• English
  • Business News
Saturday, September 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karin Farashin Man Fetur: Ko Tinubu Zai Saurari Muryar Talaka?

by Bello Hamza and Rabi'u Ali Indabawa
11 months ago
in Manyan Labarai
0
Karin Farashin Man Fetur: Ko Tinubu Zai Saurari Muryar Talaka?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Karin farashin man fetur na baya-bayan nan ya yi matukar ta da hankalin ‘yan kasuwar mai da kamfanin mai na kasa tare da kungiyar masu sayar da man fetur mai zaman kanta inda (IPMAN) din da gana da kamfanin man fetur na kasa (NNPCL) kan sabon gyaran farashin man fetur.

Shugaban Kungiyar IPMAN, Abubakar Maigandi, ya bukaci hukumar ta NNPC da ta sayar da man fetur ga mambobinta bisa ga farashin da matatar man Dangote ta ba ta.

  • MOFA: Ministan Harkokin Wajen Birtaniya Zai Ziyarci Kasar Sin
  • Mambobin Kungiyar SCO Sun Bayyana Adawa Da Matakan Kariyar Cinikayya

Yayin da yake magana a jiya a gidan Talabijin na Channels, Maigandi, ya kuma bukaci a mayar musu da kudaden da ‘yan kasuwar man ke bin su, wadanda ya ce hukumar ta NNPCPL ta rike tun watanni uku da suka gabata. Hakan ya zo ne sa’o’i 24 bayan da kamfanin NNPC ya yi karin farashin man fetur.

Kamfanin mai na kasa ya daga farashin man zuwa N1,030 daga N897/litta a Abuja, sannan ya karu zuwa Naira 998 daga Naira 868 a Legas.

Sauran wuraren dai an samu hauhawar farashin kaya, inda miliyoyin ‘yan Nijeriya ke korafin cewa an jefa su cikin mawuyacin hali.

Labarai Masu Nasaba

NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai

’Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 2 Da Wasu 156 Kan Aikata Laifuka A Jigawa

Shugaban na IPMAN ya jaddada matsalar kudi ce da aka rikewa ‘yan kasuwar man fetur, inda ya bukaci hukumar NNPC da ta dauki matakin gaggawa wajen ganin an daidaita lamarin.

Babban kalubalen da muke fuskanta a yanzu shi ne, muna da bashin da ake bin kamfanin na NNPC da kamfanin ya tara kaya ta hanyar matatar Dangote a farashi mai rahusa. Yanzu haka, kudinmu yana tare da su (NNPCL) kusan watanni uku”, in ji shi

Shima da yake zantawa da Sashen Hausa na BBC, shugaban kungiyar IPMAN a yankin Arewa, Alhaji Salisu Tantan, ya ce kamfanin NNPC ya sayi kayan a kan Naira 898 kan kowace lita daga matatar Dangote amma yana sayarwa da sama da Naira 1,000.

“Mun yi matukar kaduwa da cewa (NNPCL) sun sayar mana da shi fiye da yadda muke tsammani,” in ji shi.

Ya ce a halin yanzu ba abu ne mai wuya su sayar wa jama’a kayan a kan farashi mai rahusa ba, la’akari da cewa dole ne su dauki nauyin sufuri.

Da aka tambaye shi dalilin da ya sa suka kasa dauke kayan kai tsaye daga matatar Dangote, jigon na IPMAN ya ce suna yin iya kokarinsu don cimma wannan matsayar.

“Akwai tsari na musamman tsakanin NNPC da Dangote; suna ba shi danyen mai; ya kuma biya su a Naira. Zai yi mana wuya mu shiga cikin irin wannan tsari cikin sauki,” in ji shi.

 

Farashin zai sauko – cewar sashen kasuwanci na NNPCL

Sai dai wani jami’in kamfanin NNPC a daren jiya ya kare matakin da suka dauka, inda ya ce karin da aka yi a baya-bayan nan ya shafi kasuwar man fetur ta duniya da kuma canjin Naira da Dala.

Malam Lawan Sade, wanda shi ne Manajan Darakta na Kamfanin Trading na NNPCL, ya shaida wa BBC cewa farashin man fetur ya yi yawa sosai, musamman idan matatun mai da gwamnati ke gyarawa suka shigo cikin tsarin.

