• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kara Mu’amala Tsakanin Mabambantan Al’ummomin Duniya Zai Kawar Da Sabani Da Rashin Fahimta

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Kara Mu’amala Tsakanin Mabambantan Al’ummomin Duniya Zai Kawar Da Sabani Da Rashin Fahimta
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A duniyar yanzu, babbar matsalar dake haifar da tashe-tashen hankula da rashin girmama juna ita ce, rashin fahimta da mu’amala tsakanin mabambantan al’ummomi. Matukar ana son yi wa tufkar hanci tare da samun duniya mai fahimta da zaman lafiya, sai an inganta mu’amala tsakanin mabambantan al’ummomin duniya.

A karshen makon da ya gabata ne, yayin zaman babban zauren MDD na 78, daukacin mambobin majalisar suka amince da kudurin da Sin ta gabatar na ware wata rana, domin inganta mu’amala da tattaunawa tsakanin mabambantan al’ummomin duniya, inda aka ayyana ranar 10 ga watan Yunin kowacce shekara ta kasance wannan rana.

  • Xi Ya Jaddada Muhimmancin Inganta Tsarin Kamfanoni Na Zamani Mai Halayyar Musamman Ta Sin
  • Xi Jinping: Sin Na Fatan Kafa Tsare-Tsaren Hadin Kai Biyar Tsakaninta Da Kasashen Larabawa

Hakika hangen nesa irin na kasar Sin ya cancanci yabo. Har kullum cikin bangarorin da take mayar da hankali kansu a hadin gwiwarta da kasa da kasa shi ne, inganta mu’amala da musaya tsakanin al’ummomi, da zummar kyautata fahimta da koyi da juna. Misali, a baya-bayan nan, an yi taron musaya tsakanin matasan Sin da Afrika a birnin Beijing, kuma wannan wani taro ne da kasar Sin kan dauki nauyinsa a kowacce shekara. Ba wannan kadai ba, a ko da yaushe kasar Sin na samar da tallafin karatu ga matasan kasashen duniya daban-daban, domin su zo kasar su yi karatu da mu’amala da takwarorinsu da kuma kara fahimtar al’adu da yanayin kasar, da zummar kawar da sabani da bahaguwar fahimta. Idan zan bada misali da kai na, tabbas ra’ayi da tunanina game da kasar Sin sun sauya bayan zuwana kasar tare da mu’amala da jama’arta, ke nan, lallai mu’amala da cudanya na kara wayar da kan jama’a da samar da fahimtar juna.

Har ila yau a gainina, bambancin al’ada ko addini ko launin fata dake akwai tsakanin al’ummomin duniya, abun alfahari ne ga dan adam, sannan wata dama ce ta karin ilimi. Kowacce al’ada ko kabila na da nata sigogi na musamman, kuma ta hanyar mu’amala da musaya ne kadai, mabambantan al’ummomi za su iya fahimta da hakuri da girmama juna da kuma samun jituwa. Lamarin da zai kai ga samun zaman lafiya da girmama juna, wanda shi ne burin kasar Sin a ko da yaushe.

Dukkan bil adama matsayi daya gare su, babu wanda ya fi wani. Gane darajar dan adam da hakuri da girmama juna ba zai samu ba, har sai an fahimci juna an kuma ma’amalantu. Fatan ita ce, wannan rana da aka ayyana ta taka rawar gani wajen kawo zaman lafiya da dunkulewar al’ummun duniya cikin kwanciyar hankali da lumana. (Faeza Mustapha)

Labarai Masu Nasaba

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ci gaban duniyaDuniya labariKoriya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ranar Dimokuraɗiyyar:  Ƴan Nijeriya Fushi Suke, PDP Ga Tinubu 

Next Post

Rusau: ‘Yan Kasuwar Kano 5,000 Za Su Rasa Shagunansu Bayan Shafe Shekaru 18 A Kasuwa

Related

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa
Daga Birnin Sin

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

11 hours ago
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

12 hours ago
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

13 hours ago
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci
Daga Birnin Sin

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

14 hours ago
Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu
Daga Birnin Sin

Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

15 hours ago
Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo
Daga Birnin Sin

Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo

1 day ago
Next Post
Rusau: ‘Yan Kasuwar Kano 5,000 Za Su Rasa Shagunansu Bayan Shafe Shekaru 18 A Kasuwa

Rusau: ‘Yan Kasuwar Kano 5,000 Za Su Rasa Shagunansu Bayan Shafe Shekaru 18 A Kasuwa

LABARAI MASU NASABA

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.