ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, November 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kamfanoni 530 Suka Nuna Bukatar Neman Aikin Gyaran Jiragen Kasan Nijeriya Na Naira Biliyan 11

by Bello Hamza
2 years ago
Nijeriya

A wata sanarwa da Hukumar Jiragen Kasan Nijeriya (NRC) ta fitar, ta bayyana cewa, kamfanoni fiye da 530 suka nuna aniyarsu na aikin gyare-gyare na kayyakin hukumar jiragen kasa na Nijeriya a wannan shekarar 2024.

An dai ware za a kashe naira Biliyan 11 ne a wanann shekarar don aiwatar da ayyukan da suka shafi bunkasa harkokin jiragen kasa a Nijeriya da suka hada da samar bda hanyar jirgin da taragu da sauran kayyakin aikin da ake bukata don bunkasa harkokin sufurin jiragen kasan Nijeriya a wannan shekarar kamar yadda aka sanya a cikin kasafin kudin 2024.

  • Kotu Ta Ci Tarar ‘Yansanda Naira Miliyan 300 Kan Kisan ‘Yan Shi’a A Zariya
  • Xi Ya Aike Da Sakon Taya Murna Ga Taron OIC Karo Na 15 

An bude zama tantace kamfanonin ne a shalkwatar Hukumar Jiragen Kasan Nijeriya da ke Legas, inda shugaban Hukumar, Engr Fidet Okhiria, ya jagoranci zaman, ya kuma nuna muhimmancin ba kowa hakkin nuna bajintarsa na aiwatar da aikin da ake bukata.

ADVERTISEMENT

Ya kuma jaddada cewa, za a gudanar da tantancewar cikin gaskiya da amana, ta yadda kowa zai gamsu da sakamakon da za a fitar.

Darakta mai kula da ma’aikata a hukumar, Dr. Monsurat Omotayo, ta wakilci shugaban hukumar ta kuma bayyana makasudin taron kamar haka “Wannan wani shiri ne da muke gudanarwa a duk shedkara. Hukumar mu ta tallata ayyukan da ake bukatar kamfanonin da suke da kwarewar yin aikin su mika bukatarsu tun a watan da ya wuce, a kan haka muka taru a yau don tantance wadanda suka kware na yin aikin da ya kamata a shekarar 2024.”

LABARAI MASU NASABA

Masana’antu Masu Zaman Kansu A Arewa Sun Yi Maraba Da Harajin Kashi 15 Na Shigo Da Man Fetur

Abin Da Ya Sa NPA Ta Yi Hadaka Da ‘Snake Island Port’ -Dakta Dantsoho

Ta kuma jaddada cewa, “Wannan bikin zai taimaka mana gudanar da tantancewar a cikin adalci ta yadda kowa da kowa zai gamsu da abin da aka yi, hakan kuma ya yi daidai da dokar bayar da ayyukan kwangila a Nijeriya.”

Ganin yadda kamfanoni da dama kuma daga bangarori da dama suka nuna bukatarsu, ya zama dole mu yi aiki cikin natsuwa don fitar da kamfanin da ke da kwarewar da ake bukata don aiwatar da ayyukan da ke gabamu” in ji ta.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Masana’antu Masu Zaman Kansu A Arewa Sun Yi Maraba Da Harajin Kashi 15 Na Shigo Da Man Fetur
Tattalin Arziki

Masana’antu Masu Zaman Kansu A Arewa Sun Yi Maraba Da Harajin Kashi 15 Na Shigo Da Man Fetur

November 14, 2025
Abin Da Ya Sa NPA Ta Yi Hadaka Da ‘Snake Island Port’ -Dakta Dantsoho
Tattalin Arziki

Abin Da Ya Sa NPA Ta Yi Hadaka Da ‘Snake Island Port’ -Dakta Dantsoho

November 14, 2025
Shugaban NPA Ya Bukaci A Yi Hadaka Domin Cin Gajiyar Albarkatun Fannin Sufurin Afirka
Tattalin Arziki

Shugaban NPA Ya Bukaci A Yi Hadaka Domin Cin Gajiyar Albarkatun Fannin Sufurin Afirka

November 14, 2025
Next Post
Gwamnatin Tinubu Ta Ba ‘Yan Jarida Cikakken ‘Yanci – Minista

Gwamnatin Tinubu Ta Ba 'Yan Jarida Cikakken 'Yanci - Minista

LABARAI MASU NASABA

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

November 16, 2025
Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

November 16, 2025
Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

November 16, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

November 16, 2025
Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

November 16, 2025
An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

November 16, 2025
Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

November 16, 2025
Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
DSS

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.