Sade ya ce farashin man fetur ya yi dai-dai da bukatun duniya, kuma a matsayinsa na kamfani mai zaman kansa, kamfanin na NNPC yana mayar da martani ga sauye-sauyen bukatu da wadata.

“Muna kira ga ‘yan Najeriya da su yi hakuri da mu. Za a daidai lamarin domin samar da fa’ida cikin lokaci,” in ji shi.

 

IPMAN na fatan samun saukin farashi bayan da aka fara tattaunawa da Dangote

An ruwaito cewa ‘yan kasuwar masu zaman kansu sun fara tattaunawa da hukumar gudanarwa ta Dangote biyo bayan tsoma bakin hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) da hukumar kula da harkokin man fetur ta kasa (NMDPRA).

A karshe dai kungiyar IPMAN ta bayyana wa kamfanin man fetur na Nijeriya (NNPCL) cewa farashin man da take samu daga kamfanin mai na kasa ya haura Naira 898 akan kowacce lita yadda suke saya daga Dangote.

A cewar shugabanta kungiyar na kasa, Abubakar Maigandi, kamfanin na NNPC ya rike da kimanin Naira biliyan 15 na ‘yan kasuwa masu zaman kansu tsawon watanni uku da suka gabata.Sai dai wata majiya daga IPMAN da ta zanta da wakilinmu a jiya ta ce hukumar ta NNPC ta amince da bai wa IPMAN damar sayan man kai tsaye daga Dangote.

Hakan ya biyo bayan matakin da kamfanin mai na kasa ya dauka na barin matsakaita masu daukar mai wajen rabon mai daga matatar mai girman 650,000.

Gwamnatin tarayya ta bayyana a karshen makon da ya gabata cewa, a yanzu ‘yan kasuwar man sun samu ‘yancin yin shawarwarin sayen man fetur kai tsaye daga matatar Dangote ba tare da neman izinin hukumar ta NPL ba.

Ministan Kudi kuma Ministan Tattalin Arziki, Wale Edun wanda ya bayyana hakan ya ce, “A ci gaban da aka samu, ‘yan kasuwar man fetur sun samu damar sayan kayan kai tsaye daga matatun mai na cikin gida ba tare da aikin shiga tsakanin na NNPC ba. Ana karfafawa gwiwar ’yan kasuwa da su fara sayayya kai tsaye daga matatun mai bisa sharudan kasuwanci da aka yi sulhu tsakanin juna, wanda zai habaka gasa da habaka ingantaccen kasuwaci.

A makon da ya gabata ne kamfanin NNPC, wanda shi ne na daya a kasuwa a kasar, ya daidaita farashin famfo, inda ya kara daga Naira 855 zuwa Naira 998 kan kowace lita a Legas da kuma sama da Naira 1000 a wasu jihohi.

 

SERAP ta bukaci Tinubu da ya janye sabon farashin mai

Kungiyar Kare Hakkokin Tattalin Arziki (SERAP) ta yi kira ga Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu da ya janye sabon farashin man fetur na baya-bayan nan har zuwa lokacin da za a yanke hukuncin karar da ta shigar gaban babbar kotun tarayya da ke Legas wadda take kalubalantar ikon kamfanin man fetur na Nijeriya (NNPCL) kan kara farashin man.

SERAP ta nanata cewa idan aka bar wannan karin na baya-bayan nan ya tsaya, to zai zama abin izgili ga shari’ar da ke gaban kotu, wanda hakan zai haifar da hatsarin da zai kawo cikas ga shari’ar ko kuma a nuna son zuciya, kamar yadda ake yi.

Kungiyar ta yi wannan ikirari ne a wata budaddiyar wasika mai kwanan watan 12 ga watan Oktoba 2024 dake dauke da sa hannun mataimakin daraktan SERAP Kolawole Oluwadare, cewa daya daga cikin muhimman ka’idojin da doka ta tanada ita ce ta shafi kowa da kowa, ciki har da shugabanni da hukumomin gwamnati.

SERAP ta ci gaba da cewa, barin babbar kotun tarayya ta saurari shari’ar da kuma yanke hukunci zai yi daidai da ka’ida da tsarin mulkin Nijeriya na (da aka yi masa gyara a 1999), kan rantsuwar da kuka yi da kuma alkawurran da kuka sha na tabbatar da doka.

