• English
  • Business News
Wednesday, November 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kamata Ya Yi Kasashe Masu Ci Gaba Sun Cika Alkawarin Da Suka Yi Na Samar Da Kudaden Taimakawa Kasashe Masu Tasowa Wajen Tinkarar Sauyin Yanayi

by CGTN Hausa
2 years ago
Sauyin Yanayi

LABARAI MASU NASABA

CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

Taron COP28 da ke gudana a birnin Dubai ya cimma matsaya daya wajen fara aiki da asusun biyan asarar sauyin yanayi, ko kuma“Loss and Damage” Fund a Turance, don taimakawa kasashe masu tasowa wajen tinkarar matsalar sauyin yanayi. Hadaddiyar daular Larabawa, da Jamus sun yi alkawarin samar da kudi har dalar miliyan 100 kowaccen su, yayin da adadin da Birtaniya za ta bayar ya kai kimanin dalar miliyan 50.Amma Amurka wadda ta kan bayyana kanta a matsayin kasa dake matukar sauke nauyin dake wuyanta wajen tinkarar wannan matsala, ta yi alkawarin samar da dala miliyan 17.5 ne kacal, duk da cewa yawan hayaki mai dumama yanayi da take fitarwa gaba daya ya fi na ko wace kasa a duniya.

Amurka da dai sauran kasashen yamma, sun kwashe shekaru fiye da dari suna raya masana’antu, wanda hakan ya samar musu da arziki, da bunkasuwar tattalin arziki mai wadata, amma a sa’i daya, sun yi amfani da makamashi da albarkatu mafiya yawa, tare da fitar da abubuwa masu gurbata muhalli da yawa, hakan ya sa dole ne wadannan kasashe su dauki alhakin bullar matsalar sauyin yanayi.

  • Sin Ta Dauki Alhakinta Wajen Tinkarar Sauyin Yanayi
  • Kasar Sin Za Ta Soke Harajin Kwastam Da Ta Buga Kan Kaso 98% Na Hajojin Wasu Kasashen Afirka 6

Rahotanin da MDD ta bayar na nuna cewa, tun lokacin da aka fara Juyin juya halin masana’antu, kashi 58% na karuwar zafin yanayi da ayyukan bil Adama ke haifarwa, ya faru ne sakamakon abubuwan dumama yanayi da aka fitar kafin shekarar 1990, kuma daga shekarar 1850 zuwa 2019, yawan iskar Co2 da nahiyar arewacin Amurka da Turai suka fitar ya kai kashi 23%, da 16% na dukkan duniya. Amma abin takaici ne, kasashe maso tasowa ne suke fi fama da illar da sauyin yanayi ke haifarwa. Shugaban taron COP28 Dr. Sultan Al Jaber ya ce, wasu kasashe marasa karfi, musamman ma kasashe kananan tsibirai, da kasashe mafiya rauni, suna fama da illar sauyin yanayi mai tsanani.

Kamata ya yi, kasashe masu ci gaba sun sauke nauyin dake wuyansu na samar da kudade, don taimakawa wadannan kasashe wajen tinkarar matsalar sauyin yanayi, don samar da daidaito da adalci a fannin yanayi,. Bai kamata kasashe masu tasowa su yi asara sakamakon bunkasuwa, da wadatar da kasashe masu wadata suka samu ba. (Mai zana da rubuta: MINA)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika
Daga Birnin Sin

CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika

November 5, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

November 4, 2025
‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba
Daga Birnin Sin

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

November 4, 2025
Next Post
An Kaddamar Da Cibiyar Buga Muhimman Takardu Ta AU Da Sin Ta Ba Da Taimakon Ginawa

An Kaddamar Da Cibiyar Buga Muhimman Takardu Ta AU Da Sin Ta Ba Da Taimakon Ginawa

LABARAI MASU NASABA

Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

November 5, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

Majalisar Dattawa Ta Amince da Naira Tiriliyan 1.1 Don Biyan Bashin ‘Yan Kwangila – Akpabio

November 5, 2025
An Nemi Kasashen ECOWAS Su Samar Da Kariya Ga Yankunan Hakar Ma’adanai

ECOWAS Ta Ƙaryata Iƙirarin Trump Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

November 5, 2025
Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Sanata Barau Ya Tsaya Takarar Shugaban Majalisar Dattawa

Ba Na Jin Tsoron Trump – Martanin Sanata Barau Ga Akpabio

November 5, 2025
CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika

CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika

November 5, 2025
Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

November 4, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

November 4, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Sace A Kwara

November 4, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.