• Leadership Hausa
Thursday, March 23, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ka Yi Murabus Yanzu Ko Mu Tsige Ka – ‘Yan Majalisa Ga Kakakin Majalisar Bauchi

by Khalid Idris Doya
9 months ago
in Siyasa
0
Ka Yi Murabus Yanzu Ko Mu Tsige Ka – ‘Yan Majalisa Ga Kakakin Majalisar Bauchi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

‘Yan Majalisar Dokokin Jihar Bauchi 22, sun bukaci Kakakin Majalisar Dokokin Jihar, Rt. Hon. Abubakar Y Sulaiman da cikin ruwan sanyi ya amince ya yi murabus ba tare da bata wani lokaci ba ko su tsige shi nan ba da jimawa.

‘Yan majalisar a karkashin jagorancin mataimakin shugaban masu rinjaye, Baballe Abubakar Dambam mai wakiltar mazabar Dambam/Dagauda/Jalam, a ranar Juma’a sun jefa kuri’ar rashin kwarin guiwa kan jagororin majalisar bisa abun da suka kira rashin iya tafiyar da harkoki jagoranci yadda ya dace.

  • Mohamed Salah Ya Sabunta Kwantiraginsa A Liverpool
  • Dan Majalisar Edo Jude Ise-Idehen, Ya Rasu

Da ya ke ganawa da ‘yan jarida bayan kammala zaman nasu, Baballe ya ce “Za mu dauka daga yau Juma’a’ babu jagoranci a majisar dokokin Jihar, ina daga cikin jagororin amma mun ji a ranmu cewa yanzu ne ya dace mu yi hakan. Don haka mun kada kuri’ar rashin gamsuwa da dukkanin jagororin majalisar dokokin Jihar Bauchi.

“Muna kira ga shugabannin majalisar da su yi murabus cikin ruwan sanyi su mika takardun ajiye aiki ga akawun majalisa kawai, don samun damar gudanar da sabon zaben shugabanni.”

Mambobin sun bukaci gwamnatin jihar Bauchi a karkashin jagorancin Bala Muhammad da kada su dauka zagon kasa suke shirya wa gwamnatin jihar, illa kokarin da suke yi na ganin an samu gyara cikin lamuran da suka shafi majalisar.

Labarai Masu Nasaba

Jihar Zamfara: Dauda Lawal Dare Na Jam’iyyar PDP Ya Kayar Da Gwamna Matawalle Na APC

PDP Na Zargin Gwamnan Zamfara Da Yunkurin Murde Sakamakon Karamar Hukumar Maradun

“Muna son a samu gyara ne domin muddin aka ci gaba da tafiya karkashin jagorancin da ke a nan yanzu babu wani abin da ke tafiya yadda ya dace. Muna tabbatar wa gwamna cewa canjin da za a samu a majalisar ba zai shafi akalar majalisar dokokin Jihar da bangaren gwamnatin ba.”

Kazalika, mambobin majalisar sun nuna damuwarsu bisa yadda aka samu koma baya wajen tafiyar da harkokin aikin hajji na gaza gudanar da tsare-tsaren da suka dace a hajjin bana.

Sun kuma nuna damuwarsu yadda ba a kula da su ba wajen rabon kujerun zuwa Makkah duk kuwa da cewa kakakin majalisar jihar shi ne mataimakin shugaban kwamitin tsare-tsaren na aikin hajjin.

Da yake maida martani kan wannan matakin, babban mai bai wa gwamna shawara kan harkokin majalisa, Sani Mohammed Burra, ya ce matsalolin da aka samu kan aikin hajji a bana ba jihar Bauchi ce kadai abun ya shafa ba, ya ce kasa ne baki daya sakamakon karancin adadin kujeru da aka ware wa jihar.

Dangane da rikicin da ya kunno kai a majalisar kuwa, ya ce rikicin cikin gida ne kuma za a shawo kansa nan kusa.

