• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kaduna: Muna Neman Afuwar Kisan Masu Maulidi – Hafsan Sojin Kasa

by Sadiq
2 years ago
Kaduna

Hafsan hafsoshin sojin kasa, Janar Taoreed Lagbaja ya mika sakon neman afuwa daga al’ummar Jihar Kaduna, sakamakon harin bam din da sojoji suka kai wanda ya yi sanadiyar rasa rayukan sama da mutane 85.

Yayin da yake jawabi cikin alhini lokacin da ya kai ziyara kauyen Tudun Biri da ke Karamar Hukumar Igabi, Janar Lagbaja ya bayyana bakin cikinsa da lamarin.

  • Kotu Ta Yanke Wa Sojan Da Ya Kashe Sheikh Bagoni Aisami Hukuncin Kisa
  • Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Halartar Taron Sauyin Yanayi A Dubai

Kakakin rundunar Janar Onyema Nwachukwu, ya ce hafsan hafsoshin ya bayyana cewar a ‘yan makonnin da suka gabata, ‘yan ta’adda sun kutsa kai a wannan yankin, abin da ya sa sojoji suka kaddamar da hare-hare, kuma sakamakon haka ne na’urarsu ta gano taron dandazon mutane a wurin Maulidin da aka kai musu hari cikin kuskure.

Lagbaja ya ce abin da ya sa ya ziyarci kauyen da kansa shi ne ya jajanta wa al’ummar yankin kan faruwar lamarin.

Hafsan ya ce ya ba da umarnin gudanar da cikakken bincike kan lamarin domin gano inda aka samu kuskure, domin taimaka musu wajen inganta ayyukansu nan gaba.

LABARAI MASU NASABA

Majalisa Ta Ɗage Tantance Ministan Tinubu Saboda Rashin Rahoton Tsaro

Majalisar Kano Na Tattauna Batun Fara Amfani Da Harshen Hausa A Wurin Koyarwa A Makarantu 

A nasa jawabi, Hakimin Rigasa, Aminu Idris ya ce duk da zafin kisan da suke ji, sun gamsu da yadda rundunar sojin ta nuna damuwa da kuma amsa kuskuren da jami’anta suka yi dangane da kai harin, yayin da ya bukaci kai dauki ga iyalan wadanda abun ya shafa.

Hakimin, ya yi karin hasken cewar cikin wadanda harin ya rutsa da su har da Kiristocin da ke zaune a garin.

Daga bisani Janar Lagbaja ya jagoranci tawagarsa zuwa asibitin Barau Dikko domin duba wadanda suka jikkata.

Tuni kungiyoyi da daidaikun mutane suka shiga nuna alhininsu kan harin bam din da ya yi sanadin mutuwar masu taron Mauludin.

Sai dai lamarin ya dauki zafi a kafafen sada zumunta, inda mutane ke ganin wannan lamari a matsayin babban kuskure kuma dole ne a dauki mataki.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Majalisa Ta Ɗage Tantance Ministan Tinubu Saboda Rashin Rahoton Tsaro

November 6, 2025
Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure
Manyan Labarai

Majalisar Kano Na Tattauna Batun Fara Amfani Da Harshen Hausa A Wurin Koyarwa A Makarantu 

November 5, 2025
An Nemi Kasashen ECOWAS Su Samar Da Kariya Ga Yankunan Hakar Ma’adanai
Manyan Labarai

ECOWAS Ta Ƙaryata Iƙirarin Trump Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Next Post
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano

‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano

LABARAI MASU NASABA

Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata

Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata

November 6, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Majalisa Ta Ɗage Tantance Ministan Tinubu Saboda Rashin Rahoton Tsaro

November 6, 2025
Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

November 5, 2025
Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

November 5, 2025
Majalisar Dattawa

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

November 5, 2025
Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

November 5, 2025
Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025
Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

November 5, 2025
Gwamna Yusuf

Malam Triump: Ƙungiyoyin Ɗariƙun Sufaye Sun Maka Gwamnan Kano A Kotu

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.