• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karramawa: Ma’aikatan Kano Sun Yaba Wa Jagorancin Gwamna Abba Na Tausayi

bySadiq
9 months ago
Abba

Ma’aikatan Jihar Kano, sun jinjina wa Gwamna Abba Kabir Yusuf, bisa karramawar da ya samu na “Gwamnan Da Yafi Tausaya wa Ma’aikata” wanda Ƙungiyar Ƙwadago ta Nijeriya (NLC), reshen Kano, ta bayar.

A cikin saƙon taya murna da ya sanya wa hannu, Shugaban Ma’aikatan Jihar Kano, Abdullahi Musa, ya yaba wa gwamnan kan muhimman sauye-sauyen da ya kawo da suka inganta jin daɗin ma’aikatan jihar.

  • Zanga-zangar Yunwa: ‘Yansanda Sun Buƙaci Amnesty Ta Janye Zargin Tauye Haƙƙi
  • Saurayi Ya Fille Kan Budurwarsa A Nasarawa

Daga cikin nasarorin gwamnan akwai ƙara kuɗin fansho daga Naira 5,000 zuwa Naira 20,000, shigar da ma’aikata 10,000 da aka ɗauka a baya cikin sahun aikin gwamnati.

Sauran sun haɗa da ɗaukar sabbin ma’aikatan lafiya, malamai, da jami’an tsaro.

Bugu da ƙari, Gwamna Abba ya amince da sabon mafi ƙarancin albashi na Naira 71,000, wanda ya zarce na gwamnatin tarayya.

LABARAI MASU NASABA

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

Haka kuma, gwamnatinsa ta yi adalci wajen naɗin sakatarorin dindindin, inda aka daina yin siyasa a naɗin.

Gwamnan ya kuma biya bashin fansho sama da Naira biliyan 16, tare da tabbatar da biyan albashi da fansho a kan lokaci, wanda ya tabbatar da amincin gwamnatin wajen sarrafa kudaden jama’a.

Gwamnan ya mayar da hankali wajen horarwa da sake fasalin ma’aikatan gwamnati don ƙara musu ƙwarewa da inganta ayyukansu.

Ta hanyar shirye-shiryen horarwa da kyautata yanayin aiki, gwamnatinsa ta shimfiɗa tubalin ci gaba mai ɗorewa da inganta shugabanci.

An kuma yi kira ga ma’aikata su ci gaba da himma wajen gudanar da ayyukansu, domin ci gaban Jihar Kano.

Karramawar da NLC ta yi wa Gwamna Abba ba kawai yabo ba ne, alama ce ta haɗin kan gwamnati da ma’aikata wajen kawo ci gaba mai amfani.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Next Post
Hauhawar Farashin Kayayyaki Ya Kai Kashi 34.80 A Disamban 2024 – NBS

Hauhawar Farashin Kayayyaki Ya Kai Kashi 34.80 A Disamban 2024 - NBS

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version