• English
  • Business News
Tuesday, July 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Ka Da Ki Kuskura Ki Zo Majalisar Tarayya’, Majalisar Dattawa Ta Sake Yi Wa Natasha Gargaɗi

by Muhammad
1 day ago
in Da ɗumi-ɗuminsa, Manyan Labarai
0
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Majalisar Dattawan Nijeriya ta sake jaddada gargaɗinta ga sanata mai wakiltar Kogi ta Tsakiya da aka dakatar, Natasha Akpoti-Uduaghan, da ta nisanci harabar Majalisar Tarayya, ta ce babu wani hukuncin kotu da ya tilasta dawo wa da ita majalisar.

Wannan sabon gargaɗi ya biyo bayan sanarwar da Akpoti-Uduaghan ta yi a ranar Asabar cewa za ta koma majalisar a ranar Talata, 22 ga Yuli, bisa hukuncin da babbar kotun tarayya da ke Abuja, ƙarƙashin Mai Shari’a Binta Nyako ta yanke kwanan nan.

  • Ba Zamu Dawo Da Sanata Natasha Zauren Majalisa Ba, Sai Mun Karɓi Kwafin Hukuncin Kotu – Majalisa
  • Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

A martani da shugaban kwamitin yaɗa labarai na majalisar dattawa, Sanata Yemi Adaramodu, ya fitar a ranar Lahadi, ya ƙaryata ikirarin sanatar, yana mai cewa kotun ta bayar da shawara ne, ba da umarnin dole ba, ga majalisar dattawa.

“A karo na uku, majalisar dattawa ta sake jaddada cewa babu wani hukuncin kotu da ya tilasta mayar da Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan kafin lokacin dakatarwarta ya ƙare,” cewar Adaramodu.

Ya bayyana cewa hukuncin kotun ya bayar da shawa ne kawai kan a duba tsarin dokokin majalisar da yiwuwar sake bitar hukuncin dakatarwar, wanda kotun ta bayyana yana iya zama mai tsauri.

Labarai Masu Nasaba

Tsohon Sakataren Gwamnatin Bauchi, Ibrahim Kashim, Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

Kotu Ta Dage Shari’ar Zargin Cin Hanci Da Ake Yi Wa Shugaban KANSIEC Na Kano Zuwa Nuwamba

Ya kuma jaddada cewa kotun ta tabbatar cewa majalisar ba ta karya doka ko kundin tsarin mulki ba a yanke wannan hukunci.

“A maimakon bayar da umarnin dole, kotun ta bayar da shawara ne,” in ji shi. “Har ila yau, kotun ta same ta da laifin raina kotu, ta ci ta tara ₦5 miliyan tare da umarnin bayar da haƙuri a manyan jaridu biyu da kuma shafinta na Facebook. Waɗannan umarni ba a cika su ba har yanzu.”

Ya gargadi Natasha cewa duk wani yunƙuri na dawo wa ta karfi ta hanyar amfani da fassarar da ba ta dace da hukuncin kotu ba, zai zama tauye doka da raina hurumin majalisa.

“Majalisar na jaddada cewa babu wani umarni na dole da ke tilasta dawowarta,” in ji shi. “Za mu yi nazari kan shawarar kotu a lokacin da ya dace, kuma za mu sanar da matakin da aka ɗauka.”

Majalisar ta buƙaci Natasha da ta girmama tsarin dokokin majalisa, kuma ta kaucewa harabar zauren.

“Ya kamata ta bari tsarin doka ya yi aikinsa,” cewar Adaramodu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GargaɗiKogiKotu Majalisar DattawaLauyoyiNatashaNijeriyaSanata
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Rufe Bikin Baje Koli Na CISCE Karo Na Uku

Next Post

Kamfanonin Kera Kayan Likitanci Na Duniya: Tsarin Samar Da Kayayyaki Na Kasar Sin Babban Ginshiki Ne

Related

Tsohon Sakataren Gwamnatin Bauchi, Ibrahim Kashim, Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP
Manyan Labarai

Tsohon Sakataren Gwamnatin Bauchi, Ibrahim Kashim, Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

2 minutes ago
Kotu Ta Dage Shari’ar Zargin Cin Hanci Da Ake Yi Wa Shugaban KANSIEC Na Kano Zuwa Nuwamba
Da ɗumi-ɗuminsa

Kotu Ta Dage Shari’ar Zargin Cin Hanci Da Ake Yi Wa Shugaban KANSIEC Na Kano Zuwa Nuwamba

