• English
  • Business News
Thursday, October 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kaduna: Muna Neman Afuwar Kisan Masu Maulidi – Hafsan Sojin Kasa

by Sadiq
2 years ago
Kaduna

Hafsan hafsoshin sojin kasa, Janar Taoreed Lagbaja ya mika sakon neman afuwa daga al’ummar Jihar Kaduna, sakamakon harin bam din da sojoji suka kai wanda ya yi sanadiyar rasa rayukan sama da mutane 85.

Yayin da yake jawabi cikin alhini lokacin da ya kai ziyara kauyen Tudun Biri da ke Karamar Hukumar Igabi, Janar Lagbaja ya bayyana bakin cikinsa da lamarin.

  • Kotu Ta Yanke Wa Sojan Da Ya Kashe Sheikh Bagoni Aisami Hukuncin Kisa
  • Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Halartar Taron Sauyin Yanayi A Dubai

Kakakin rundunar Janar Onyema Nwachukwu, ya ce hafsan hafsoshin ya bayyana cewar a ‘yan makonnin da suka gabata, ‘yan ta’adda sun kutsa kai a wannan yankin, abin da ya sa sojoji suka kaddamar da hare-hare, kuma sakamakon haka ne na’urarsu ta gano taron dandazon mutane a wurin Maulidin da aka kai musu hari cikin kuskure.

Lagbaja ya ce abin da ya sa ya ziyarci kauyen da kansa shi ne ya jajanta wa al’ummar yankin kan faruwar lamarin.

Hafsan ya ce ya ba da umarnin gudanar da cikakken bincike kan lamarin domin gano inda aka samu kuskure, domin taimaka musu wajen inganta ayyukansu nan gaba.

LABARAI MASU NASABA

Afuwar Tinubu Ga Fursunoni: Saura Ƙasa Da Shekaru 6 Maryam Sanda Ta Shaƙi Iskar ‘Yanci

Ba Matakan Tinubu Ne Suka Karyar Da Farashin Kayan Abinci Ba – ADC

A nasa jawabi, Hakimin Rigasa, Aminu Idris ya ce duk da zafin kisan da suke ji, sun gamsu da yadda rundunar sojin ta nuna damuwa da kuma amsa kuskuren da jami’anta suka yi dangane da kai harin, yayin da ya bukaci kai dauki ga iyalan wadanda abun ya shafa.

Hakimin, ya yi karin hasken cewar cikin wadanda harin ya rutsa da su har da Kiristocin da ke zaune a garin.

Daga bisani Janar Lagbaja ya jagoranci tawagarsa zuwa asibitin Barau Dikko domin duba wadanda suka jikkata.

Tuni kungiyoyi da daidaikun mutane suka shiga nuna alhininsu kan harin bam din da ya yi sanadin mutuwar masu taron Mauludin.

Sai dai lamarin ya dauki zafi a kafafen sada zumunta, inda mutane ke ganin wannan lamari a matsayin babban kuskure kuma dole ne a dauki mataki.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Afuwar Tinubu Ga Fursunoni: Saura Ƙasa Da Shekaru 6 Maryam Sanda Ta Shaƙi Iskar ‘Yanci
Manyan Labarai

Afuwar Tinubu Ga Fursunoni: Saura Ƙasa Da Shekaru 6 Maryam Sanda Ta Shaƙi Iskar ‘Yanci

October 29, 2025
ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa
Manyan Labarai

Ba Matakan Tinubu Ne Suka Karyar Da Farashin Kayan Abinci Ba – ADC

October 29, 2025
‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa
Manyan Labarai

‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

October 29, 2025
Next Post
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano

‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

October 29, 2025
Asuu

Gwamnatin Tarayya Ta Saki Naira Biliyan 2.3 Ga ASUU

October 29, 2025
Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki

Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki

October 29, 2025
Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

October 29, 2025
An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest

An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest

October 29, 2025
majalisar kasa

Majalisar Wakilai Ta Amince Da Bukatar Amso Bashin Dala Biliyan 2.34 A Kasuwar Jari Ta Duniya

October 29, 2025
An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin

An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin

October 29, 2025
Kotu Ta Umarci Ƙwace Dala 49,700 Daga Tsohon Jami’in INEC

Kotu Ta Umarci Ƙwace Dala 49,700 Daga Tsohon Jami’in INEC

October 29, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kara Kyautata Tsarin Kare Muradun Al’umma A Bangaren Shari’a

Yadda Kasar Sin Ke Kara Kyautata Tsarin Kare Muradun Al’umma A Bangaren Shari’a

October 29, 2025
COAS Shaibu Ya Sha Alwashin Murƙushe ‘Yan Ta’addar Lakurawa 

COAS Shaibu Ya Sha Alwashin Murƙushe ‘Yan Ta’addar Lakurawa 

October 29, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.