ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

by CGTN Hausa and Sulaiman
8 months ago
Sin

A yayin taron sauyin yanayi na MDD na watan Satumba, a karon farko a tarihin kasar Sin, shugaban kasar Xi Jinping ya gabatar da sabbin matakan kasa na samar da gudunmawa ga cimma nasarar yarjejeniyar sauyin yanayi ko NDCs a takaice, mai kunshe da dukkanin burikan tattalin arziki masu nasaba da kawo karshen fitar da dukkanin nau’ikan hayaki masu dumama yanayi.

 

To ko me wadannan matakai suka kunsa? Amsar a bayyane take, domin kuwa Sin ta sha alwashin nan zuwa shekarar 2035, za ta rage fitar da nau’o’in hayaki masu dumama yanayi da kaso 7 zuwa kaso 10 bisa dari, daga kololuwar matakan fitar da su, da kara adadin kasonta cikin jimillar makamashin da take amfani da shi daga hanyoyin da ba na kona mai ko iskar gas ba zuwa sama da kaso 30 bisa dari. Kana Sin din za ta fadada adadin cibiyoyin samar da lantarki ta iska, da hasken rana zuwa sama da rubi shida kan matsayin da take a shekarar 2020.

ADVERTISEMENT
  • Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 
  • An Kama Wani Mutum Kan Zargin Kashe Matarsa A Sakkwato

Baya ga wadannan matakai, shugaban na Sin ya gabatar da shawarwari uku, da suka hada da bukatar karfafa gwiwa domin tunkarar aikin da aka sanya gaba, da kira ga sassa masu ruwa da tsaki da su sauke nauyin dake wuyansu, da jaddada muhimmancin zurfafa hadin gwiwa. Wanda hakan ya samu matukar karbuwa tsakanin masharhanta, da masu lura da harkokin da suka shafi sauyin yanayi. Duk da haka, akwai wasu sassa musamman na yammacin duniya da suka nuna rashin gamsuwa da kwazon na kasar Sin. Idan wadannan bangarori sun kawar da kai daga shaidu na zahiri, masu nuni ga manyan nasarori da Sin ta cimma a wannan fanni.

 

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Ko shakka babu, yunkurin kasar Sin na cimma nasarar kawar da fitar da hayakin carbon daga kololuwar matsayinsa nan zuwa shekarar 2060 ya cancanci yabo. Kuma abu ne mai yiwuwa, duba da nasarorin baya da kasar ta cimma, ciki har da nasarar da ta samu ta rage fitar da hayakin na carbon a shekarar 2020 da kaso 60 bisa dari kan na shekarar 2005, adadin da ya haura hasashen nasarar da aka yi fata da karin kaso 40 zuwa 45 bisa dari.

 

A fannin cimma burikan kafa karin cibiyoyin samar da lantarki ta iska da hasken rana kuwa, yanzu haka kasar Sin ta kai inda take buri, tun ma kafin shekarar 2030 da a baya aka tsara cimma burin hakan. A daya bangaren kuma, tana tallafawa wasu kasashe masu tasowa, karkashin manufofi irin su hadin gwiwar gina shawarar “ziri daya da hanya daya”, wajen aiwatar da dabarun dakile sauyin yanayi, da jure tasirinsa, da aiwatar da dubban matakai masu nasaba da hakan.

 

Tabbas kowa ya yarda cewa shawo kan kalubalen sauyin yanayi na bukatar hadin gwiwar dukkanin sassa, kuma la’akari da gudunmawar da Sin ke bayarwa a gida da waje, ma iya cewa tana kan turbar jagorantar duniya wajen cimma nasarar hakan ta yadda za a gudu tare a tsira tare, wato a kai ga cin gajiyar kyakkyawan muhallin duniya mai kayatarwa. (Saminu Alhassan)

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje
  • Sulaiman
    Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa
  • Sulaiman
    Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci
  • Sulaiman
    Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

MASU ALAKA

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje
Daga Birnin Sin

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa
Daga Birnin Sin

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026
Daga Birnin Sin

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Next Post
Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.