• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karin Kudin Mai: Hakika An Ci Amanarmu, In Ji ‘Yan Kwadago

byRabi'u Ali Indabawa and Khalid Idris Doya
1 year ago
Kwadago

Dangane da abin da ya shafi karin kudin mai da gwamnati ta yi, mun lura da irin cin amanar da gwamnatin tarayya ta yi asirce na kara wannan farashi. Kuma a fahimtarmu shi ne daga daga cikin dalilan amincewa da Naira 70,000 a matsayin mafi karancin albashi, wanda mun sani cewa gwamnati ba za a kara farashin duk da cewa Naira 70,000 din ma ba za ta wadatar da ma’aikata ba.

Mun tuna a fili lokacin da shugaban kasa ya bamu zabe cewa: ko dai Naira 250,000 a matsayin mafi karancin albashi, amma za a yi karin kudin mai tsakanin Naira 1,500 zuwa Naiar 2,000) da kuma Naira 70,000 (a tsohon farashi)., sai muka zabi na karshe. Mun yi haka ne don ba za mu yi sanadin jefa ’yan Nijeriya a kuncin rayuwa ba.

  • A Gaggauta Janye Ƙara Farashin Man Fetur – NLC Ga Gwamnatin Tarayya 
  • Gwamnatin Tarayya Ta Fara Sayar Da Buhun Shinkafa Kan Dubu 30

Sai gashi wata daya da ayyana hakan amma gwamnati ba ta fara biyan sabon mafi karancin albashin ma’aikata na kasa ba kuma ta zo da wani sabon lamari da za mu lamunce shi ba.

 

Gaba daya lamarin ya zama wani mafarki mai ban tsoro

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Amma duk da haka, lokacin da muka gaya wa gwamnati cewa matakin da za a bi don magance wannan lamari ba zai haifar da da mai ido ba,  kuma ba abu ne da zai dore ba, sai wasu shugabanni daga cikinsu  suka rika yi mana izgilanci cewa, ba mu fahimci asaln yadda tattalin arziki yake ba.

Kwadago

 

To amma idan za a kalli gaskiya, wannan aikin ne na cin amana da ya yi daidai da halayyar wannan gwamnati. Mun tuna da tabbacin da shugabannin majalisar suka ba mu kan karin kudin fito na kashi 250% na cewa an magance shi kuma babu bukatar sai an gabatar da Ministan wutar lantarki da ke wajen taron.

Maimakon a dawo da batun tsohon farshin da aka yi alkawari tun daga wancan lokacin, ai kawai sai farashin man ya sake tashin gwauron zabo inda ya kara jefa ‘yan Nijeriya da ‘yan kasuwa cikin mawuyacin hali.

Maimakon yin gyara, gwamnati ta kama tare da tsare wasu daga cikin wadanda suka halarci zanga-zangar, wasu kuma wadanda ba su da alaka da wannan zanga-zangar, tana tuhumar su da laifin hada baki, zagon kasa, cin amanar kasa, bayar da kudaden ta’addanci da kuma aikata laifuka ta intanet da nufin kifar da gwamnatin shugaba Tinubu.

Tuni dai ‘yansanda da sauran jami’an tsaro suka ci gaba da addabar al’ummar kasar domin cimma manufofin gwamnati na murkushe ‘yan adawa masu mutunci.

Suka yi tsayin daka wajen bata suna da kuma tozarta dimbim al’umma.

Sun yi nisa wajen daidaita ayyukan da doka ta tanada na Ma’aikatar Kwadago da Aiki wajen warware batutuwan da suka shafi kasuwanci da kuma batutuwan da ba su dace da hukumomin tsaro ba.

A halin da ake ciki gwamnati na ta muzgunawa gami da takurawa rayuwar al’umma, wanda kuma hakan ba karamin al’amari bane, amma muna yi wa ‘yan Nijeriya alkawari cewa mu a Kungiyar Kwadago ta Nijeriya, tare da kungiyoyin farar hula ba za a yi wa kasa biyayya ba, kuma mu muka kawo wannan dimokuradiyya a lokacin da wasu daga cikin masu rike da madafun iko a yau suke hada baki da sojoji kan yadda za su ci gaba da rike madafun iko na siyasa.

