• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karin Kudin Mai: Hakika An Ci Amanarmu, In Ji ‘Yan Kwadago

by Rabi'u Ali Indabawa and Khalid Idris Doya
1 year ago
in Manyan Labarai
0
Karin Kudin Mai: Hakika An Ci Amanarmu, In Ji ‘Yan Kwadago
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dangane da abin da ya shafi karin kudin mai da gwamnati ta yi, mun lura da irin cin amanar da gwamnatin tarayya ta yi asirce na kara wannan farashi. Kuma a fahimtarmu shi ne daga daga cikin dalilan amincewa da Naira 70,000 a matsayin mafi karancin albashi, wanda mun sani cewa gwamnati ba za a kara farashin duk da cewa Naira 70,000 din ma ba za ta wadatar da ma’aikata ba.

Mun tuna a fili lokacin da shugaban kasa ya bamu zabe cewa: ko dai Naira 250,000 a matsayin mafi karancin albashi, amma za a yi karin kudin mai tsakanin Naira 1,500 zuwa Naiar 2,000) da kuma Naira 70,000 (a tsohon farashi)., sai muka zabi na karshe. Mun yi haka ne don ba za mu yi sanadin jefa ’yan Nijeriya a kuncin rayuwa ba.

  • A Gaggauta Janye Ƙara Farashin Man Fetur – NLC Ga Gwamnatin Tarayya 
  • Gwamnatin Tarayya Ta Fara Sayar Da Buhun Shinkafa Kan Dubu 30

Sai gashi wata daya da ayyana hakan amma gwamnati ba ta fara biyan sabon mafi karancin albashin ma’aikata na kasa ba kuma ta zo da wani sabon lamari da za mu lamunce shi ba.

 

Gaba daya lamarin ya zama wani mafarki mai ban tsoro

Labarai Masu Nasaba

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Amma duk da haka, lokacin da muka gaya wa gwamnati cewa matakin da za a bi don magance wannan lamari ba zai haifar da da mai ido ba,  kuma ba abu ne da zai dore ba, sai wasu shugabanni daga cikinsu  suka rika yi mana izgilanci cewa, ba mu fahimci asaln yadda tattalin arziki yake ba.

Kwadago

 

To amma idan za a kalli gaskiya, wannan aikin ne na cin amana da ya yi daidai da halayyar wannan gwamnati. Mun tuna da tabbacin da shugabannin majalisar suka ba mu kan karin kudin fito na kashi 250% na cewa an magance shi kuma babu bukatar sai an gabatar da Ministan wutar lantarki da ke wajen taron.

Maimakon a dawo da batun tsohon farshin da aka yi alkawari tun daga wancan lokacin, ai kawai sai farashin man ya sake tashin gwauron zabo inda ya kara jefa ‘yan Nijeriya da ‘yan kasuwa cikin mawuyacin hali.

Maimakon yin gyara, gwamnati ta kama tare da tsare wasu daga cikin wadanda suka halarci zanga-zangar, wasu kuma wadanda ba su da alaka da wannan zanga-zangar, tana tuhumar su da laifin hada baki, zagon kasa, cin amanar kasa, bayar da kudaden ta’addanci da kuma aikata laifuka ta intanet da nufin kifar da gwamnatin shugaba Tinubu.

Tuni dai ‘yansanda da sauran jami’an tsaro suka ci gaba da addabar al’ummar kasar domin cimma manufofin gwamnati na murkushe ‘yan adawa masu mutunci.

Suka yi tsayin daka wajen bata suna da kuma tozarta dimbim al’umma.

Sun yi nisa wajen daidaita ayyukan da doka ta tanada na Ma’aikatar Kwadago da Aiki wajen warware batutuwan da suka shafi kasuwanci da kuma batutuwan da ba su dace da hukumomin tsaro ba.

A halin da ake ciki gwamnati na ta muzgunawa gami da takurawa rayuwar al’umma, wanda kuma hakan ba karamin al’amari bane, amma muna yi wa ‘yan Nijeriya alkawari cewa mu a Kungiyar Kwadago ta Nijeriya, tare da kungiyoyin farar hula ba za a yi wa kasa biyayya ba, kuma mu muka kawo wannan dimokuradiyya a lokacin da wasu daga cikin masu rike da madafun iko a yau suke hada baki da sojoji kan yadda za su ci gaba da rike madafun iko na siyasa.

