ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kafa Majalisar Zartarwa: Kallo Ya Koma Kan Tinubu

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Tinubu

Masu sharhi kan harkokin siyasa na ciki da wajen Nijeriya idanunsu sun karkata kan majalisar ministocin da Shugaba Bola Ahmed Tinubu zai kafa.

An dai ayyana Shugaba Tinubu a matsayin shugaban Nijeriya ne bayan ya lashe zaben da aka gudanar a watan Fabrairu wanda a halin yanzu ake kalubalantarsa kotun sauraron kararrakin zaben shugaban kasa da dan takarar jam’iyyar PDP, tsohon mataimakin Shugaban kasa Atiku Abubakar kuma dan takarar jam’iyyar LP, Mista Peter Obi.

An ci gaba da ce-ce-ku-ce kan shugabancin Tinubu kan yadda ‘yan Nijeriya ke fatan ganin wa’adin mulkinsa ya kai ga ci gaban al’ummar kasar bayan da ya cimma burinsa na rayuwa na shugaban kasar Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Tuni dai Shugaba Tinubu ya dauki kwararan matakai dangane da maye gurbin shugabannin hukumomin tsaro da dakatarwar da ya yi wa gwamnan babban bankin kasa, Godwin Emefiele da kuma na shugaban hukumar EFCC, Abdulrasheed Bawa, amma har yanzu ‘yan Nijeriya da dama na cikin kokwanton kan abubuwan da suke tsammani ga Shugaba Tinubu.

A wurin bikin rantsuwa na ranar 29 ga watan Mayun 2023, Shugaba Tinubu ya bayyana cewa shi mai cin gajiyar goyon baya ne da kuma fatan mai kyau ga al’ummar Nijeriya, inda ya yi alkawarin ba zai ci amanar miliyoyin ‘yan Nijeriya ba.

LABARAI MASU NASABA

Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai

Sowore Ya Yi Kira Ga Zanga-Zangar Kasa Kan Tinubu Ranar Litinin

A wata hira da jakadar kasar Ingila a Nijeriya, Richard Montgomery, ya bayyana cewa Ingila na jiran Shugaba Tinubu ya kafa majalisar ministocinsa domin daukar matakan da suka dace wajen karfafa dangantakar tattalin arziki da Nijeriya.

Montgomery ya bayyana cewa gwamnatin Burtaniya ta gano wasu bukatu shida wadanda kasashen biyu za su iya karfafa hadin gwiwa da kuma gina sababbin wuraren da za a ci moriyar juna.

Jakadar ya ce Birtaniya ta fi sha’awar kara alakar kasashen biyu kamar yadda Tinubu ya bayyana a baya-bayan nan game da shawarwarin tattalin arziki.

“Muna da dadaddiyar alaka mai cike da tarihi kuma muna da ginshiki mai karfi da za mu gina, sannan ina da kwarin gwiwa game da alkiblar Nijeriya a cikin shekaru masu zuwa.

“Muna fatan inganta dangantakarmu ta fuskar tattalin arziki, musamman game da matakin farko da sabuwar gwamnati ta yanke ya nuna cewa za ta dauki manyan matakai kan tattalin arzikin da nake ganin za su ba mu damar bunkasa harkokin kasuwanci da zuba jari.

“Kuma ina ganin akwai fannoni da dama da gwamnatin Burtaniya za ta iya inganta harkokin diflomasiyya bisa alakarmu da Nijeriya. Amma ko shakka babu, muna jiran nadin sabbin ministoci domin mu sami damar tattaunawa ta diflomasiyya da ta dace don shimfida dangantaka,” in ji Montgomery.
A bangare guda kuma, kungiyar habaka tattalin arzikin Arewa (AEC) ta bukaci Shugaban kasa Tinubu kar ya ba da fifiko wajen nada mukaman ministoci.

Shugaban kungiyar, Ibrahim Yahaya Dandakata shi ya yi wannan kiran a wata tattaunawa da manema labarai a Abuja.
Ibrahim ya kara da cewa shugaban kasa na iya tabbatar da cewa an dora wa mutane nagartattun mutane alhakkin yi wa kasa hidima ta hanyar sanya cancantar a sahun gaba wajen yanke shawarar wadanda za a bai wa mukamin ministoci.

“Nijeriya tana fama da matsalolin tattalin arziki, zamantakewa da siyasa, wanda hakan ya haifar da matsalolin da suka shafi kasar baki daya, kamar yawan rashin aikin yi, hauhawar farashin kayayyaki da ba a taba ganin irinsa ba, da rashin hadin kan ‘yan kasa lamarin da ya haifar da rashin tsaro a wasu sassan kasar nan.