Lokacin da Jami’an tsaro suka kama mu a wannan gwagwarmaya, mun sha zargi. Mun san sun suna da wani mugun nufi da kuma bukatar su karkatar da hankalinmu ko su firgita mu ko raunanawa mu don kada mu sami amsa mai kyakkyawar hujja.

Yanzu dai burinsu ya cika, kuma gaskiyarmu ta bayyana a cikin zargin da muka yi musu. Duk da haka, muna so mu sanar da ‘yan Nijeriya cewa sun cimma burinsu na kara farashin man fertur wanda shi ne na farko a cikin daidaitattun manufofin da gwamnati ke kai.

A namu bangaren, mun tsaya tsayin daka kan hakkin jama’a, kuma ba za mu bari gwamnati ko jami’anta na tsaro su janye hankalinmu ba ko kuma su tsorata mu.

 

Saboda haka, muna bukatar aiwatar da wadannan abubuwa cikin gaggawa::

1). Janye sabon farashin man fetur da aka kara;

2). Sakin duk wadanda ake tsare da su ko kuma ake tuhumar su bisa zaton sun shiga zanga-zangar kwanan nan;

3). Dakatar da kamawa gami da tsare ’yan kasa bisa zargin karya;

4). Janye karin kudin wutar lantarki;

5). Kawo karshen yin sama da fadi da ayyukan Ma’aikatar Kwadago da Aiki;

6). Kawo karshen manufofin da ke haifar da yunwa da rashin tsaro;

7). Dakatar da dabi’ar gwamnati na ta’addanci, tsoro da karya.

 

‘Yan Nijeriya Na Cikin Tsaka-mai-wuya Yayin Ake Sayar Da Litar Mai Naira 1,000

‘Yan Nijeriya a sassan kasar sun shiga halin damuwa da tsananin kokawa yayin da tilas ta sanya suke sayan litar man fetur a kan kudi har naira 1,000 a sassa daban-daban da suke fadin kasar.

Wannan lamarin dai na zuwa ne a daidai lokacin da matatar man Dangote ta bai wa kamfanin kula da albarkatun mai ta Nijeriya (NNPCL) damar ficewa daga tsarin shigo da mai daga kasar waje domin za a iya share mata hawayenta a cikin nan gida Nijeriya muddin ta amince.

Tun da farko dai, matatar man Dagote da ke Legas ta tabbatar wa majiyarmu cewa tana da karfin fitar da ganga 650,000 kowace rana.

A cewar jami’in watsa labarai na rukunin kamfanonin Dangote, Anthony Chiejina, ya ce, man Dangote tabbas zai iya share wa al’ummar Nijeriya hawaye da dogon layin neman mai da suke kan yi gami da wahalar samun mai din.

“Kamfanin ya fara sarrafa man fetur. A daidai lokacin da ya kai matakin shiga kasuwa za ku ga tasirinsa.

Fara sarrafa man Dangote na zuwa ne daidai lokacin da kamfanin NNPCL ke fargabar yadda ake kashe maguden kudade wajen biyan kudin jigilar mai da kuma tulin basukan da ake bin dillalai mai da ya haura sama da dala biliyan 6.

Kakakin kamfanin, Olufemi Soneye, ya shaida cewar kalubalen yawan kudade na barazana ga daurewar jigilar mai a kasar nan. Babban matsalar dai shi ne, kudin shigo da mai daga waje.

Bayanin bazaranar kudi na NNPCL ya ta da hankula, inda masu ruwa da tsaki a bangaren mai da iskar gas suka dukufa tofa albarkacin bakinsu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi
Manyan Labarai

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
Next Post
Kusantar Annabi (SAW) Da Allah

Kusantar Annabi (SAW) Da Allah

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version