ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ka Yi Murabus Yanzu Ko Mu Tsige Ka – ‘Yan Majalisa Ga Kakakin Majalisar Bauchi

by Khalid Idris Doya
4 years ago
Majalisa

‘Yan Majalisar Dokokin Jihar Bauchi 22, sun bukaci Kakakin Majalisar Dokokin Jihar, Rt. Hon. Abubakar Y Sulaiman da cikin ruwan sanyi ya amince ya yi murabus ba tare da bata wani lokaci ba ko su tsige shi nan ba da jimawa.

‘Yan majalisar a karkashin jagorancin mataimakin shugaban masu rinjaye, Baballe Abubakar Dambam mai wakiltar mazabar Dambam/Dagauda/Jalam, a ranar Juma’a sun jefa kuri’ar rashin kwarin guiwa kan jagororin majalisar bisa abun da suka kira rashin iya tafiyar da harkoki jagoranci yadda ya dace.

  • Mohamed Salah Ya Sabunta Kwantiraginsa A Liverpool
  • Dan Majalisar Edo Jude Ise-Idehen, Ya Rasu

Da ya ke ganawa da ‘yan jarida bayan kammala zaman nasu, Baballe ya ce “Za mu dauka daga yau Juma’a’ babu jagoranci a majisar dokokin Jihar, ina daga cikin jagororin amma mun ji a ranmu cewa yanzu ne ya dace mu yi hakan. Don haka mun kada kuri’ar rashin gamsuwa da dukkanin jagororin majalisar dokokin Jihar Bauchi.

ADVERTISEMENT

“Muna kira ga shugabannin majalisar da su yi murabus cikin ruwan sanyi su mika takardun ajiye aiki ga akawun majalisa kawai, don samun damar gudanar da sabon zaben shugabanni.”

Mambobin sun bukaci gwamnatin jihar Bauchi a karkashin jagorancin Bala Muhammad da kada su dauka zagon kasa suke shirya wa gwamnatin jihar, illa kokarin da suke yi na ganin an samu gyara cikin lamuran da suka shafi majalisar.

LABARAI MASU NASABA

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

“Muna son a samu gyara ne domin muddin aka ci gaba da tafiya karkashin jagorancin da ke a nan yanzu babu wani abin da ke tafiya yadda ya dace. Muna tabbatar wa gwamna cewa canjin da za a samu a majalisar ba zai shafi akalar majalisar dokokin Jihar da bangaren gwamnatin ba.”

Kazalika, mambobin majalisar sun nuna damuwarsu bisa yadda aka samu koma baya wajen tafiyar da harkokin aikin hajji na gaza gudanar da tsare-tsaren da suka dace a hajjin bana.

Sun kuma nuna damuwarsu yadda ba a kula da su ba wajen rabon kujerun zuwa Makkah duk kuwa da cewa kakakin majalisar jihar shi ne mataimakin shugaban kwamitin tsare-tsaren na aikin hajjin.

Da yake maida martani kan wannan matakin, babban mai bai wa gwamna shawara kan harkokin majalisa, Sani Mohammed Burra, ya ce matsalolin da aka samu kan aikin hajji a bana ba jihar Bauchi ce kadai abun ya shafa ba, ya ce kasa ne baki daya sakamakon karancin adadin kujeru da aka ware wa jihar.

Dangane da rikicin da ya kunno kai a majalisar kuwa, ya ce rikicin cikin gida ne kuma za a shawo kansa nan kusa.

Majalisa
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai Na Aikin Hajjin Bana Na Bauchi Ya Rasu A Saudiyya
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Na Bar Harƙoƙin Siyasa Gaba Ɗaya – Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi, Air Marshal Saddique Baba

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe
Siyasa

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM
Siyasa

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

June 3, 2026
Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
Siyasa

Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada

June 1, 2026
Next Post
An Gurfanar Da Masu Gadi Kan Zargin Satar ‘Cornflakes’ Din Miliyan 2.1

Za A Jefe Mutum Uku Da Dutse Har Su Mutu Har Lahira Kan Laifin Yin Luwadi A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.