• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kakakin Ofishin Jakadancin Sin Dake Amurka Ya Soki Lamirin Ganawar Tsai Ing-wen Da Kakakin Majalissar Wakilan Amurka

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kakakin Ofishin Jakadancin Sin Dake Amurka Ya Soki Lamirin Ganawar Tsai Ing-wen Da Kakakin Majalissar Wakilan Amurka

NEW YORK, UNITED STATES - 2023/03/31: Supporters of unified China gather to protest against the President of Taiwan Tsai Ing-wen as she about to leave Lotte New York Palace Hotel. The President of Taiwan will continue to visit Washington, DC, Los Angeles and South American countries later on. (Photo by Lev Radin/Pacific Press/LightRocket via Getty Images)

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kakakin ofishin jakadancin Sin a Amurka, ya soki lamirin damar da Amurka ta baiwa jagorar yankin Taiwan, na bi ta cikin kasar yayin da take bulaguro, inda har ta samu zarafin ganawa da kakakin majalissar wakilan kasar Kevin McCarthy.

Kakakin ofishin jakadancin na Sin, wanda ya yi tsokaci kan batun a ranar Laraba, ya ce shigar Tsai Ing-wen cikin Amurka, tare da ganawa da Kevin McCarthy matakin watsi ne da kashedin da kasar Sin ta sha yi kan hakan.

  • Likitocin Kasar Sin Sun Yi Jinyar Marasa Lafiya Miliyan 290 Karkashin Shirin Tallafi Da Ta Aiwatar A Ketare

Jami’in ya ce Amurka ta keta hurumin manufar nan ta kasar Sin daya tak a duniya, da sanarwoyin hadin gwiwa 3 da sassan biyu suka amincewa. Har ila yau Amurka ta yi watsi da alkawarin da ta yi don gane da batun Taiwan, ta kuma aike da mummunan sako ga masu rajin samun ‘yancin yankin na Taiwan.

Sakamakon hakan, kasar Sin ta soki matakin da kakkausar murya, tana kuma matukar adawa da shi, kana za ta dau matakin da ya dace da wannan keta ka’ida da Amurka ta yi.

Har ila yau, jami’in ya kara da cewa, ba wani sashe da zai iya dakatar da manufar dinkewar dukkanin sassan kasar Sin. Kuma tarihi zai shafe masu neman goyon bayan Amurka game da burin su na “Samun ‘yancin kan yankin Taiwan”. Bugu da kari, masu amfani da yankin Taiwan da nufin sarrafa akalar kasar Sin za su gane cewa “Kan su suka hakawa ramin mugunta”.

Labarai Masu Nasaba

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

A Juma’ar nan ne ofishin lura da harkokin yankin Taiwan na kwamitin kolin JKS, ya sanar da kakaba takunkumi kan dan-gani-kashenin burin “Cin gashin kan Taiwan” mai suna Bi-khim Hsiao. Kaza lika ofishin ya bayyana hukunci kan wasu kungiyoyin yankin, da suka hada da “Prospect Foundation”, da “Council of Asian Liberals and Democrats”, bisa zargin su da yayata manufar “Neman ‘yancin Taiwan”. (Saminu Alhassan)

 

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Daure Minista A Uganda Saboda Satar Kwanon Rufi

Next Post

Gwamnatin Kaduna Ta Musanta Rahoton Sace Mutane A Hanyar Abuja-Kaduna

Related

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

6 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

6 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

8 hours ago
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

11 hours ago
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

13 hours ago
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

14 hours ago
Next Post
Gwamnatin Kaduna Ta Musanta Rahoton Sace Mutane A Hanyar Abuja-Kaduna

Gwamnatin Kaduna Ta Musanta Rahoton Sace Mutane A Hanyar Abuja-Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.