9 hours ago
Kotu Ta Kori Ƙarar Da APC Ta Shigar Kan Dakatar Da Kuɗaɗen Ƙananan Hukumomin Kano
Da ɗumi-ɗuminsa

Kotu Ta Kori Ƙarar Da APC Ta Shigar Kan Dakatar Da Kuɗaɗen Ƙananan Hukumomin Kano

10 hours ago
Tsoffin Ƴansanda Sun Fara Zanga-Zangar Ƙuncin Rayuwa A Abuja
Manyan Labarai

Tsoffin Ƴansanda Sun Fara Zanga-Zangar Ƙuncin Rayuwa A Abuja

18 hours ago
Iran Ta Zargi Birtaniya, Faransa, Da Jamus Da Gazawa Kan Yarjejeniyar Nukiliyar 2015
Kasashen Ketare

Iran Ta Zargi Birtaniya, Faransa, Da Jamus Da Gazawa Kan Yarjejeniyar Nukiliyar 2015

19 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Tafka Gagarumar Sata A Bauchi, Sun Tafi Da Mutane 4
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Tafka Gagarumar Sata A Bauchi, Sun Tafi Da Mutane 4

21 hours ago
Next Post
Kamfanonin Kera Kayan Likitanci Na Duniya: Tsarin Samar Da Kayayyaki Na Kasar Sin Babban Ginshiki Ne

Kamfanonin Kera Kayan Likitanci Na Duniya: Tsarin Samar Da Kayayyaki Na Kasar Sin Babban Ginshiki Ne

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Sakataren Gwamnatin Bauchi, Ibrahim Kashim, Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

Tsohon Sakataren Gwamnatin Bauchi, Ibrahim Kashim, Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

July 22, 2025
Kasar Sin Na Fatan EU Za Ta Yi Aiki Da Ita Bisa Alkibla Guda Da Tsara Hadin Gwiwa Na Shekaru 50 Masu Zuwa

Kasar Sin Na Fatan EU Za Ta Yi Aiki Da Ita Bisa Alkibla Guda Da Tsara Hadin Gwiwa Na Shekaru 50 Masu Zuwa

July 21, 2025
PSC Ta Amince Da Ɗaga Darajar Jami’an ‘Yan Sanda 12 Daga Matakin CP Zuwa AIG, Da Sauransu

PSC Ta Amince Da Ɗaga Darajar Jami’an ‘Yan Sanda 12 Daga Matakin CP Zuwa AIG, Da Sauransu

July 21, 2025
Kotu Ta Dage Shari’ar Zargin Cin Hanci Da Ake Yi Wa Shugaban KANSIEC Na Kano Zuwa Nuwamba

Kotu Ta Dage Shari’ar Zargin Cin Hanci Da Ake Yi Wa Shugaban KANSIEC Na Kano Zuwa Nuwamba

July 21, 2025
Shirin Ba Da Horo A Kasar Sin Ya Taimaka Wa Inganta Masana’antar Gyadar Senegal

Shirin Ba Da Horo A Kasar Sin Ya Taimaka Wa Inganta Masana’antar Gyadar Senegal

July 21, 2025
Ana Iya Samun Masu Samar Da Kayayyaki Iri-Iri Cikin Awa Daya A Kasar Sin

Ana Iya Samun Masu Samar Da Kayayyaki Iri-Iri Cikin Awa Daya A Kasar Sin

July 21, 2025
Kotu Ta Kori Ƙarar Da APC Ta Shigar Kan Dakatar Da Kuɗaɗen Ƙananan Hukumomin Kano

Kotu Ta Kori Ƙarar Da APC Ta Shigar Kan Dakatar Da Kuɗaɗen Ƙananan Hukumomin Kano

July 21, 2025
Tsarin Samar Da Kayayyaki Na Sin Ya Hada Sassan Kasa Da Kasa

Tsarin Samar Da Kayayyaki Na Sin Ya Hada Sassan Kasa Da Kasa

July 21, 2025
Adadin Masu Amfani Da Intanet A Sin Ya Kai Sama Da Mutane Biliyan 1.12

Adadin Masu Amfani Da Intanet A Sin Ya Kai Sama Da Mutane Biliyan 1.12

July 21, 2025
Sin Ta Gina Tsarin Layin Dogo Da Manyan Hanyoyin Mota Da Na Aikewa Da Kunshin Sakwanni Mafi Girma A Duniya

Sin Ta Gina Tsarin Layin Dogo Da Manyan Hanyoyin Mota Da Na Aikewa Da Kunshin Sakwanni Mafi Girma A Duniya

July 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.