ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Ci Tarar ‘Yansanda Naira Miliyan 300 Kan Kisan ‘Yan Shi’a A Zariya

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
'yansanda

Wata Babbar Kotun Tarayya da ke zamanta a Kaduna ta umurci hukumomin ‘yansanda da su biya zunzurutun kudi Naira miliyan 300 ga iyayen ‘yan Shi’a uku da ake zargin jami’anta sun kashe a lokacin da suke gudanar da muzahara a shekarar 2022 a Zariya.

Mai shari’a Hawa Buhari, a cikin hukuncin da ta yanke, ta ce “masu neman hakkokinsu kamar yadda doka ta yi umarnin a ba su a cikin sashe na 33, 38, 39, 40, 42 da 46 na kundin tsarin mulkin 1999 (da aka gyara); Umarni na 2, Dokoki na 1, 2, 3, 4, 11 da 12 na Dokokin Kare Hakki da nuna Mahimmanci (Tasirin Tilastawa) da tsarin Dokokin 2009; ya yi nuni da cewa; Ana aiwatar da doka ta 4, 8, 10, 11 da 12 na Yarjejeniya Ta Afirka ta 2004 game da ‘yancin dan’Adam da jama’a.”
Alkalin kotun ta ce adadin Naira miliyan 100 da ya zama dole a biya ga kowane iyayen mamacin, inda za a biya jimillar Naira miliyan 300, a matsayin diyya, sannan kuma gamayyar diyyar, za a rika samar da riba ta kashi 10 cikin 100 a duk shekara har sai an biya kudaden.

  • Wani Dansanda Mai Rakiyar Jirgin Kasan Kaduna Zuwa Abuja Ya Rasu Acikin Jirgin
  • Kotu Ta Hana ‘Yansanda Kama Shugabannin Jam’iyyar APC Da Suka Dakatar Da Ganduje A Kano

Mai shari’a Buhari, a hukuncin da ta yanke a ranar 22 ga Afrilu, 2024, tare da kwafin na hukuncin da aka bai wa manema labarai ranar Lahadi a Abuja, ya karfafa kararraki guda uku da makusantan mamatan uku suka shigar.

ADVERTISEMENT

“Za a ba wa kowane iyayen mamaci Kudi Naira miliyan 100,000,000.00 a matsayin diyya da kuma jimillar diyyar za ta zama tare da ribar kashi 10 a duk shekara har sai an cika adadin.

“Wadanda aka yi kara za su nemi afuwar masu kara a bainar jama’a kowace rana saboda keta haddinsu da suka yi,” in ji ta.

LABARAI MASU NASABA

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

Za a iya tunawa cewa mutane uku ne da suka hada da; Magaji Yusuf, Muhammad Lawal da Aliyu Badamasi sun shigar da kara mai lamba: FHC/KH/KD/138/2022, FHC/KH/KD/140/2022 da FHC/KH/KD/146/2022 a gaban kotun.
Sun yi zargin cewa a ranar 8 ga Agusta, 2022, jami’an ‘yan sandan Nijeriya sun harbe Jafar Magaji, Aliyu Lawal da Muhsin Badamasi, a lokacin da suke gudanar da ibadarsu ta Muzaharar Ashura a Garin Zariya.

Sun kai karar Sufeto-Janar na ’yansanda (IGP), Mataimakin Sufeto-Janar na ’yansanda na shiyya ta 7, Kwamishinan ’Yansandan Jihar Kaduna, AC Surajo Fana (Kwamandan yankin Zariya), Ibrahim Zubairu (Jami’in ’Yansanda, Kasuwar Mata, Sabon Garin). Zaria Dibision), da Kasim Muhammad (DPO, Zaria City Dibision) a matsayin wadanda ake kara na 1 zuwa na 6.

Masu neman a gabatar da karar a ranar 26 ga Satumba, 2022 da kuma gabatarwa a ranar 26 ga Satumba, 2022, ta tawagar lauyoyinsu da suka hada da H.G Magashi, M.D Abubakar da Dokta Yusha’u Shaikh, da sauran mutum bakwai.

Sun nemi a bayyana cewa harbin da aka yi wa Jafar Magaji, Aliyu Lawal da Muhsin Badamasi a ranar da ake gudanar da muzaharar a matsayin abin da ya saba wa doka, kuma ya saba wa kundin tsarin mulkin kasa da kuma tauye hakkinsu na rayuwa kamar yadda sashe na 33 na kundin tsarin mulkin 1999 da sashe na 1999 ya tabbatar, da kuma Yarjejeniya 4 Ta Afirka Kan Hakkokin Dan’Adam da Jama’a Cap A9 LFN, 2004.

Don haka sun roki kotu da ta umarci wadanda ake kara tare da su biya su Naira miliyan 200 kowannensu saboda tauye hakkin ‘yan uwansu da suka rasu.

Haka kuma sun nemi oda, inda suka umurci wadanda ake kara da su rubuta takardar neman gafara ta hanyar bugawa a cikin jaridun kasar guda biyu da ke yawo a Arewacin Nijeriya.

Amma wadanda ake kara, a cikin kararsu ta farko mai kwanan wata da kuma gabatar da su a ranar 8 ga Nuwamba, 2022, sun nemi a ba da umarnin soke kararrakin ukun saboda rashin hukumci.

Bayan haka, sun kuma gabatar da takardar shaidar adawa da kara.

Sai dai mai shari’a Buhari ya amince da gabatar da lauyoyin wanda ya shigar da karar, kuma ya dauki hukumci kan lamarin.

'Yan Shi'a
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Kotu Da Ɗansanda

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

June 18, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Next Post
An Gabatar Da Rahoto Dangane Da Hadin Gwiwar Da Kasar Sin Da Kasashen Turai Suke Yi A Fannin Kare Muhalli

An Gabatar Da Rahoto Dangane Da Hadin Gwiwar Da Kasar Sin Da Kasashen Turai Suke Yi A Fannin Kare Muhalli

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.