ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Iran Ta Zargi Birtaniya, Faransa, Da Jamus Da Gazawa Kan Yarjejeniyar Nukiliyar 2015

by Abubakar Sulaiman
12 months ago
Iran

Ƙasar Iran ta zargi Birtaniya, Faransa, da Jamus da karya alƙawuran da suka ɗauka a ƙarƙashin yarjejeniyar JCPOA da aka cimma a shekarar 2015, bayan ƙasashen uku sun yi barazanar dawo da takunkumi karya tattalin arziƙi ga ƙasar.

An ƙulla yarjejeniyar ne domin taƙaita shirye-shiryen nukiliyar Iran a maimakon sassauta mata takunkumi, sai dai yarjejeniyar ta fara rushewa ne bayan Amurka ta fice daga ciki a 2018 a lokacin shugaba Trump, inda ta dawo da manyan takunkumin karya tattalin arziƙi kan Iran.

  • Nijeriya Na Kashe Naira Miliyan 4.3 A Kullum Don Ciyar Da Wadanda Ke Jiran Hukuncin Kisa
  • Shugaba Xi Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Game Da Aikin Raya Birane 

Ko da yake Turawan sun yi alƙawarin bin yarjejeniyar, da ƙoƙarinsu na rage wa Iran raɗaɗin takunkumin Amurka bai haifar da ɗa mai ido ba. Manufofin kuɗi da Turai ta ƙaddamar domin taimaka wa Iran sun gaza, kamfanoni daga yammacin duniya kuma sun fice daga Iran, lamarin da ya tsananta matsin tattalin arziƙi a ƙasar. Iran na zargin ƙasashen Turai da cewa sun tsaya ne a kan magana kawai ba tare da aiki ba.

ADVERTISEMENT

A ranar Litinin, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen Iran, Esmail Baqaei, ya soki Turai bisa abin da ya kira da “gazawa da sakaci” wajen aiwatar da yarjejeniyar, yana mai kiran barazanar da suke yi a yanzu da “rashin adalci” kuma “cike da son zuciya”. Wannan na zuwa ne bayan Turawan sun nuna damuwa kan matakin da Iran ta kai na inganta sinadarin uranium zuwa kashi 60% wanda hukumar IAEA ta ce ya ninka ƙima mafi girma da yarjejeniyar JCPOA ta amince da shi wato 3.67%.

Ƙasashen Birtaniya, Faransa da Jamus na shirin amfani da tsarin “snapback” na Majalisar Ɗinkin Duniya wanda ke ba su damar dawo da takunkumi idan aka samu Iran da laifin karya yarjejeniya. Baqaei ya kare matakin Iran da cewa ƙasar ta fara rage bin yarjejeniyar ne bayan ficewar Amurka da gazawar Turai wajen cika alƙawari, yana mai cewa duk matakan Iran sun yi daidai da sharuɗɗan yarjejeniyar dangane da martani na musaya.

LABARAI MASU NASABA

Mutum 1 Ya Mutu, 7 Sun Jikkata Yayin Da Ginin Majalisar Dokokin Gombe Ya Rufta

Duk Da Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Ƴan Nijeriya Na Fama Da Tsadar Man Fetur

Wannan rikici ya ƙara jaddada gazawar yarjejeniyar ta JCPOA kuma ya tayar da ƙarin shakku kan yiwuwar dawo da tattaunawar diflomasiyya don taƙaita shirye-shiryen nukiliyar Iran. Tunda kowanne ɓangare ke jifan ɗayan da laifi, yanzu dai alamar dawowa ga yarjejeniyar 2015 na ƙara dusashewa.

Iran
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Mutum 1 Ya Mutu, 7 Sun Jikkata Yayin Da Ginin Majalisar Dokokin Gombe Ya Rufta
  • Abubakar Sulaiman
    Duk Da Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Ƴan Nijeriya Na Fama Da Tsadar Man Fetur
  • Abubakar Sulaiman
    Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga A Wani Ƙauyen Katsina
  • Abubakar Sulaiman
    Yadda Jana’izar Ruhullah Khomeini Ta Shiga Kundin Tarihi Na Guinness

MASU ALAKA

Mutum 1 Ya Mutu, 7 Sun Jikkata Yayin Da Ginin Majalisar Dokokin Gombe Ya Rufta
Manyan Labarai

Mutum 1 Ya Mutu, 7 Sun Jikkata Yayin Da Ginin Majalisar Dokokin Gombe Ya Rufta

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Manyan Labarai

Duk Da Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Ƴan Nijeriya Na Fama Da Tsadar Man Fetur

July 11, 2026
2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa
Da ɗumi-ɗuminsa

2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

July 10, 2026
Next Post
Tsoffin Ƴansanda Sun Fara Zanga-Zangar Ƙuncin Rayuwa A Abuja

Tsoffin Ƴansanda Sun Fara Zanga-Zangar Ƙuncin Rayuwa A Abuja

LABARAI MASU NASABA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Ra’ayin Al’umma Game Da Shirin Gwamnati Na Sake Fasalin Hukumar NYSC

July 11, 2026
Mutum 1 Ya Mutu, 7 Sun Jikkata Yayin Da Ginin Majalisar Dokokin Gombe Ya Rufta

Mutum 1 Ya Mutu, 7 Sun Jikkata Yayin Da Ginin Majalisar Dokokin Gombe Ya Rufta

July 11, 2026

Ronaldo Da Ƴanwasan Da Suka Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe A Rayuwarsu

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

NDLEA Ta Cafke Ƴar Shekara 67 Da Hodar Iblis Da Aka Ɓoye A Cikin Ayaba

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Duk Da Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Ƴan Nijeriya Na Fama Da Tsadar Man Fetur

July 11, 2026
Kasar Sin Ta Fitar Da Shirin Kai Wa Matakin Koli Na Fitar Da Hayakin Carbon

Kasar Sin Ta Fitar Da Shirin Kai Wa Matakin Koli Na Fitar Da Hayakin Carbon

July 10, 2026
Sin Ta Yi Nasarar Dawo Da Rokar Da Ake Sarrafa Dawowarta A Tashin Farko Na Samfurin Long March-10B

Sin Ta Yi Nasarar Dawo Da Rokar Da Ake Sarrafa Dawowarta A Tashin Farko Na Samfurin Long March-10B

July 10, 2026
CMG Ya Gabatar Da Shiri Na Musamman Mai Taken “Samun Nasara Dangane Da AI+” A Ketare

CMG Ya Gabatar Da Shiri Na Musamman Mai Taken “Samun Nasara Dangane Da AI+” A Ketare

July 10, 2026
Zargin Da Wasu Sassa Ke Yiwa Kasar Sin Na Takure Sauran Kasashe Masu Tasowa Ba Shi da Tushe Ko Makama

Zargin Da Wasu Sassa Ke Yiwa Kasar Sin Na Takure Sauran Kasashe Masu Tasowa Ba Shi da Tushe Ko Makama

July 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.