A watan da ya gabata ne dai kungiyar farar hula ta maka gwamnati da kamfanin na NNPC gaban kotu domin kalubalantar halaccin karin farashin man fetur da kuma rashin binciken zargin cin hanci da rashawa a hukumar ta NNPC.

 

Ra’ayoyin jama’a game da sabon farashin mai

An ci gaba da mayar da martani dangane da karin farashin man fetur da kamfanin man fetur na Nijeriya (NNPC) ya yi.

Karin farashin man fetur ya tayar da hankulan jama’a a baya-bayan nan, inda yanzu ya kai Naira 1,030 kan kowace lita a Abuja da kuma Naira 998 a Legas. Wannan shi ne karo na biyu da aka kara kudin mai cikin wata guda, wanda ke nuna hauhawar kashi 430 cikin 100 tun daga watan Mayun 2023.

Shugaban kungiyar ‘yan kasuwa, masana’antu, ma’adinai da noma ta Nijeriya (NACCIMA), Dele Kelbin Oye, ya nuna damuwarsa kan karin farashin man.

Da yake mayar da martani kan hakan, Oye ya ce: “Sabon karin farashin man zuwa Naira 998 kowace lita a Legas da kuma Naira 1030 a Abuja na da matukar tasiri ga kasuwanci da gidaje a Nijeriya.

Har ila yau, Kungiyar ‘Yan Kasuwa (TUC) ta bukaci gwamnatin tarayya da ta aiwatar da wani shiri na musamman na musayar kudaden waje ga matatar Dangote domin daidaitawa da rage farashin man fetur.

Shugaban TUC, Festus Osifo a wani taron tattaunawa da aka yi jiya a Abuja, ya bayyana cewa, rage ka’idojin da aka samu a bangaren man fetur, tare da sauye-sauyen canjin kudi ne, ya haifar da hauhawar farashin mai, inda farashin ya haura Naira 1,000 kan kowace lita.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kara FarashiMan feturTalakaTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

A Farfado Da Rayuwar Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Maiduguri

Next Post

Shekara 90: Gwagwarmayar Rayuwar Janar Gowon Da Tasirinsa A Nijeriya

Related

NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai
Manyan Labarai

NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai

2 hours ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 2 Da Wasu 156 Kan Aikata Laifuka A Jigawa

17 hours ago
Sojoji Sun Kwato Makamai Da Babura, Sun Ceto Mutane 3 A Kaduna 
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Bindiga Ɗauke Da Makamai A Jihar Filato

20 hours ago
Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai
Da ɗumi-ɗuminsa

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

1 day ago
Ministan Tsaro
Manyan Labarai

Dawowar Matsalar Tsaro: Ta Haifar Da Cece-kuce Kan Daukar Matakin Kare Kai

1 day ago
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 13 A Wani Harin Kwanton-ɓauna A Borno
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 13 A Wani Harin Kwanton-ɓauna A Borno

2 days ago
Next Post
Shekara 90: Gwagwarmayar Rayuwar Janar Gowon Da Tasirinsa A Nijeriya

Shekara 90: Gwagwarmayar Rayuwar Janar Gowon Da Tasirinsa A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

September 6, 2025

Ilimi Shi Ne Matakin Nasarar Rayuwar Duniya Da Lahira – Yerima Shettima

September 6, 2025
NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai

NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai

September 6, 2025
Maulidi: Gwamnan Zamfara Ya Taya Al’ummar Musulmi Murna, Ya Buƙaci A Dage Da Addu’o’in Samun Zaman Lafiya

Maulidi: Gwamnan Zamfara Ya Taya Al’ummar Musulmi Murna, Ya Buƙaci A Dage Da Addu’o’in Samun Zaman Lafiya

September 6, 2025
Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

September 5, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

September 5, 2025
Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

September 5, 2025
Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 

Ana Ci Gaba Da Caccakar El-rufai Kan Kalamansa Game Da Tsaron Kasa

September 5, 2025
Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

September 5, 2025
Yadda Al’ummar Da Ke Zaune Da ‘Yan Bindiga Ke Rayuwa A Zamfara

Duk Da Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ana Ci Gaba Da Kai Hare-hare Wasu Yankunan Zamfara

September 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.