• English
  • Business News
Sunday, October 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Ka Da Ki Kuskura Ki Zo Majalisar Tarayya’, Majalisar Dattawa Ta Sake Yi Wa Natasha Gargaɗi

by Muhammad
3 months ago
Natasha

Majalisar Dattawan Nijeriya ta sake jaddada gargaɗinta ga sanata mai wakiltar Kogi ta Tsakiya da aka dakatar, Natasha Akpoti-Uduaghan, da ta nisanci harabar Majalisar Tarayya, ta ce babu wani hukuncin kotu da ya tilasta dawo wa da ita majalisar.

Wannan sabon gargaɗi ya biyo bayan sanarwar da Akpoti-Uduaghan ta yi a ranar Asabar cewa za ta koma majalisar a ranar Talata, 22 ga Yuli, bisa hukuncin da babbar kotun tarayya da ke Abuja, ƙarƙashin Mai Shari’a Binta Nyako ta yanke kwanan nan.

  • Ba Zamu Dawo Da Sanata Natasha Zauren Majalisa Ba, Sai Mun Karɓi Kwafin Hukuncin Kotu – Majalisa
  • Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

A martani da shugaban kwamitin yaɗa labarai na majalisar dattawa, Sanata Yemi Adaramodu, ya fitar a ranar Lahadi, ya ƙaryata ikirarin sanatar, yana mai cewa kotun ta bayar da shawara ne, ba da umarnin dole ba, ga majalisar dattawa.

“A karo na uku, majalisar dattawa ta sake jaddada cewa babu wani hukuncin kotu da ya tilasta mayar da Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan kafin lokacin dakatarwarta ya ƙare,” cewar Adaramodu.

Ya bayyana cewa hukuncin kotun ya bayar da shawa ne kawai kan a duba tsarin dokokin majalisar da yiwuwar sake bitar hukuncin dakatarwar, wanda kotun ta bayyana yana iya zama mai tsauri.

LABARAI MASU NASABA

Gwarzon Banki Na Shekarar 2025 Bankin Providus

Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

Ya kuma jaddada cewa kotun ta tabbatar cewa majalisar ba ta karya doka ko kundin tsarin mulki ba a yanke wannan hukunci.

“A maimakon bayar da umarnin dole, kotun ta bayar da shawara ne,” in ji shi. “Har ila yau, kotun ta same ta da laifin raina kotu, ta ci ta tara ₦5 miliyan tare da umarnin bayar da haƙuri a manyan jaridu biyu da kuma shafinta na Facebook. Waɗannan umarni ba a cika su ba har yanzu.”

Ya gargadi Natasha cewa duk wani yunƙuri na dawo wa ta karfi ta hanyar amfani da fassarar da ba ta dace da hukuncin kotu ba, zai zama tauye doka da raina hurumin majalisa.

“Majalisar na jaddada cewa babu wani umarni na dole da ke tilasta dawowarta,” in ji shi. “Za mu yi nazari kan shawarar kotu a lokacin da ya dace, kuma za mu sanar da matakin da aka ɗauka.”

Majalisar ta buƙaci Natasha da ta girmama tsarin dokokin majalisa, kuma ta kaucewa harabar zauren.

“Ya kamata ta bari tsarin doka ya yi aikinsa,” cewar Adaramodu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji
Manyan Labarai

Gwarzon Banki Na Shekarar 2025 Bankin Providus

October 25, 2025
Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI
Manyan Labarai

Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

October 25, 2025
Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka
Kiwon Lafiya

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

October 25, 2025
Next Post
Kamfanonin Kera Kayan Likitanci Na Duniya: Tsarin Samar Da Kayayyaki Na Kasar Sin Babban Ginshiki Ne

Kamfanonin Kera Kayan Likitanci Na Duniya: Tsarin Samar Da Kayayyaki Na Kasar Sin Babban Ginshiki Ne

LABARAI MASU NASABA

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 25, 2025

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

October 25, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Banki Na Shekarar 2025 Bankin Providus

October 25, 2025
Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

October 25, 2025
Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

October 25, 2025
An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

October 25, 2025

Daɓid Adeyemi

October 25, 2025
Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD

Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD

October 25, 2025
Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

October 25, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.