Tags: BauchimajalisaSiyasa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mohamed Salah Ya Sabunta Kwantiraginsa A Liverpool

Next Post

Za A Jefe Mutum Uku Da Dutse Har Su Mutu Har Lahira Kan Laifin Yin Luwadi A Bauchi

Related

Jihar Zamfara: Dauda Lawal Dare Na Jam’iyyar PDP Ya Kayar Da Gwamna Matawalle Na APC
Siyasa

Jihar Zamfara: Dauda Lawal Dare Na Jam’iyyar PDP Ya Kayar Da Gwamna Matawalle Na APC

2 days ago
Babban Kwamatin Ayyuka Na Jam’iyyar PDP Na kasa Ya Gana Da ‘Yan Takarar Gwamna Na Jam’iyyar
Siyasa

PDP Na Zargin Gwamnan Zamfara Da Yunkurin Murde Sakamakon Karamar Hukumar Maradun

3 days ago
Da Dumi-Dumi: INEC Ta Ce Sakamakon Zaben Gwamnan Kebbi Bai Kammalu Ba
Siyasa

Da Dumi-Dumi: INEC Ta Ce Sakamakon Zaben Gwamnan Kebbi Bai Kammalu Ba

3 days ago
Dan Takarar PDP, Hon. Dauda Lawal Shi Ne A Gaba A Zaben Gwamnan Zamfara
Siyasa

Dan Takarar PDP, Hon. Dauda Lawal Shi Ne A Gaba A Zaben Gwamnan Zamfara

4 days ago
Dogara Ya Mara Wa Dan Takarar Gwamnan APC A Bauchi Baya
Siyasa

Dogara Ya Mara Wa Dan Takarar Gwamnan APC A Bauchi Baya

2 weeks ago
Rikicin PDP: Bayan Ganawar Tinubu Da Wike A Landan, Ba Shiri Atiku Ya Garzaya Birtaniya
Siyasa

Wike Ya Yi Wa Atiku Shagube Kan Zanga-Zangar Neman INEC Ta Soke Zaben Shugaban Kasa

2 weeks ago
Next Post
An Gurfanar Da Masu Gadi Kan Zargin Satar ‘Cornflakes’ Din Miliyan 2.1

Za A Jefe Mutum Uku Da Dutse Har Su Mutu Har Lahira Kan Laifin Yin Luwadi A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Siyasantar Da Batun Gano Asalin COVID-19 Dabara Ce Ta Boye Gaskiya

Siyasantar Da Batun Gano Asalin COVID-19 Dabara Ce Ta Boye Gaskiya

March 23, 2023
Jirgin Saman Nijeriya Zai Fara Aiki Kafin Ranar 29 Ga Mayu

Jirgin Saman Nijeriya Zai Fara Aiki Kafin Ranar 29 Ga Mayu

March 23, 2023
Ina So A Ko’ina A Ji Hikima Da Fasaharmu – Yusuf King

Ina So A Ko’ina A Ji Hikima Da Fasaharmu – Yusuf King

March 23, 2023
Hadin Gwiwar Sin Da Rasha Na Da Muhimmanci Sosai Ga Duniya

Hadin Gwiwar Sin Da Rasha Na Da Muhimmanci Sosai Ga Duniya

March 23, 2023
Ramadan: Lokutan Sahur Da Buda-baki Na Azumin Gobe A Wasu Birane

Ramadan: Lokutan Sahur Da Buda-baki Na Azumin Gobe A Wasu Birane

March 23, 2023
Gyare-gyare Su Kan Faru Ne Bisa Sauyawar Tunanin Mutum

Gyare-gyare Su Kan Faru Ne Bisa Sauyawar Tunanin Mutum

March 23, 2023
NLC Za Ta Shiga Yajin Aiki Saboda Karancin Kudi A Nijeriya

NLC Za Ta Shiga Yajin Aiki Saboda Karancin Kudi A Nijeriya

March 23, 2023
FEC Ta Amince Da Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Wajen Gina Barikin Jami’an NDLEA

FEC Ta Amince Da Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Wajen Gina Barikin Jami’an NDLEA

March 23, 2023
Mata Magoya Bayan PDP Na Zanga-Zangar Watsi Da Sakamakon Zaben Gwamnan Kaduna

Mata Magoya Bayan PDP Na Zanga-Zangar Watsi Da Sakamakon Zaben Gwamnan Kaduna

March 23, 2023
DSS Ce Abokiyar Hamayyar Mu A Jihar Kano Ba APC Ba – NNPP

NNPP Ta Zargi Gwamnatin Ganduje Da Kai Hare-Hare Kan Mazauna Kano

March 23, 2023
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.