• English
  • Business News
Friday, August 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kamfanonin Nijeriya 54 Da Suka Ki Biyan Masu Hannun Jarinsu A Cikin Shekara 5

by Bello Hamza
1 year ago
in Tattalin Arziki
0
Kamfanonin Nijeriya 54 Da Suka Ki Biyan Masu Hannun Jarinsu A Cikin Shekara 5
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jaridar leadership ta gano cewa kamfanoni 54 suka kasa ko kuma suka ki biyan kudaden ribar da ake rarrabawa ga masu hannun jari a karshen shekara tun shekara 5 da suka wuce.

A duk karshen shekara kamfanoni kan raba wa masu hannun jari ribar da aka samu a cikin shekarar. Amma bayani ya nuna cewa, daga cikin kamfanoni 153 da suke da rajista a kasar nan 54 daga cikin su ba su biya irin wannan kudaden ba ga masu hannun jarinsu tun shekarar 2019, wanda hadakar kudaden ya zama jarin da kamfanion ke tafiyar da harkokinsa da su, wannan yana nuna cewa kashi 34 kenan na kamfanonin da ke Nijeriya suka ki biyan wannan kudaden ga masu zuba jarin su.

  • Ana Gudanar Da Horo Kan Gina “Koren Babbar Ganuwa” A Afirka A Beijing
  • Sin Na Goyon Bayan Yunkurin IAEA Na Tabbatar Da Tsaron Tashar Nukiliya Ta Zaporizhzhia

Masana sun bayyana cewa, rashin biyan riba ga masu zuba jari ba wai yana nufin kamfani baya samun riba ba ne ko kuma bai kamata a zuba jari a kamfanin ba ne amma ya dangantane da irin tsarin da kamfanin yake da shi na yadda zai rika rarraba ribar da aka samu a kasrshen shekara.

Wasu kamfanonin sun gwamnace su sake zuba jari da ribar da suka samu don fadada kamfani wasu kuma sun ci karo da asara ko kuma rashin samun riba saboda karyewar tattalin arziki kasa a kan haka suka dakatar da raba wa masu jari ribar da aka samu don ci gaba da wanzuwar kamfanin.

Kididdiga daga hukumar kula da kamfanonin Nijeriya ya nuna cewa, kamfanoni hudu sun bayar da riba ga masu zuba jari a shekara 5 da suka wuce, kamfanoni uku sun bayar a shekara 6 da suka wuce, kamfani 2 sun bayar da ribar a shekara 7 da suka wuce yayin da kamfani 2 suka biya irin wannan kudin shekara 7 da suka wuce; haka kuma wasu kamfanoni 2 sun biya ribar na karshe ne a shekara 8 da suka wuce, kamfani 2 kuma sun bayar da kudin riba ne shekara 11 da suka wuce.

Labarai Masu Nasaba

Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

Bayanin ya kuma nuna cewa, kamfani 3 sun biya kudaden ne na karshe shekara 13 da suka wuce yayin kamfani 6 suka biya a shekara 14 da suka gabata; wani kamfani ya biya kudin na karshe ne shekara 15 da 16 da suka gabata yayin wasu kamfanioni 3 suka biya a shekara 21 da suka gabata.

Haka kuma kamfanoni kamar ASeM board, Capital Oil sun bayar da ribar na karshe ne a shekarar 2001, ita kuwa kamfanin Rak Unity Petroleum a shekarar 2019 ta bayar da na karshe.

A karkashin kamfanonin harkar gona, kamfanonin FTN Cocoa Processors (ta bayar a shekarar 2010), John Holts (2005) SCOA Nigeria (2015), Arbico Plc, (1998).

Bayani ya kuma nuna yadda wasu kamfanonin suka bayar da ribar hannun jarinsu na karshe kamar haka DN Tyre & Rubber (2002), Champion Breweries (1986), Golden Guinea Breweries (1997), Multi-Tred Integrated Foods (2010), Union Dicon Salt (2002), da kuma Nigerian Enamelware (2016).

A bangaren harkokin bankuna kuma bincike ya nuna cewa sun biya kudaden hannun jari na karshe kamar haka, Unity Bank (2011) Guinea Insurance (2010), Mutual Benefits Assurance (2018), Niger Insurance, Prestige Assurance, Regency Assurance (2019), Sobereign Trust Insurance (2011), Staco Insurance (2008), Standard Alliance Insurance (2009), Unibersal Insurance, Beritas Kapital Assurance (2017), Coronation Insurance (2016).

