• English
  • Business News
Friday, May 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kamata Ya Yi Sin Da Amurka Su Mai Da Hankalinsu A Kan Ci Gaban Duniya

by Sulaiman and CGTN Hausa
6 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Kamata Ya Yi Sin Da Amurka Su Mai Da Hankalinsu A Kan Ci Gaban Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da takwaransa na kasar Amurka Joe Biden a birnin Lima a ranar 16 ga wata, kimanin shekara daya ke nan tun bayan ganawarsu a birnin San Fransisco. Ganawarsu a wannan karo kuma ta kasance ta uku a tsakaninsu a cikin shekaru hudu da suka gabata. 

 

A kimanin tsawon sa’o’i biyu, shugabannin kasashen biyu sun yi musayar ra’ayoyi a kan huldar da ke tsakanin kasashensu da ma batutuwan kasa da kasa, inda shugaban kasar Sin Xi Jinping ya takaita wasu abubuwa guda bakwai da ya kamata a yi la’akari da su bisa ga bunkasar huldar kasashen biyu cikin shekarun hudu da suka gabata, kuma ya fara ne da ambaton batun samun kyakkyawar fahimtar juna, inda ya yi nuni da cewa, husuma a tsakanin kasashe masu tasowa da manya ba aba ce da za a ce dole sai an yi ta ba a tarihi. Bai kamata a bari sabon yakin cacar-baka ta barke ba kuma babu mai yin nasara a ciki. Neman dakile ci gaban kasar Sin rashin wayewa ne kuma ba abin yarda ba ne kuma hakan zai fadi kasa warwas.

  • Kwalara Ta Yi Ajalin Mutane 25 A Sakkwato
  • Shugabannin Sin Da Faransa Sun Rubuta Bayanai Domin Wani Bikin Baje Koli Na Musamman

Yadda kasashen biyu ke fahimtar juna, wato su abokan gaba ne ko aminai ne, ya zama tambaya da dole su amsa lokacin da suke hulda da juna. Don haka, a yayin tuntubar juna a tsakanin manyan jami’an kasashen biyu cikin ‘yan shekarun baya, sun sha tattauna batun.

 

Labarai Masu Nasaba

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci

A cikin ‘yan shekarun baya, kasar Sin ta bunkasa da sauri tare da cimma nasarorin a-zo-a-gani, sai dai hakan ya sa kasar Amurka matukar damuwa. Don kiyaye matsayinta na fin karfi a duniya, ta dauki matakai iri- iri na dakile kasar Sin, ciki har da katse huldar tattalin arziki da ita da yayata kalaman wai “Sin barazana ce”, matakan da kuma suka lalata huldar kasashen biyu. Sai dai abin da Amurka ba ta gane ba shi ne, kowace kasa da kuma kowace kabila tana da ‘yancin bunkasa kanta, kuma manufar kasar Sin ta bunkasa kanta ita ce don al’ummarta su ji dadin rayuwarsu, a maimakon a ce tana neman maye gurbin wata. A sa’i daya kuma, ya kamata Amurka ta gane cewa, babu wanda zai iya hana al’ummar kasar Sin ‘yancinsu na tabbatar da ci gaba. Har ila yau, ya kamata Amurka ta gane cewa, zamanin kasar Amurka na nuna fin karfi ya kare, yadda kasashe masu tasowa ke bunkasa da sauri da ma kasancewar bangarori masu ci gaba da dama a duniya ya zama tabbas, don haka yin hadin gwiwar cin moriyar juna ya zama dole.

 

Tarihi ya sha shaida mana cewa, hadin gwiwar Sin da Amurka zai amfanawa kowacensu ne, a yayin da kuma dukkansu za su yi hasara idan sun yi fada. Musamman ma a yanayin da ake ciki yanzu, moriyar bai daya tsakanin kasashen biyu ta kara karuwa a maimakon raguwa. Ko ta fannonin tattalin arziki da noma da yaki da miyagun kwayoyi da aiwatar da dokoki da kiwon lafiya, ko kuma a gaban kalubale da baki dayan duniyarmu ke fuskanta irinsu sauyin yanayi da fasahar kwaikwayon tunanin dan Adam, har ma a lokacin da ake daidaita batutuwan da ke janyo hankalin kasa da kasa, duka ana bukatar Sin da Amurka su yi hadin gwiwa da juna. Don haka kamata ya yi Sin da Amurka su fadada hadin gwiwarsu.

 

A yayin ganawar, shugaba Xi Jinping ya kuma jaddada cewa, kasancewarsu kasashe manya, ya kamata Sin da Amurka su dauki nauyin da ke wuyansu, su yi la’akari da makomar dan Adam a ko da yaushe, furucin da ya nuna inda ya kamata huldar kasashen biyu ta dosa.

 

Hakika, a halin yanzu, duniyarmu na fama da tashin hankali da rikice-rikice, kuma dan Adan na fuskantar kalubalen da bai taba gani ba. Huldar da ke tsakanin Sin da Amurka na shafar al’ummominsu, har ma da makomar dan Adam baki daya. Don haka, daukacin kasashen duniya na fatan ganin kasashen biyu su kyautata huldarsu, haka kuma suna fatan ganin ci gaba cikin lumana da hadin gwiwar cin moriyar juna ya zama jigon zamanin da muke ciki. Kamata ya yi kasashen Sin da Amurka su dauki nauyin da ke bisa wuyansu, su yi la’akari da ci gaban duniya, su samar da tabbas ga duniyar da ke fama da rashin tabbas. (Lubabatu Lei)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kwalara Ta Yi Ajalin Mutane 25 A Sakkwato

Next Post

Xi Ya Yi Kiran Gina Duniya Mai Ci Gaba Ta Bai Daya Bisa Adalci A Taron G20

Related

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka
Ra'ayi Riga

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

1 day ago
Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci
Ra'ayi Riga

Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci

4 days ago
Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta
Ra'ayi Riga

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

6 days ago
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

1 week ago
Tattalin Arzikin Sin Tamkar Teku Ne Ba Karamin Tabki Ba
Ra'ayi Riga

Tattalin Arzikin Sin Tamkar Teku Ne Ba Karamin Tabki Ba

1 week ago
Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya
Ra'ayi Riga

Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya

2 weeks ago
Next Post
Xi Ya Yi Kiran Gina Duniya Mai Ci Gaba Ta Bai Daya Bisa Adalci A Taron G20

Xi Ya Yi Kiran Gina Duniya Mai Ci Gaba Ta Bai Daya Bisa Adalci A Taron G20

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana

Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana

May 15, 2025
Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

May 15, 2025
Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

May 15, 2025
Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci

Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci

May 15, 2025
Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

Majalisar Wakilai Za Ta Binciki Yadda Aka Samu Mummunan Sakamakon Jarabawar UTME 2025

May 15, 2025
Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

May 15, 2025
An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

May 15, 2025
HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42

HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42

May 15, 2025
Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

May 15, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.