• English
  • Business News
Tuesday, October 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ka Yi Murabus Yanzu Ko Mu Tsige Ka – ‘Yan Majalisa Ga Kakakin Majalisar Bauchi

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Majalisa

‘Yan Majalisar Dokokin Jihar Bauchi 22, sun bukaci Kakakin Majalisar Dokokin Jihar, Rt. Hon. Abubakar Y Sulaiman da cikin ruwan sanyi ya amince ya yi murabus ba tare da bata wani lokaci ba ko su tsige shi nan ba da jimawa.

‘Yan majalisar a karkashin jagorancin mataimakin shugaban masu rinjaye, Baballe Abubakar Dambam mai wakiltar mazabar Dambam/Dagauda/Jalam, a ranar Juma’a sun jefa kuri’ar rashin kwarin guiwa kan jagororin majalisar bisa abun da suka kira rashin iya tafiyar da harkoki jagoranci yadda ya dace.

  • Mohamed Salah Ya Sabunta Kwantiraginsa A Liverpool
  • Dan Majalisar Edo Jude Ise-Idehen, Ya Rasu

Da ya ke ganawa da ‘yan jarida bayan kammala zaman nasu, Baballe ya ce “Za mu dauka daga yau Juma’a’ babu jagoranci a majisar dokokin Jihar, ina daga cikin jagororin amma mun ji a ranmu cewa yanzu ne ya dace mu yi hakan. Don haka mun kada kuri’ar rashin gamsuwa da dukkanin jagororin majalisar dokokin Jihar Bauchi.

“Muna kira ga shugabannin majalisar da su yi murabus cikin ruwan sanyi su mika takardun ajiye aiki ga akawun majalisa kawai, don samun damar gudanar da sabon zaben shugabanni.”

Mambobin sun bukaci gwamnatin jihar Bauchi a karkashin jagorancin Bala Muhammad da kada su dauka zagon kasa suke shirya wa gwamnatin jihar, illa kokarin da suke yi na ganin an samu gyara cikin lamuran da suka shafi majalisar.

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu

Tsohon Ɗan Majalisar Bayelsa Ya Shawarci Jonathan Ya Guji Neman Takara A 2027

“Muna son a samu gyara ne domin muddin aka ci gaba da tafiya karkashin jagorancin da ke a nan yanzu babu wani abin da ke tafiya yadda ya dace. Muna tabbatar wa gwamna cewa canjin da za a samu a majalisar ba zai shafi akalar majalisar dokokin Jihar da bangaren gwamnatin ba.”

Kazalika, mambobin majalisar sun nuna damuwarsu bisa yadda aka samu koma baya wajen tafiyar da harkokin aikin hajji na gaza gudanar da tsare-tsaren da suka dace a hajjin bana.

Sun kuma nuna damuwarsu yadda ba a kula da su ba wajen rabon kujerun zuwa Makkah duk kuwa da cewa kakakin majalisar jihar shi ne mataimakin shugaban kwamitin tsare-tsaren na aikin hajjin.

Da yake maida martani kan wannan matakin, babban mai bai wa gwamna shawara kan harkokin majalisa, Sani Mohammed Burra, ya ce matsalolin da aka samu kan aikin hajji a bana ba jihar Bauchi ce kadai abun ya shafa ba, ya ce kasa ne baki daya sakamakon karancin adadin kujeru da aka ware wa jihar.

Dangane da rikicin da ya kunno kai a majalisar kuwa, ya ce rikicin cikin gida ne kuma za a shawo kansa nan kusa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu
Siyasa

Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu

October 20, 2025
Tsohon Ɗan Majalisar Bayelsa Ya Shawarci Jonathan Ya Guji Neman Takara A 2027
Siyasa

Tsohon Ɗan Majalisar Bayelsa Ya Shawarci Jonathan Ya Guji Neman Takara A 2027

October 17, 2025
Gwamnan Edo Ya Umarci Kwamishinoni Su Riƙa Sanya Hular Tinubu
Siyasa

Gwamnan Edo Ya Umarci Kwamishinoni Su Riƙa Sanya Hular Tinubu

October 16, 2025
Next Post
An Gurfanar Da Masu Gadi Kan Zargin Satar ‘Cornflakes’ Din Miliyan 2.1

Za A Jefe Mutum Uku Da Dutse Har Su Mutu Har Lahira Kan Laifin Yin Luwadi A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

An Ɗage Shari’ar Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Zuwa 19 Ga Watan Nuwamba

An Ɗage Shari’ar Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Zuwa 19 Ga Watan Nuwamba

October 21, 2025
Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa

Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa

October 21, 2025
Mutane 3,433 Sun Rasu a Hatsarin Mota 6,858 Cikin Wata 9 A Nijeriya – FRSC

Mutane 3,433 Sun Rasu a Hatsarin Mota 6,858 Cikin Wata 9 A Nijeriya – FRSC

October 21, 2025
NLC Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Don Biyan Buƙatun ASUU Da Sauran Ƙungiyoyi 

NLC Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Don Biyan Buƙatun ASUU Da Sauran Ƙungiyoyi 

October 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Ɗan Fashi Sanye Da Kayan NYSC A Enugu

October 21, 2025
Gwamnatin Gombe Ta Ceto Yara 59 Da Aka Yi Safararsu

Gwamnatin Gombe Ta Ceto Yara 59 Da Aka Yi Safararsu

October 21, 2025
Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

October 20, 2025
An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

October 20, 2025
Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

October 20, 2025
Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu

Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu

October 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.