• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ka Yi Murabus Yanzu Ko Mu Tsige Ka – ‘Yan Majalisa Ga Kakakin Majalisar Bauchi

byKhalid Idris Doya
3 years ago
Majalisa

‘Yan Majalisar Dokokin Jihar Bauchi 22, sun bukaci Kakakin Majalisar Dokokin Jihar, Rt. Hon. Abubakar Y Sulaiman da cikin ruwan sanyi ya amince ya yi murabus ba tare da bata wani lokaci ba ko su tsige shi nan ba da jimawa.

‘Yan majalisar a karkashin jagorancin mataimakin shugaban masu rinjaye, Baballe Abubakar Dambam mai wakiltar mazabar Dambam/Dagauda/Jalam, a ranar Juma’a sun jefa kuri’ar rashin kwarin guiwa kan jagororin majalisar bisa abun da suka kira rashin iya tafiyar da harkoki jagoranci yadda ya dace.

  • Mohamed Salah Ya Sabunta Kwantiraginsa A Liverpool
  • Dan Majalisar Edo Jude Ise-Idehen, Ya Rasu

Da ya ke ganawa da ‘yan jarida bayan kammala zaman nasu, Baballe ya ce “Za mu dauka daga yau Juma’a’ babu jagoranci a majisar dokokin Jihar, ina daga cikin jagororin amma mun ji a ranmu cewa yanzu ne ya dace mu yi hakan. Don haka mun kada kuri’ar rashin gamsuwa da dukkanin jagororin majalisar dokokin Jihar Bauchi.

“Muna kira ga shugabannin majalisar da su yi murabus cikin ruwan sanyi su mika takardun ajiye aiki ga akawun majalisa kawai, don samun damar gudanar da sabon zaben shugabanni.”

Mambobin sun bukaci gwamnatin jihar Bauchi a karkashin jagorancin Bala Muhammad da kada su dauka zagon kasa suke shirya wa gwamnatin jihar, illa kokarin da suke yi na ganin an samu gyara cikin lamuran da suka shafi majalisar.

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas

Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara

“Muna son a samu gyara ne domin muddin aka ci gaba da tafiya karkashin jagorancin da ke a nan yanzu babu wani abin da ke tafiya yadda ya dace. Muna tabbatar wa gwamna cewa canjin da za a samu a majalisar ba zai shafi akalar majalisar dokokin Jihar da bangaren gwamnatin ba.”

Kazalika, mambobin majalisar sun nuna damuwarsu bisa yadda aka samu koma baya wajen tafiyar da harkokin aikin hajji na gaza gudanar da tsare-tsaren da suka dace a hajjin bana.

Sun kuma nuna damuwarsu yadda ba a kula da su ba wajen rabon kujerun zuwa Makkah duk kuwa da cewa kakakin majalisar jihar shi ne mataimakin shugaban kwamitin tsare-tsaren na aikin hajjin.

Da yake maida martani kan wannan matakin, babban mai bai wa gwamna shawara kan harkokin majalisa, Sani Mohammed Burra, ya ce matsalolin da aka samu kan aikin hajji a bana ba jihar Bauchi ce kadai abun ya shafa ba, ya ce kasa ne baki daya sakamakon karancin adadin kujeru da aka ware wa jihar.

Dangane da rikicin da ya kunno kai a majalisar kuwa, ya ce rikicin cikin gida ne kuma za a shawo kansa nan kusa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas
Labarai

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas

October 2, 2025
Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara
Siyasa

Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara

September 28, 2025
Tinubu Zai Gana Da Manyan Ƴan Kasuwa, Zai Ƙaddamar Da Muhimman Aiyuka A Legas
Siyasa

Tinubu Zai Gana Da Manyan Ƴan Kasuwa, Zai Ƙaddamar Da Muhimman Aiyuka A Legas

September 27, 2025
Next Post
An Gurfanar Da Masu Gadi Kan Zargin Satar ‘Cornflakes’ Din Miliyan 2.1

Za A Jefe Mutum Uku Da Dutse Har Su Mutu Har Lahira Kan Laifin Yin Luwadi A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version