• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kafa Majalisar Zartarwa: Kallo Ya Koma Kan Tinubu

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya, Manyan Labarai
0
Tinubu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Masu sharhi kan harkokin siyasa na ciki da wajen Nijeriya idanunsu sun karkata kan majalisar ministocin da Shugaba Bola Ahmed Tinubu zai kafa.

An dai ayyana Shugaba Tinubu a matsayin shugaban Nijeriya ne bayan ya lashe zaben da aka gudanar a watan Fabrairu wanda a halin yanzu ake kalubalantarsa kotun sauraron kararrakin zaben shugaban kasa da dan takarar jam’iyyar PDP, tsohon mataimakin Shugaban kasa Atiku Abubakar kuma dan takarar jam’iyyar LP, Mista Peter Obi.

An ci gaba da ce-ce-ku-ce kan shugabancin Tinubu kan yadda ‘yan Nijeriya ke fatan ganin wa’adin mulkinsa ya kai ga ci gaban al’ummar kasar bayan da ya cimma burinsa na rayuwa na shugaban kasar Nijeriya.

Tuni dai Shugaba Tinubu ya dauki kwararan matakai dangane da maye gurbin shugabannin hukumomin tsaro da dakatarwar da ya yi wa gwamnan babban bankin kasa, Godwin Emefiele da kuma na shugaban hukumar EFCC, Abdulrasheed Bawa, amma har yanzu ‘yan Nijeriya da dama na cikin kokwanton kan abubuwan da suke tsammani ga Shugaba Tinubu.

A wurin bikin rantsuwa na ranar 29 ga watan Mayun 2023, Shugaba Tinubu ya bayyana cewa shi mai cin gajiyar goyon baya ne da kuma fatan mai kyau ga al’ummar Nijeriya, inda ya yi alkawarin ba zai ci amanar miliyoyin ‘yan Nijeriya ba.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

A wata hira da jakadar kasar Ingila a Nijeriya, Richard Montgomery, ya bayyana cewa Ingila na jiran Shugaba Tinubu ya kafa majalisar ministocinsa domin daukar matakan da suka dace wajen karfafa dangantakar tattalin arziki da Nijeriya.

Montgomery ya bayyana cewa gwamnatin Burtaniya ta gano wasu bukatu shida wadanda kasashen biyu za su iya karfafa hadin gwiwa da kuma gina sababbin wuraren da za a ci moriyar juna.

Jakadar ya ce Birtaniya ta fi sha’awar kara alakar kasashen biyu kamar yadda Tinubu ya bayyana a baya-bayan nan game da shawarwarin tattalin arziki.

“Muna da dadaddiyar alaka mai cike da tarihi kuma muna da ginshiki mai karfi da za mu gina, sannan ina da kwarin gwiwa game da alkiblar Nijeriya a cikin shekaru masu zuwa.

“Muna fatan inganta dangantakarmu ta fuskar tattalin arziki, musamman game da matakin farko da sabuwar gwamnati ta yanke ya nuna cewa za ta dauki manyan matakai kan tattalin arzikin da nake ganin za su ba mu damar bunkasa harkokin kasuwanci da zuba jari.

“Kuma ina ganin akwai fannoni da dama da gwamnatin Burtaniya za ta iya inganta harkokin diflomasiyya bisa alakarmu da Nijeriya. Amma ko shakka babu, muna jiran nadin sabbin ministoci domin mu sami damar tattaunawa ta diflomasiyya da ta dace don shimfida dangantaka,” in ji Montgomery.
A bangare guda kuma, kungiyar habaka tattalin arzikin Arewa (AEC) ta bukaci Shugaban kasa Tinubu kar ya ba da fifiko wajen nada mukaman ministoci.

Shugaban kungiyar, Ibrahim Yahaya Dandakata shi ya yi wannan kiran a wata tattaunawa da manema labarai a Abuja.
Ibrahim ya kara da cewa shugaban kasa na iya tabbatar da cewa an dora wa mutane nagartattun mutane alhakkin yi wa kasa hidima ta hanyar sanya cancantar a sahun gaba wajen yanke shawarar wadanda za a bai wa mukamin ministoci.

“Nijeriya tana fama da matsalolin tattalin arziki, zamantakewa da siyasa, wanda hakan ya haifar da matsalolin da suka shafi kasar baki daya, kamar yawan rashin aikin yi, hauhawar farashin kayayyaki da ba a taba ganin irinsa ba, da rashin hadin kan ‘yan kasa lamarin da ya haifar da rashin tsaro a wasu sassan kasar nan.

“Nada mutanen da suka cancanta da suka dace suke da hazaka da kwazo da iya aiki wani muhimmin mataki ne na samun ingantaccen jagoranci da shugabanci. Nijeriya ta samu kanta a wani mawuyacin hali kuma dole ne shugabanni su kasance suna da wadannan siffofi a maimakon a mayar da hankali kan siyasa da son zuciya.
“An zabi shugaban ne bisa karfin aikinsa a matsayinsa na dan siyasa kuma shahararren dan kasuwa. An dai shaide shi da rikon gaskiya da amana a wajen kula da dukiyar al’umma.

“Muna kira gare shi da ya ci gaba da kiyaye wannan abin da ya gada tare da fito da kyakkyawan tsari na gwamnatinsa da kasa baki daya. Kamar yadda aka yi la’akari da nade-naden mukamai da suka hada da na ministoci da sauran mukamai, muna karfafa wa shugaban kasa gwiwa da ya yi la’akari da kwarewa da cancanta fiye da komai,” in ji Ibrahim.

Ita ma kungiyar masana’antu ta Nijeriya (MAN), ta kuma shawarci Shugaba Tinubu da ya nada ministan wutar lantarki mai nagarta wanda ba ya cin hanci da rashawa ke da kwarewa sosai a bangaren wutar lantarki.

Kungiyar ta bayyana hakan ne a wata sanarwa mai dauke da sa hannun Darakta Janar na MAN, Mista Segun Ajayi Kadir, inda ta ce nasarar da dokar samar da wutar lantarki ta shekarar 2023 da shugaban kasa ya sanya wa hannu za ta ta’allaka ne kan aiwatar da shi yadda ya kamata da kuma nada kwararre a fannin fasaha.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Bikin Babbar Sallah: Shugabanni Sun Jaddada Bukatar Kaunar Juna Da Sadaukarwa A Tsakanin ‘Yan Nijeriya

Next Post

Yadda Babbar Sallar Bana Ta Zo Wa ‘Yan Nijeriya

Related

NNPP
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

10 hours ago
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Manyan Labarai

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

12 hours ago
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis
Manyan Labarai

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

18 hours ago
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

19 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
Manyan Labarai

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

22 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

1 day ago
Next Post
Zan Iya Yi Wa Mamaci Layya?

Yadda Babbar Sallar Bana Ta Zo Wa ‘Yan Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

September 18, 2025
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

September 18, 2025
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.