A kan haka masana suka bayar da shawara cewa, kafin mai zuba jari ya antaya kudadensa a cikin kamfani ya kamata ya binciki tarihin kamfani na biyan masu hannun jari don kada ya yi zaben tumun dare.

Sun kuma lura da cewa, wasu kamfanonin da gangan suke kin raba ribar da aka samu ba wai don rashin kudi ba.

“Sai kaga kamfanoni na hankoron kara fadada harkokin su amma sun ki biyan riba ga masu hannun jari a kamfanin wanda haka yana karya gwiwar masu zuba jari na ciki da kasashen waje, iin ji wani masani da ya bukaci mu sakaya sunansa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Karin Kudin Wutar Lantarki Ya Jefa Harkokin Kasuwanci Cikin Garari

Next Post

Majalisar Kasa Ta Bayyana Dalilan Watsi Da Zarge-zargen Badakalar Naira Biliyan 178 A Kan Shugaban NPA

Related

Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA
Tattalin Arziki

Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

6 days ago
Dangote
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

2 weeks ago
Afrika Ta Zama Kasuwar Sayar Da Man Fetur Mara Inganci – Dangote
Tattalin Arziki

Afrika Ta Zama Kasuwar Sayar Da Man Fetur Mara Inganci – Dangote

2 weeks ago
NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma
Tattalin Arziki

NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma

3 weeks ago
NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta
Tattalin Arziki

NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta

3 weeks ago
Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu
Tattalin Arziki

Kungiyar MEMAN Ta Yi Maraba Da Shirin Dangote Na Rabar Da Man Fetur

4 weeks ago
Next Post
NPA Ta Gargadi Masu Jibge Kwantaina Ba Bisa Ka’ida Ba

Majalisar Kasa Ta Bayyana Dalilan Watsi Da Zarge-zargen Badakalar Naira Biliyan 178 A Kan Shugaban NPA

LABARAI MASU NASABA

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafi Jawabin Xi Jinping Game Da Kiyaye Muhallin Halittu

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafi Jawabin Xi Jinping Game Da Kiyaye Muhallin Halittu

July 31, 2025
Dangote Ya Bada Shawarar Samar Da Gidaje Masu Rahusa Da ‘Yan Nijeriya Za Su Iya Mallaka

Dangote Ya Bada Shawarar Samar Da Gidaje Masu Rahusa Da ‘Yan Nijeriya Za Su Iya Mallaka

July 31, 2025
NIN-SIM: Masu Hulda Da Kamfanonin Sadarwa Sun Koka Kan Katse Layinsu Daga Tsarin Kira

Kamfanonin Sadarwa Za Su Ci Gaba Da Rajistar Sabon SIM – NIMC

July 31, 2025
Matsayar Bai Daya Da Sin Da Amurka Suka Cimma Ta Fuskar Haraji Na Da Babbar Ma’ana

Matsayar Bai Daya Da Sin Da Amurka Suka Cimma Ta Fuskar Haraji Na Da Babbar Ma’ana

July 31, 2025
Mutane 44 Suka Mutu Bayan Mamakon Ruwa Da Aka Tafka A Beijing

Mutane 44 Suka Mutu Bayan Mamakon Ruwa Da Aka Tafka A Beijing

July 31, 2025
Yadda Yajin Aikin Ma’aikatan Jinya Ya Bar Baya Da Kura A Asibitocin Jihar Filato

Yadda Yajin Aikin Ma’aikatan Jinya Ya Bar Baya Da Kura A Asibitocin Jihar Filato

July 31, 2025
Zargin Da Wasu ’Yan Siyasar Amurka Ke Yi Wa Sin Na Fitar Da Hajoji Fiye Da Kima Ya Sabawa Hujjoji Na Hakika

Zargin Da Wasu ’Yan Siyasar Amurka Ke Yi Wa Sin Na Fitar Da Hajoji Fiye Da Kima Ya Sabawa Hujjoji Na Hakika

July 31, 2025
Gwamnatin Borno Ta Nada Kwamitin Aiwatar Da Mafi Karancin Albashi

Gwamna Zulum Ya Sauke Kwamishinoni Biyu Tare Da Maye Gurbinsu Da Wasu

July 31, 2025
Uganda Ta Jinjinawa Gudummawar Sin Ga Manufofin Wanzar Da Zaman Lafiya A Yankin Kahon Afirka

Uganda Ta Jinjinawa Gudummawar Sin Ga Manufofin Wanzar Da Zaman Lafiya A Yankin Kahon Afirka

July 31, 2025
Yanzu-yanzu: Sanata Dino Melaye Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

Yanzu-yanzu: Sanata Dino Melaye Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

July 31, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.