• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kafar Sadarwa Ta Karrama Fintiri, Bindow, Boss Mustapha Da Wasu 17 A Adamawa

by Muh'd Shafi'u Saleh
2 years ago
in Labarai
0
Kafar Sadarwa Ta Karrama Fintiri, Bindow, Boss Mustapha Da Wasu 17 A Adamawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kafar sadarwa ta TGnews, ta karrama gwamnan Jihar Adamawa Ahmadu Umaru Fintiri, tsohon gwamnan jihar Umaru Jibrilla Bindow, da wasu mutum 18, ranar Asabar.

Kafar ta kuma karrama tsohon sakataren gwamnatin tarayya (SGF), Boss Mustapha, da Admiral Jamila Sadiq Malafa (mai ritaya), da dan majalisar wakilai mai wakiltar kananan hukumomin Song/Fufore a majalisar wakilai ta kasa Honorabul Aliyu Wakili Boya.

  • Gobara Ta Lalata Shaguna 10 A Adamawa
  • Isra’ila Na Kara Iza Wutar Rikici A Sassan Gabas Ta Tsakiya -Lebanon

Haka kuma kafar ta karrama mataimakin shugaban jami’ar tarayya da ke Kashere Jihar Gombe, Farfesa Umar Pate, Reberan Dakta Panti Filibus, LCCN. Arch Bishop, Sarkin Mubi Alhaji Abubakar Isa Ahmadu, sarkin Ganye Gangwari Ganye, Alhaji Adamu Sanda, Hama Bachama Homun Ismaila Daniel Shaga da Kwandi Nunguriya, Mai Martaba Kuruhaye Dishon Dansanda.

Sauran mutanen da kafar ta karrama su ne shugaban bangaren labarai na kafar sadarwar talabijin na TVC, Stella Din-Peters, Mal Hamisu Idris Medugu, Barista Shafari Shadrach Kanya, tsohon dan majalisar dokokin jihar Honarabul Hassan Mamman Barguma, Ardo Usman da Madam Celina Yakubu.

Da yake jawabi lokacin karbar lambar yabon, Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri, ya gode wa kafar sadarwar yada labarai ta TGNews, bisa yadda ya amince da kokarin gwamnatinsa na ganin an samar da shugabanci na gari ga jama’a.

Labarai Masu Nasaba

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

Gwamnan wanda ya samu wakilcin mataimakiyarsa Farfesa Kaletapwa Farauta, ya yi alkawarin ci gaba da samar da ribar dimokuradiyya ga ’yan jihar, tare da gode wa wadanda su ka shirya taron bisa karramawar da aka masa.

Da shi ma ke jawabi a bikin mataimakin shugaban jami’ar fasaha ta gwamnatin tarayya dake Kashere, Farfesa Umar Pate, ya ce fasahar sadarwa ta kawo sauyi ba kawai a fannin aikin jarida ba, har ma a rayuwar dan adam baki daya.

Farfesa Pate ya yaba wa kamfanin dillancin labarai na TG game da shirya taron kuma ya bukaci ‘yan jarida da su rungumi gagarumin sauyin da fasahar sadarwa ta kawo, tare da baiwa jama’a bayanai da rahotanni na gaskiya.

A jawabinsa na maraba, Babban Edita/Mawallafin TG News, Tom Garba, ya yaba wa wadanda su ka samu kyautar da kuma wadanda su ka dauki lokaci na halartan taron, tare da nuna godiyarsa ga bikin karramawar da ya bayyana da “mai dimbin tarihi”

Haka kuma kafar TGNews, ta kaddamar da mujalla ta farko ta TGNews Magazine, da za ta rika fita wata-wata domin ci gaba da hidimta wa al’umma.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Hadin Garin Dilka Don Kawata Fata

Next Post

Majalisar Gudanarwar Sin Ta Yi Kira Da A Kara Bunkasa Tsarin Kula Da Tsoffi

Related

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas
Labarai

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

18 minutes ago
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa
Labarai

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

2 hours ago
Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP
Manyan Labarai

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

5 hours ago
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru
Manyan Labarai

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

16 hours ago
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

22 hours ago
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?
Labarai

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

23 hours ago
Next Post
Majalisar Gudanarwar Sin Ta Yi Kira Da A Kara Bunkasa Tsarin Kula Da Tsoffi

Majalisar Gudanarwar Sin Ta Yi Kira Da A Kara Bunkasa Tsarin Kula Da Tsoffi

LABARAI MASU NASABA

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

August 24, 2025
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

August 24, 2025
Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

August 24, 2025
Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

August 24, 2025
Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

August 24, 2025
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

August 24, 2025
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.