ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Ci Tarar ‘Yansanda Naira Miliyan 300 Kan Kisan ‘Yan Shi’a A Zariya

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
'yansanda

Wata Babbar Kotun Tarayya da ke zamanta a Kaduna ta umurci hukumomin ‘yansanda da su biya zunzurutun kudi Naira miliyan 300 ga iyayen ‘yan Shi’a uku da ake zargin jami’anta sun kashe a lokacin da suke gudanar da muzahara a shekarar 2022 a Zariya.

Mai shari’a Hawa Buhari, a cikin hukuncin da ta yanke, ta ce “masu neman hakkokinsu kamar yadda doka ta yi umarnin a ba su a cikin sashe na 33, 38, 39, 40, 42 da 46 na kundin tsarin mulkin 1999 (da aka gyara); Umarni na 2, Dokoki na 1, 2, 3, 4, 11 da 12 na Dokokin Kare Hakki da nuna Mahimmanci (Tasirin Tilastawa) da tsarin Dokokin 2009; ya yi nuni da cewa; Ana aiwatar da doka ta 4, 8, 10, 11 da 12 na Yarjejeniya Ta Afirka ta 2004 game da ‘yancin dan’Adam da jama’a.”
Alkalin kotun ta ce adadin Naira miliyan 100 da ya zama dole a biya ga kowane iyayen mamacin, inda za a biya jimillar Naira miliyan 300, a matsayin diyya, sannan kuma gamayyar diyyar, za a rika samar da riba ta kashi 10 cikin 100 a duk shekara har sai an biya kudaden.

  • Wani Dansanda Mai Rakiyar Jirgin Kasan Kaduna Zuwa Abuja Ya Rasu Acikin Jirgin
  • Kotu Ta Hana ‘Yansanda Kama Shugabannin Jam’iyyar APC Da Suka Dakatar Da Ganduje A Kano

Mai shari’a Buhari, a hukuncin da ta yanke a ranar 22 ga Afrilu, 2024, tare da kwafin na hukuncin da aka bai wa manema labarai ranar Lahadi a Abuja, ya karfafa kararraki guda uku da makusantan mamatan uku suka shigar.

ADVERTISEMENT

“Za a ba wa kowane iyayen mamaci Kudi Naira miliyan 100,000,000.00 a matsayin diyya da kuma jimillar diyyar za ta zama tare da ribar kashi 10 a duk shekara har sai an cika adadin.

“Wadanda aka yi kara za su nemi afuwar masu kara a bainar jama’a kowace rana saboda keta haddinsu da suka yi,” in ji ta.

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja

An Cafke Mutum 7 Kan Satar Waya Da Fasa Gidaje A Jihar Yobe

Za a iya tunawa cewa mutane uku ne da suka hada da; Magaji Yusuf, Muhammad Lawal da Aliyu Badamasi sun shigar da kara mai lamba: FHC/KH/KD/138/2022, FHC/KH/KD/140/2022 da FHC/KH/KD/146/2022 a gaban kotun.
Sun yi zargin cewa a ranar 8 ga Agusta, 2022, jami’an ‘yan sandan Nijeriya sun harbe Jafar Magaji, Aliyu Lawal da Muhsin Badamasi, a lokacin da suke gudanar da ibadarsu ta Muzaharar Ashura a Garin Zariya.

Sun kai karar Sufeto-Janar na ’yansanda (IGP), Mataimakin Sufeto-Janar na ’yansanda na shiyya ta 7, Kwamishinan ’Yansandan Jihar Kaduna, AC Surajo Fana (Kwamandan yankin Zariya), Ibrahim Zubairu (Jami’in ’Yansanda, Kasuwar Mata, Sabon Garin). Zaria Dibision), da Kasim Muhammad (DPO, Zaria City Dibision) a matsayin wadanda ake kara na 1 zuwa na 6.

Masu neman a gabatar da karar a ranar 26 ga Satumba, 2022 da kuma gabatarwa a ranar 26 ga Satumba, 2022, ta tawagar lauyoyinsu da suka hada da H.G Magashi, M.D Abubakar da Dokta Yusha’u Shaikh, da sauran mutum bakwai.

Sun nemi a bayyana cewa harbin da aka yi wa Jafar Magaji, Aliyu Lawal da Muhsin Badamasi a ranar da ake gudanar da muzaharar a matsayin abin da ya saba wa doka, kuma ya saba wa kundin tsarin mulkin kasa da kuma tauye hakkinsu na rayuwa kamar yadda sashe na 33 na kundin tsarin mulkin 1999 da sashe na 1999 ya tabbatar, da kuma Yarjejeniya 4 Ta Afirka Kan Hakkokin Dan’Adam da Jama’a Cap A9 LFN, 2004.

Don haka sun roki kotu da ta umarci wadanda ake kara tare da su biya su Naira miliyan 200 kowannensu saboda tauye hakkin ‘yan uwansu da suka rasu.

Haka kuma sun nemi oda, inda suka umurci wadanda ake kara da su rubuta takardar neman gafara ta hanyar bugawa a cikin jaridun kasar guda biyu da ke yawo a Arewacin Nijeriya.

Amma wadanda ake kara, a cikin kararsu ta farko mai kwanan wata da kuma gabatar da su a ranar 8 ga Nuwamba, 2022, sun nemi a ba da umarnin soke kararrakin ukun saboda rashin hukumci.

Bayan haka, sun kuma gabatar da takardar shaidar adawa da kara.

Sai dai mai shari’a Buhari ya amince da gabatar da lauyoyin wanda ya shigar da karar, kuma ya dauki hukumci kan lamarin.

'Yan Shi'a
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja
Kotu Da Ɗansanda

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja

May 2, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum 7 Kan Satar Waya Da Fasa Gidaje A Jihar Yobe

April 25, 2026
An Sake Samun Gawar Wani Dan Nijeriya A Gidansa Da Ke Burtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Sake Samun Gawar Wani Dan Nijeriya A Gidansa Da Ke Burtaniya

April 25, 2026
Next Post
An Gabatar Da Rahoto Dangane Da Hadin Gwiwar Da Kasar Sin Da Kasashen Turai Suke Yi A Fannin Kare Muhalli

An Gabatar Da Rahoto Dangane Da Hadin Gwiwar Da Kasar Sin Da Kasashen Turai Suke Yi A Fannin Kare Muhalli

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.