Lokacin da Jami’an tsaro suka kama mu a wannan gwagwarmaya, mun sha zargi. Mun san sun suna da wani mugun nufi da kuma bukatar su karkatar da hankalinmu ko su firgita mu ko raunanawa mu don kada mu sami amsa mai kyakkyawar hujja.

Yanzu dai burinsu ya cika, kuma gaskiyarmu ta bayyana a cikin zargin da muka yi musu. Duk da haka, muna so mu sanar da ‘yan Nijeriya cewa sun cimma burinsu na kara farashin man fertur wanda shi ne na farko a cikin daidaitattun manufofin da gwamnati ke kai.

A namu bangaren, mun tsaya tsayin daka kan hakkin jama’a, kuma ba za mu bari gwamnati ko jami’anta na tsaro su janye hankalinmu ba ko kuma su tsorata mu.

 

Saboda haka, muna bukatar aiwatar da wadannan abubuwa cikin gaggawa::

1). Janye sabon farashin man fetur da aka kara;

2). Sakin duk wadanda ake tsare da su ko kuma ake tuhumar su bisa zaton sun shiga zanga-zangar kwanan nan;

3). Dakatar da kamawa gami da tsare ’yan kasa bisa zargin karya;

4). Janye karin kudin wutar lantarki;

5). Kawo karshen yin sama da fadi da ayyukan Ma’aikatar Kwadago da Aiki;

6). Kawo karshen manufofin da ke haifar da yunwa da rashin tsaro;

7). Dakatar da dabi’ar gwamnati na ta’addanci, tsoro da karya.

 

‘Yan Nijeriya Na Cikin Tsaka-mai-wuya Yayin Ake Sayar Da Litar Mai Naira 1,000

‘Yan Nijeriya a sassan kasar sun shiga halin damuwa da tsananin kokawa yayin da tilas ta sanya suke sayan litar man fetur a kan kudi har naira 1,000 a sassa daban-daban da suke fadin kasar.

Wannan lamarin dai na zuwa ne a daidai lokacin da matatar man Dangote ta bai wa kamfanin kula da albarkatun mai ta Nijeriya (NNPCL) damar ficewa daga tsarin shigo da mai daga kasar waje domin za a iya share mata hawayenta a cikin nan gida Nijeriya muddin ta amince.

Tun da farko dai, matatar man Dagote da ke Legas ta tabbatar wa majiyarmu cewa tana da karfin fitar da ganga 650,000 kowace rana.

A cewar jami’in watsa labarai na rukunin kamfanonin Dangote, Anthony Chiejina, ya ce, man Dangote tabbas zai iya share wa al’ummar Nijeriya hawaye da dogon layin neman mai da suke kan yi gami da wahalar samun mai din.

“Kamfanin ya fara sarrafa man fetur. A daidai lokacin da ya kai matakin shiga kasuwa za ku ga tasirinsa.

Fara sarrafa man Dangote na zuwa ne daidai lokacin da kamfanin NNPCL ke fargabar yadda ake kashe maguden kudade wajen biyan kudin jigilar mai da kuma tulin basukan da ake bin dillalai mai da ya haura sama da dala biliyan 6.

Kakakin kamfanin, Olufemi Soneye, ya shaida cewar kalubalen yawan kudade na barazana ga daurewar jigilar mai a kasar nan. Babban matsalar dai shi ne, kudin shigo da mai daga waje.

Bayanin bazaranar kudi na NNPCL ya ta da hankula, inda masu ruwa da tsaki a bangaren mai da iskar gas suka dukufa tofa albarkacin bakinsu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FeturJayin AikiKwadagoMai
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mace-mace A Wuraren Hakar Ma’adanai

Next Post

Kusantar Annabi (SAW) Da Allah

Related

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis
Manyan Labarai

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

2 hours ago
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

3 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
Manyan Labarai

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

6 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

15 hours ago
Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

20 hours ago
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025
Da ɗumi-ɗuminsa

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

22 hours ago
Next Post
Kusantar Annabi (SAW) Da Allah

Kusantar Annabi (SAW) Da Allah

LABARAI MASU NASABA

Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

September 18, 2025
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

September 18, 2025
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

September 18, 2025
’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

September 18, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

September 18, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

September 17, 2025
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

September 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

September 17, 2025
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

September 17, 2025
Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.