“Nada mutanen da suka cancanta da suka dace suke da hazaka da kwazo da iya aiki wani muhimmin mataki ne na samun ingantaccen jagoranci da shugabanci. Nijeriya ta samu kanta a wani mawuyacin hali kuma dole ne shugabanni su kasance suna da wadannan siffofi a maimakon a mayar da hankali kan siyasa da son zuciya.
“An zabi shugaban ne bisa karfin aikinsa a matsayinsa na dan siyasa kuma shahararren dan kasuwa. An dai shaide shi da rikon gaskiya da amana a wajen kula da dukiyar al’umma.

“Muna kira gare shi da ya ci gaba da kiyaye wannan abin da ya gada tare da fito da kyakkyawan tsari na gwamnatinsa da kasa baki daya. Kamar yadda aka yi la’akari da nade-naden mukamai da suka hada da na ministoci da sauran mukamai, muna karfafa wa shugaban kasa gwiwa da ya yi la’akari da kwarewa da cancanta fiye da komai,” in ji Ibrahim.

Ita ma kungiyar masana’antu ta Nijeriya (MAN), ta kuma shawarci Shugaba Tinubu da ya nada ministan wutar lantarki mai nagarta wanda ba ya cin hanci da rashawa ke da kwarewa sosai a bangaren wutar lantarki.

Kungiyar ta bayyana hakan ne a wata sanarwa mai dauke da sa hannun Darakta Janar na MAN, Mista Segun Ajayi Kadir, inda ta ce nasarar da dokar samar da wutar lantarki ta shekarar 2023 da shugaban kasa ya sanya wa hannu za ta ta’allaka ne kan aiwatar da shi yadda ya kamata da kuma nada kwararre a fannin fasaha.

Tinubu
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Hukuncin Kotu Na Barazana Ga Zaben 2027 —INEC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana

MASU ALAKA

Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai
Manyan Labarai

Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai

June 14, 2026
Sowore Ya Yi Kira Ga Zanga-Zangar Kasa Kan Tinubu Ranar Litinin
Manyan Labarai

Sowore Ya Yi Kira Ga Zanga-Zangar Kasa Kan Tinubu Ranar Litinin

June 14, 2026
Ƴansanda Sun Kunce Bam Ɗin Da ƴan Bindiga Suka Dasa A Zamfara
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kunce Bam Ɗin Da ƴan Bindiga Suka Dasa A Zamfara

June 14, 2026
Next Post
Zan Iya Yi Wa Mamaci Layya?

Yadda Babbar Sallar Bana Ta Zo Wa ‘Yan Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Farashin Mai Ya Fadi Rigis Bayan Amurka Da Iran Sun Sasanta Kan Mashigar Hormuz

Farashin Mai Ya Fadi Rigis Bayan Amurka Da Iran Sun Sasanta Kan Mashigar Hormuz

June 15, 2026
An Daure Ɗan Gidan Gimbiyar Masarautar Norway Shekara 4 Kan Laifin Fyaɗe

An Daure Ɗan Gidan Gimbiyar Masarautar Norway Shekara 4 Kan Laifin Fyaɗe

June 15, 2026
An Yi Wa Mata 600 Gwajin Cutar Sankarar Mama, An Yi Wa 50 Tiyata A Katsina

An Yi Wa Mata 600 Gwajin Cutar Sankarar Mama, An Yi Wa 50 Tiyata A Katsina

June 15, 2026
Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga Uku Yayin Zazzafar Musayar Wuta

Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga Uku Yayin Zazzafar Musayar Wuta

June 15, 2026
Jamus Ta Sake Yi Wa Abokiyar Karawarta Ruwan Ƙwallaye 7 A Gasar Kofin Duniya

Jamus Ta Sake Yi Wa Abokiyar Karawarta Ruwan Ƙwallaye 7 A Gasar Kofin Duniya

June 14, 2026
Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai

Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai

June 14, 2026
Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin

Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin

June 14, 2026
Atiku Ya Soki Shirin Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Bangaren Wutar Lantarki

Atiku Ya Soki Shirin Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Bangaren Wutar Lantarki

June 14, 2026
An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

June 14, 2026
Ododo Ya Kai Ziyara Sansanin Horar Dakarun Tsaro Daji A Kogi

Ododo Ya Kai Ziyara Sansanin Horar Dakarun Tsaro Daji A Kogi

June 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.