ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karin Kudin Mai: Hakika An Ci Amanarmu, In Ji ‘Yan Kwadago

by Rabi'u Ali Indabawa and Khalid Idris Doya
2 years ago
Kwadago

Dangane da abin da ya shafi karin kudin mai da gwamnati ta yi, mun lura da irin cin amanar da gwamnatin tarayya ta yi asirce na kara wannan farashi. Kuma a fahimtarmu shi ne daga daga cikin dalilan amincewa da Naira 70,000 a matsayin mafi karancin albashi, wanda mun sani cewa gwamnati ba za a kara farashin duk da cewa Naira 70,000 din ma ba za ta wadatar da ma’aikata ba.

Mun tuna a fili lokacin da shugaban kasa ya bamu zabe cewa: ko dai Naira 250,000 a matsayin mafi karancin albashi, amma za a yi karin kudin mai tsakanin Naira 1,500 zuwa Naiar 2,000) da kuma Naira 70,000 (a tsohon farashi)., sai muka zabi na karshe. Mun yi haka ne don ba za mu yi sanadin jefa ’yan Nijeriya a kuncin rayuwa ba.

  • A Gaggauta Janye Ƙara Farashin Man Fetur – NLC Ga Gwamnatin Tarayya 
  • Gwamnatin Tarayya Ta Fara Sayar Da Buhun Shinkafa Kan Dubu 30

Sai gashi wata daya da ayyana hakan amma gwamnati ba ta fara biyan sabon mafi karancin albashin ma’aikata na kasa ba kuma ta zo da wani sabon lamari da za mu lamunce shi ba.

ADVERTISEMENT

 

Gaba daya lamarin ya zama wani mafarki mai ban tsoro

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Amma duk da haka, lokacin da muka gaya wa gwamnati cewa matakin da za a bi don magance wannan lamari ba zai haifar da da mai ido ba,  kuma ba abu ne da zai dore ba, sai wasu shugabanni daga cikinsu  suka rika yi mana izgilanci cewa, ba mu fahimci asaln yadda tattalin arziki yake ba.

Kwadago

 

To amma idan za a kalli gaskiya, wannan aikin ne na cin amana da ya yi daidai da halayyar wannan gwamnati. Mun tuna da tabbacin da shugabannin majalisar suka ba mu kan karin kudin fito na kashi 250% na cewa an magance shi kuma babu bukatar sai an gabatar da Ministan wutar lantarki da ke wajen taron.

Maimakon a dawo da batun tsohon farshin da aka yi alkawari tun daga wancan lokacin, ai kawai sai farashin man ya sake tashin gwauron zabo inda ya kara jefa ‘yan Nijeriya da ‘yan kasuwa cikin mawuyacin hali.

Maimakon yin gyara, gwamnati ta kama tare da tsare wasu daga cikin wadanda suka halarci zanga-zangar, wasu kuma wadanda ba su da alaka da wannan zanga-zangar, tana tuhumar su da laifin hada baki, zagon kasa, cin amanar kasa, bayar da kudaden ta’addanci da kuma aikata laifuka ta intanet da nufin kifar da gwamnatin shugaba Tinubu.

Tuni dai ‘yansanda da sauran jami’an tsaro suka ci gaba da addabar al’ummar kasar domin cimma manufofin gwamnati na murkushe ‘yan adawa masu mutunci.

Suka yi tsayin daka wajen bata suna da kuma tozarta dimbim al’umma.

Sun yi nisa wajen daidaita ayyukan da doka ta tanada na Ma’aikatar Kwadago da Aiki wajen warware batutuwan da suka shafi kasuwanci da kuma batutuwan da ba su dace da hukumomin tsaro ba.

A halin da ake ciki gwamnati na ta muzgunawa gami da takurawa rayuwar al’umma, wanda kuma hakan ba karamin al’amari bane, amma muna yi wa ‘yan Nijeriya alkawari cewa mu a Kungiyar Kwadago ta Nijeriya, tare da kungiyoyin farar hula ba za a yi wa kasa biyayya ba, kuma mu muka kawo wannan dimokuradiyya a lokacin da wasu daga cikin masu rike da madafun iko a yau suke hada baki da sojoji kan yadda za su ci gaba da rike madafun iko na siyasa.

