zuwa 2028 – Harry Kane

Ina Son Ci Gaba Da Zama Kyaftin Din Ingila Har Zuwa 2028 - Harry Kane

LABARAI MASU NASABA

2027: Tsohon Kakakin Majalisar Kaduna Abdulfatah Ya Zama Ɗan Takarar Gwamnan PRP

2027: Tsohon Kakakin Majalisar Kaduna Abdulfatah Ya Zama Ɗan Takarar Gwamnan PRP

June 18, 2026
Sojoji Sun Ceto Mutane 5 Da Aka Sace A Kogi

Sojoji Sun Ceto Mutane 5 Da Aka Sace A Kogi

June 18, 2026
Kotu A Birtaniya Ta Wanke Diezani Daga Zargin Cin Hanci

Kotu A Birtaniya Ta Wanke Diezani Daga Zargin Cin Hanci

June 18, 2026
’Yan Bindiga Sun Kashe Mutum Ɗaya, Sun Sace Limami Da Wasu Mutane 7 A Filato

‘Yan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gwande A Jihar Filato

June 18, 2026
Matsalar Tsaro: Davido Ya Mayar Wa Rarara Martani Kan Rashin Tsaro

Matsalar Tsaro: Davido Ya Mayar Wa Rarara Martani Kan Rashin Tsaro

June 18, 2026
Xi: Sin Na Gudanar Da Ayyukan Hadin Gwiwa Tsakanin Yankunan Gabashi Da Yammacin Kasar

Xi: Sin Na Gudanar Da Ayyukan Hadin Gwiwa Tsakanin Yankunan Gabashi Da Yammacin Kasar

June 17, 2026
Sin Ta Samar Da Tallafin Jin Kai Na Gaggawa Ga DRC Da AU

Sin Ta Samar Da Tallafin Jin Kai Na Gaggawa Ga DRC Da AU

June 17, 2026
Fahimtar Tattalin Arzikin Sin Na Watannin Biyar Na Farkon Bana Ta Kalmomi Guda Uku

Fahimtar Tattalin Arzikin Sin Na Watannin Biyar Na Farkon Bana Ta Kalmomi Guda Uku

June 17, 2026
Kasar Sin Za Ta Habaka Bude Fannonin Hada-Hadar Kudi Ga Duniya

Kasar Sin Za Ta Habaka Bude Fannonin Hada-Hadar Kudi Ga Duniya

June 17, 2026
Sin Na Gaggauta Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Kasa Da Kasa

Sin Na Gaggauta Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Kasa Da Kasa

June 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.