• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karramawa: Ma’aikatan Kano Sun Yaba Wa Jagorancin Gwamna Abba Na Tausayi

by Sadiq
6 months ago
in Labarai
0
Karramawa: Ma’aikatan Kano Sun Yaba Wa Jagorancin Gwamna Abba Na Tausayi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ma’aikatan Jihar Kano, sun jinjina wa Gwamna Abba Kabir Yusuf, bisa karramawar da ya samu na “Gwamnan Da Yafi Tausaya wa Ma’aikata” wanda Ƙungiyar Ƙwadago ta Nijeriya (NLC), reshen Kano, ta bayar.

A cikin saƙon taya murna da ya sanya wa hannu, Shugaban Ma’aikatan Jihar Kano, Abdullahi Musa, ya yaba wa gwamnan kan muhimman sauye-sauyen da ya kawo da suka inganta jin daɗin ma’aikatan jihar.

  • Zanga-zangar Yunwa: ‘Yansanda Sun Buƙaci Amnesty Ta Janye Zargin Tauye Haƙƙi
  • Saurayi Ya Fille Kan Budurwarsa A Nasarawa

Daga cikin nasarorin gwamnan akwai ƙara kuɗin fansho daga Naira 5,000 zuwa Naira 20,000, shigar da ma’aikata 10,000 da aka ɗauka a baya cikin sahun aikin gwamnati.

Sauran sun haɗa da ɗaukar sabbin ma’aikatan lafiya, malamai, da jami’an tsaro.

Bugu da ƙari, Gwamna Abba ya amince da sabon mafi ƙarancin albashi na Naira 71,000, wanda ya zarce na gwamnatin tarayya.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

Haka kuma, gwamnatinsa ta yi adalci wajen naɗin sakatarorin dindindin, inda aka daina yin siyasa a naɗin.

Gwamnan ya kuma biya bashin fansho sama da Naira biliyan 16, tare da tabbatar da biyan albashi da fansho a kan lokaci, wanda ya tabbatar da amincin gwamnatin wajen sarrafa kudaden jama’a.

Gwamnan ya mayar da hankali wajen horarwa da sake fasalin ma’aikatan gwamnati don ƙara musu ƙwarewa da inganta ayyukansu.

Ta hanyar shirye-shiryen horarwa da kyautata yanayin aiki, gwamnatinsa ta shimfiɗa tubalin ci gaba mai ɗorewa da inganta shugabanci.

An kuma yi kira ga ma’aikata su ci gaba da himma wajen gudanar da ayyukansu, domin ci gaban Jihar Kano.

Karramawar da NLC ta yi wa Gwamna Abba ba kawai yabo ba ne, alama ce ta haɗin kan gwamnati da ma’aikata wajen kawo ci gaba mai amfani.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamna AbbajagorancikanoKarramaNlcTausayi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Zanga-zangar Yunwa: ‘Yansanda Sun Buƙaci Amnesty Ta Janye Zargin Tauye Haƙƙi

Next Post

Hauhawar Farashin Kayayyaki Ya Kai Kashi 34.80 A Disamban 2024 – NBS

Related

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano
Labarai

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

1 hour ago
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark
Labarai

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

2 hours ago
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara
Labarai

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

6 hours ago
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace
Labarai

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

7 hours ago
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
Wasanni

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

16 hours ago
Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta
Labarai

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

18 hours ago
Next Post
Hauhawar Farashin Kayayyaki Ya Kai Kashi 34.80 A Disamban 2024 – NBS

Hauhawar Farashin Kayayyaki Ya Kai Kashi 34.80 A Disamban 2024 - NBS

LABARAI MASU NASABA

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

July 27, 2025
Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

July 27, 2025
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

July 27, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

July 27, 2025
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

July 27, 2025
aure

Ko Kin San… Matsalolin Mahaifa Da Suke Hana Haihuwa 

July 27, 2025
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

July 27, 2025
Yadda Ake Faten Acca

Yadda Ake Faten Acca

July 27, 2025
Hanyoyin Gyaran Gashi

Hanyoyin Gyaran Gashi

July 27, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.