Lokacin da Jami’an tsaro suka kama mu a wannan gwagwarmaya, mun sha zargi. Mun san sun suna da wani mugun nufi da kuma bukatar su karkatar da hankalinmu ko su firgita mu ko raunanawa mu don kada mu sami amsa mai kyakkyawar hujja.

Yanzu dai burinsu ya cika, kuma gaskiyarmu ta bayyana a cikin zargin da muka yi musu. Duk da haka, muna so mu sanar da ‘yan Nijeriya cewa sun cimma burinsu na kara farashin man fertur wanda shi ne na farko a cikin daidaitattun manufofin da gwamnati ke kai.

A namu bangaren, mun tsaya tsayin daka kan hakkin jama’a, kuma ba za mu bari gwamnati ko jami’anta na tsaro su janye hankalinmu ba ko kuma su tsorata mu.

 

Saboda haka, muna bukatar aiwatar da wadannan abubuwa cikin gaggawa::

1). Janye sabon farashin man fetur da aka kara;

2). Sakin duk wadanda ake tsare da su ko kuma ake tuhumar su bisa zaton sun shiga zanga-zangar kwanan nan;

3). Dakatar da kamawa gami da tsare ’yan kasa bisa zargin karya;

4). Janye karin kudin wutar lantarki;

5). Kawo karshen yin sama da fadi da ayyukan Ma’aikatar Kwadago da Aiki;

6). Kawo karshen manufofin da ke haifar da yunwa da rashin tsaro;

7). Dakatar da dabi’ar gwamnati na ta’addanci, tsoro da karya.

 

‘Yan Nijeriya Na Cikin Tsaka-mai-wuya Yayin Ake Sayar Da Litar Mai Naira 1,000

‘Yan Nijeriya a sassan kasar sun shiga halin damuwa da tsananin kokawa yayin da tilas ta sanya suke sayan litar man fetur a kan kudi har naira 1,000 a sassa daban-daban da suke fadin kasar.

Wannan lamarin dai na zuwa ne a daidai lokacin da matatar man Dangote ta bai wa kamfanin kula da albarkatun mai ta Nijeriya (NNPCL) damar ficewa daga tsarin shigo da mai daga kasar waje domin za a iya share mata hawayenta a cikin nan gida Nijeriya muddin ta amince.

Tun da farko dai, matatar man Dagote da ke Legas ta tabbatar wa majiyarmu cewa tana da karfin fitar da ganga 650,000 kowace rana.

A cewar jami’in watsa labarai na rukunin kamfanonin Dangote, Anthony Chiejina, ya ce, man Dangote tabbas zai iya share wa al’ummar Nijeriya hawaye da dogon layin neman mai da suke kan yi gami da wahalar samun mai din.

“Kamfanin ya fara sarrafa man fetur. A daidai lokacin da ya kai matakin shiga kasuwa za ku ga tasirinsa.

Fara sarrafa man Dangote na zuwa ne daidai lokacin da kamfanin NNPCL ke fargabar yadda ake kashe maguden kudade wajen biyan kudin jigilar mai da kuma tulin basukan da ake bin dillalai mai da ya haura sama da dala biliyan 6.

Kakakin kamfanin, Olufemi Soneye, ya shaida cewar kalubalen yawan kudade na barazana ga daurewar jigilar mai a kasar nan. Babban matsalar dai shi ne, kudin shigo da mai daga waje.

Bayanin bazaranar kudi na NNPCL ya ta da hankula, inda masu ruwa da tsaki a bangaren mai da iskar gas suka dukufa tofa albarkacin bakinsu.

Kwadago
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas
Kwadago
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ‘Yansanda Sun Cafke Tsoho Mai Shekara 70 Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 8 Fyaɗe A Bauchi

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
Next Post
Kusantar Annabi (SAW) Da Allah

Kusantar Annabi (SAW) Da Allah

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.