• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kamata Ya Yi Sin Da Amurka Su Mai Da Hankalinsu A Kan Ci Gaban Duniya

by Sulaiman and CGTN Hausa
7 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Kamata Ya Yi Sin Da Amurka Su Mai Da Hankalinsu A Kan Ci Gaban Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da takwaransa na kasar Amurka Joe Biden a birnin Lima a ranar 16 ga wata, kimanin shekara daya ke nan tun bayan ganawarsu a birnin San Fransisco. Ganawarsu a wannan karo kuma ta kasance ta uku a tsakaninsu a cikin shekaru hudu da suka gabata. 

 

A kimanin tsawon sa’o’i biyu, shugabannin kasashen biyu sun yi musayar ra’ayoyi a kan huldar da ke tsakanin kasashensu da ma batutuwan kasa da kasa, inda shugaban kasar Sin Xi Jinping ya takaita wasu abubuwa guda bakwai da ya kamata a yi la’akari da su bisa ga bunkasar huldar kasashen biyu cikin shekarun hudu da suka gabata, kuma ya fara ne da ambaton batun samun kyakkyawar fahimtar juna, inda ya yi nuni da cewa, husuma a tsakanin kasashe masu tasowa da manya ba aba ce da za a ce dole sai an yi ta ba a tarihi. Bai kamata a bari sabon yakin cacar-baka ta barke ba kuma babu mai yin nasara a ciki. Neman dakile ci gaban kasar Sin rashin wayewa ne kuma ba abin yarda ba ne kuma hakan zai fadi kasa warwas.

  • Kwalara Ta Yi Ajalin Mutane 25 A Sakkwato
  • Shugabannin Sin Da Faransa Sun Rubuta Bayanai Domin Wani Bikin Baje Koli Na Musamman

Yadda kasashen biyu ke fahimtar juna, wato su abokan gaba ne ko aminai ne, ya zama tambaya da dole su amsa lokacin da suke hulda da juna. Don haka, a yayin tuntubar juna a tsakanin manyan jami’an kasashen biyu cikin ‘yan shekarun baya, sun sha tattauna batun.

 

Labarai Masu Nasaba

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore

A cikin ‘yan shekarun baya, kasar Sin ta bunkasa da sauri tare da cimma nasarorin a-zo-a-gani, sai dai hakan ya sa kasar Amurka matukar damuwa. Don kiyaye matsayinta na fin karfi a duniya, ta dauki matakai iri- iri na dakile kasar Sin, ciki har da katse huldar tattalin arziki da ita da yayata kalaman wai “Sin barazana ce”, matakan da kuma suka lalata huldar kasashen biyu. Sai dai abin da Amurka ba ta gane ba shi ne, kowace kasa da kuma kowace kabila tana da ‘yancin bunkasa kanta, kuma manufar kasar Sin ta bunkasa kanta ita ce don al’ummarta su ji dadin rayuwarsu, a maimakon a ce tana neman maye gurbin wata. A sa’i daya kuma, ya kamata Amurka ta gane cewa, babu wanda zai iya hana al’ummar kasar Sin ‘yancinsu na tabbatar da ci gaba. Har ila yau, ya kamata Amurka ta gane cewa, zamanin kasar Amurka na nuna fin karfi ya kare, yadda kasashe masu tasowa ke bunkasa da sauri da ma kasancewar bangarori masu ci gaba da dama a duniya ya zama tabbas, don haka yin hadin gwiwar cin moriyar juna ya zama dole.

 

Tarihi ya sha shaida mana cewa, hadin gwiwar Sin da Amurka zai amfanawa kowacensu ne, a yayin da kuma dukkansu za su yi hasara idan sun yi fada. Musamman ma a yanayin da ake ciki yanzu, moriyar bai daya tsakanin kasashen biyu ta kara karuwa a maimakon raguwa. Ko ta fannonin tattalin arziki da noma da yaki da miyagun kwayoyi da aiwatar da dokoki da kiwon lafiya, ko kuma a gaban kalubale da baki dayan duniyarmu ke fuskanta irinsu sauyin yanayi da fasahar kwaikwayon tunanin dan Adam, har ma a lokacin da ake daidaita batutuwan da ke janyo hankalin kasa da kasa, duka ana bukatar Sin da Amurka su yi hadin gwiwa da juna. Don haka kamata ya yi Sin da Amurka su fadada hadin gwiwarsu.

 

A yayin ganawar, shugaba Xi Jinping ya kuma jaddada cewa, kasancewarsu kasashe manya, ya kamata Sin da Amurka su dauki nauyin da ke wuyansu, su yi la’akari da makomar dan Adam a ko da yaushe, furucin da ya nuna inda ya kamata huldar kasashen biyu ta dosa.

 

Hakika, a halin yanzu, duniyarmu na fama da tashin hankali da rikice-rikice, kuma dan Adan na fuskantar kalubalen da bai taba gani ba. Huldar da ke tsakanin Sin da Amurka na shafar al’ummominsu, har ma da makomar dan Adam baki daya. Don haka, daukacin kasashen duniya na fatan ganin kasashen biyu su kyautata huldarsu, haka kuma suna fatan ganin ci gaba cikin lumana da hadin gwiwar cin moriyar juna ya zama jigon zamanin da muke ciki. Kamata ya yi kasashen Sin da Amurka su dauki nauyin da ke bisa wuyansu, su yi la’akari da ci gaban duniya, su samar da tabbas ga duniyar da ke fama da rashin tabbas. (Lubabatu Lei)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kwalara Ta Yi Ajalin Mutane 25 A Sakkwato

Next Post

Xi Ya Yi Kiran Gina Duniya Mai Ci Gaba Ta Bai Daya Bisa Adalci A Taron G20

Related

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

5 hours ago
Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore
Ra'ayi Riga

Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore

2 days ago
Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya
Ra'ayi Riga

Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya

5 days ago
Akwai Ma’ana Mai Zurfi A Bayan Da’a
Ra'ayi Riga

Akwai Ma’ana Mai Zurfi A Bayan Da’a

2 weeks ago
Ta Yaya Kasashe Masu Tasowa Za Su Iya Tinkarar Yakin Haraji Da Amurka Ta Tayar?
Ra'ayi Riga

Ta Yaya Kasashe Masu Tasowa Za Su Iya Tinkarar Yakin Haraji Da Amurka Ta Tayar?

2 weeks ago
Ingancin Tattalin Arzikin Sin Mai Bude Kofa Na Bayyana Sosai Duba Da Yawan Zuwan Baki Masu Sayayya
Ra'ayi Riga

Ingancin Tattalin Arzikin Sin Mai Bude Kofa Na Bayyana Sosai Duba Da Yawan Zuwan Baki Masu Sayayya

2 weeks ago
Next Post
Xi Ya Yi Kiran Gina Duniya Mai Ci Gaba Ta Bai Daya Bisa Adalci A Taron G20

Xi Ya Yi Kiran Gina Duniya Mai Ci Gaba Ta Bai Daya Bisa Adalci A Taron G20

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.