ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Ci Tarar ‘Yansanda Naira Miliyan 300 Kan Kisan ‘Yan Shi’a A Zariya

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
'yansanda

Wata Babbar Kotun Tarayya da ke zamanta a Kaduna ta umurci hukumomin ‘yansanda da su biya zunzurutun kudi Naira miliyan 300 ga iyayen ‘yan Shi’a uku da ake zargin jami’anta sun kashe a lokacin da suke gudanar da muzahara a shekarar 2022 a Zariya.

Mai shari’a Hawa Buhari, a cikin hukuncin da ta yanke, ta ce “masu neman hakkokinsu kamar yadda doka ta yi umarnin a ba su a cikin sashe na 33, 38, 39, 40, 42 da 46 na kundin tsarin mulkin 1999 (da aka gyara); Umarni na 2, Dokoki na 1, 2, 3, 4, 11 da 12 na Dokokin Kare Hakki da nuna Mahimmanci (Tasirin Tilastawa) da tsarin Dokokin 2009; ya yi nuni da cewa; Ana aiwatar da doka ta 4, 8, 10, 11 da 12 na Yarjejeniya Ta Afirka ta 2004 game da ‘yancin dan’Adam da jama’a.”
Alkalin kotun ta ce adadin Naira miliyan 100 da ya zama dole a biya ga kowane iyayen mamacin, inda za a biya jimillar Naira miliyan 300, a matsayin diyya, sannan kuma gamayyar diyyar, za a rika samar da riba ta kashi 10 cikin 100 a duk shekara har sai an biya kudaden.

  • Wani Dansanda Mai Rakiyar Jirgin Kasan Kaduna Zuwa Abuja Ya Rasu Acikin Jirgin
  • Kotu Ta Hana ‘Yansanda Kama Shugabannin Jam’iyyar APC Da Suka Dakatar Da Ganduje A Kano

Mai shari’a Buhari, a hukuncin da ta yanke a ranar 22 ga Afrilu, 2024, tare da kwafin na hukuncin da aka bai wa manema labarai ranar Lahadi a Abuja, ya karfafa kararraki guda uku da makusantan mamatan uku suka shigar.

ADVERTISEMENT

“Za a ba wa kowane iyayen mamaci Kudi Naira miliyan 100,000,000.00 a matsayin diyya da kuma jimillar diyyar za ta zama tare da ribar kashi 10 a duk shekara har sai an cika adadin.

“Wadanda aka yi kara za su nemi afuwar masu kara a bainar jama’a kowace rana saboda keta haddinsu da suka yi,” in ji ta.

LABARAI MASU NASABA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

Za a iya tunawa cewa mutane uku ne da suka hada da; Magaji Yusuf, Muhammad Lawal da Aliyu Badamasi sun shigar da kara mai lamba: FHC/KH/KD/138/2022, FHC/KH/KD/140/2022 da FHC/KH/KD/146/2022 a gaban kotun.
Sun yi zargin cewa a ranar 8 ga Agusta, 2022, jami’an ‘yan sandan Nijeriya sun harbe Jafar Magaji, Aliyu Lawal da Muhsin Badamasi, a lokacin da suke gudanar da ibadarsu ta Muzaharar Ashura a Garin Zariya.

Sun kai karar Sufeto-Janar na ’yansanda (IGP), Mataimakin Sufeto-Janar na ’yansanda na shiyya ta 7, Kwamishinan ’Yansandan Jihar Kaduna, AC Surajo Fana (Kwamandan yankin Zariya), Ibrahim Zubairu (Jami’in ’Yansanda, Kasuwar Mata, Sabon Garin). Zaria Dibision), da Kasim Muhammad (DPO, Zaria City Dibision) a matsayin wadanda ake kara na 1 zuwa na 6.

Masu neman a gabatar da karar a ranar 26 ga Satumba, 2022 da kuma gabatarwa a ranar 26 ga Satumba, 2022, ta tawagar lauyoyinsu da suka hada da H.G Magashi, M.D Abubakar da Dokta Yusha’u Shaikh, da sauran mutum bakwai.

Sun nemi a bayyana cewa harbin da aka yi wa Jafar Magaji, Aliyu Lawal da Muhsin Badamasi a ranar da ake gudanar da muzaharar a matsayin abin da ya saba wa doka, kuma ya saba wa kundin tsarin mulkin kasa da kuma tauye hakkinsu na rayuwa kamar yadda sashe na 33 na kundin tsarin mulkin 1999 da sashe na 1999 ya tabbatar, da kuma Yarjejeniya 4 Ta Afirka Kan Hakkokin Dan’Adam da Jama’a Cap A9 LFN, 2004.

Don haka sun roki kotu da ta umarci wadanda ake kara tare da su biya su Naira miliyan 200 kowannensu saboda tauye hakkin ‘yan uwansu da suka rasu.

Haka kuma sun nemi oda, inda suka umurci wadanda ake kara da su rubuta takardar neman gafara ta hanyar bugawa a cikin jaridun kasar guda biyu da ke yawo a Arewacin Nijeriya.

Amma wadanda ake kara, a cikin kararsu ta farko mai kwanan wata da kuma gabatar da su a ranar 8 ga Nuwamba, 2022, sun nemi a ba da umarnin soke kararrakin ukun saboda rashin hukumci.

Bayan haka, sun kuma gabatar da takardar shaidar adawa da kara.

Sai dai mai shari’a Buhari ya amince da gabatar da lauyoyin wanda ya shigar da karar, kuma ya dauki hukumci kan lamarin.

'Yan Shi'a
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas

MASU ALAKA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota
Kotu Da Ɗansanda

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

July 18, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

July 18, 2026
Disu
Kotu Da Ɗansanda

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Next Post
An Gabatar Da Rahoto Dangane Da Hadin Gwiwar Da Kasar Sin Da Kasashen Turai Suke Yi A Fannin Kare Muhalli

An Gabatar Da Rahoto Dangane Da Hadin Gwiwar Da Kasar Sin Da Kasashen Turai Suke Yi A Fannin Kare Muhalli

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.