ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 21, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Iran Ta Zargi Birtaniya, Faransa, Da Jamus Da Gazawa Kan Yarjejeniyar Nukiliyar 2015

by Abubakar Sulaiman
11 months ago
Iran

Ƙasar Iran ta zargi Birtaniya, Faransa, da Jamus da karya alƙawuran da suka ɗauka a ƙarƙashin yarjejeniyar JCPOA da aka cimma a shekarar 2015, bayan ƙasashen uku sun yi barazanar dawo da takunkumi karya tattalin arziƙi ga ƙasar.

An ƙulla yarjejeniyar ne domin taƙaita shirye-shiryen nukiliyar Iran a maimakon sassauta mata takunkumi, sai dai yarjejeniyar ta fara rushewa ne bayan Amurka ta fice daga ciki a 2018 a lokacin shugaba Trump, inda ta dawo da manyan takunkumin karya tattalin arziƙi kan Iran.

  • Nijeriya Na Kashe Naira Miliyan 4.3 A Kullum Don Ciyar Da Wadanda Ke Jiran Hukuncin Kisa
  • Shugaba Xi Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Game Da Aikin Raya Birane 

Ko da yake Turawan sun yi alƙawarin bin yarjejeniyar, da ƙoƙarinsu na rage wa Iran raɗaɗin takunkumin Amurka bai haifar da ɗa mai ido ba. Manufofin kuɗi da Turai ta ƙaddamar domin taimaka wa Iran sun gaza, kamfanoni daga yammacin duniya kuma sun fice daga Iran, lamarin da ya tsananta matsin tattalin arziƙi a ƙasar. Iran na zargin ƙasashen Turai da cewa sun tsaya ne a kan magana kawai ba tare da aiki ba.

ADVERTISEMENT

A ranar Litinin, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen Iran, Esmail Baqaei, ya soki Turai bisa abin da ya kira da “gazawa da sakaci” wajen aiwatar da yarjejeniyar, yana mai kiran barazanar da suke yi a yanzu da “rashin adalci” kuma “cike da son zuciya”. Wannan na zuwa ne bayan Turawan sun nuna damuwa kan matakin da Iran ta kai na inganta sinadarin uranium zuwa kashi 60% wanda hukumar IAEA ta ce ya ninka ƙima mafi girma da yarjejeniyar JCPOA ta amince da shi wato 3.67%.

Ƙasashen Birtaniya, Faransa da Jamus na shirin amfani da tsarin “snapback” na Majalisar Ɗinkin Duniya wanda ke ba su damar dawo da takunkumi idan aka samu Iran da laifin karya yarjejeniya. Baqaei ya kare matakin Iran da cewa ƙasar ta fara rage bin yarjejeniyar ne bayan ficewar Amurka da gazawar Turai wajen cika alƙawari, yana mai cewa duk matakan Iran sun yi daidai da sharuɗɗan yarjejeniyar dangane da martani na musaya.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ceto Mutane 22 A Jihar Sakkwato

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

Wannan rikici ya ƙara jaddada gazawar yarjejeniyar ta JCPOA kuma ya tayar da ƙarin shakku kan yiwuwar dawo da tattaunawar diflomasiyya don taƙaita shirye-shiryen nukiliyar Iran. Tunda kowanne ɓangare ke jifan ɗayan da laifi, yanzu dai alamar dawowa ga yarjejeniyar 2015 na ƙara dusashewa.

Iran
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Farashin Mai Na Iya Sauka Har Zuwa Dala $60 Kan Kowanne Ganga
  • Abubakar Sulaiman
    Sojoji Sun Yi Wa Ƴan Bindiga Mummunar Barna A Katsina
  • Abubakar Sulaiman
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gundumar Gwande A Jihar Filato

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kashe Mayakan Boko Haram 6, Sun Kama Wasu A Borno
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Mutane 22 A Jihar Sakkwato

June 20, 2026
Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa
Manyan Labarai

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

June 19, 2026
Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160
Manyan Labarai

Tinubu Ya Ba Da Umarnin Tsaurara Tsaro A NIPSS Bayan Harin ’Yan Bindiga

June 19, 2026
Next Post
Tsoffin Ƴansanda Sun Fara Zanga-Zangar Ƙuncin Rayuwa A Abuja

Tsoffin Ƴansanda Sun Fara Zanga-Zangar Ƙuncin Rayuwa A Abuja

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Wasa 23 Da Eric Chelle Ya Gayyata Domin Buga Wasannin Sada Zumunci 

Duk Da Rashin Halartar ‘Super Eagles’ Gasar Kofin Duniya, Nijeriya Ba Ta Rasa Wakilai Ba

June 20, 2026
Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin

Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin

June 20, 2026
Darussan Da Suka Fi Dacewa A Fahimta Daga Alkur’ani A Wannan Zamanin (2)

Hijira: Malaman Musulunci Sun Buƙaci  Musulmi Su Yi Riƙo Da Gaskiya Da Adalci

June 20, 2026
Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire

Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire

June 20, 2026
Nijeriya

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Sin Na Kira Ga Al’ummun Kasa Da Kasa Da Su Himmatu Wajen Tallafawa Ayyukan Jin kai

Sin Na Kira Ga Al’ummun Kasa Da Kasa Da Su Himmatu Wajen Tallafawa Ayyukan Jin kai

June 20, 2026
Sojoji Sun Kashe Mayakan Boko Haram 6, Sun Kama Wasu A Borno

Sojoji Sun Ceto Mutane 22 A Jihar Sakkwato

June 20, 2026
A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki

A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki

June 20, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

June 20, 2026
IMF

Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

June 20, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.