• English
  • Business News
Saturday, May 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasafin Kudi Na 2025: Kowanne Ɗan Ƙasa Ɗaya Zai Kashe Ƙasa Da $2.15 – Rahoto

by Abubakar Abba
1 month ago
in Siyasa
0
Kasafin Kudi Na 2025: Kowanne Ɗan Ƙasa Ɗaya Zai Kashe Ƙasa Da $2.15 – Rahoto
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Idan aka yi nazari kan daukacin kasafin kudin Gwamnatin Tarayya da na jihohi na 2025, an lisaffa kasafin ne, kan dala 0.63, wanda kuma ya kai kasa da dala 2.15, da dan Nijeriya daya, zai iya kashe wa.

Wannan ya faru ne, kamar yadda Bankin Duniya ya ayyana cewa, talakan kasar, na cikin matsin talauci.

  • Yadda Rasuwar Galadima Abbas Ta Haɗa Kawuna ‘Yan Siyasar Kano Masu Hamayya Da Juna
  • Ofishin Siyasa Na Kwamitin Tsakiyar Jks Ya Kira Taron Nazarin Ayyukan Kiyaye Muhallin Halittu Da Sauransu

Hakazalika, wannan babban koma baya ne, musamman duba da yadda aka yi hasashen cewa, Nijeriya ce, kan gaba wajen fama da talauci.

An fitar da wannan bayanain ne, bisa wani sabon rahoto da wani Kamfanin yin bincike kan tattalin arziki na ADSR ya fitar a kan kasafin kudin na Gwamnatin Tarayya da kuma jihohi wanda duk dan Nijeriya daya, zai iya amfana wanda ya kai tsakanin daga dala 0.43 zuwa dala 0.21.

daukacin wannan adadin, ya kai kasa da daga kasa da dala 0.56 zuwa dala 0.36, sabainin na shekarar 2024.

Labarai Masu Nasaba

A Tsammaci Garambawul Ga Dokar Zabe Kafin Zaben 2027 — Shugaban INEC

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

“An tsara kasafin kudin na Gwamnatin Tarayya da na jihohin da dan Nijeriya daya zai amfana, musamman saboda talaucin da kasar ke ciki, bai wuce kasa da dala 2.15,”. Inji masu fashin bakin.

Kazalika, rahoton ya sanar da cewa, wannan ya nuna cewa, kasafin kudin na Gwamnatin Tarayya da na jihohin, ba za su iya biyan bukatun ‘yan kasar ba, musamman kan abinda ya shafi samun abinci, kula da kiwon lafiya da kuma samun ilimin zamani.

Kasafin kudin na Gwamnatin da dan Nijeriya day zai iya amfana, ya kai Naira 235,706, wanda hakan ke nuna cewa, kowanne dan Nijeriya daya, a kullum, zai iya kashe Naira 645.8, musamman idna har, kasafin kudin ya isa ga daukacin ‘yan kasar.

Hakazalika, a matakin jihohi kuwa, kasafin kudin, kowanne dan Nijeriya daya, a cikin shekara daya, zai iya kashe Naira 115,500, inda kuma a rana daya, kasafin ya kai Naira 317.

“Gaba dayan kasafin kudin na kasa, idan an rabawa ‘yan kasar, kowanne mutum daya, a cikin shekara daya, zai samu Naira 348,481 a cikin kasafin kudin na 2025, amma a nan, ana nufin idan kowanne dan kasar daya, zai iya samun Naira 955 a kullum daga cikin kasafin kudin,”. Acewar rahoton.

Kasafin kudin na 2025 a kan duk dan Nijeriya daya, ya nuna nawa ne, yawan jarin da Gwamantin Tarayya ta zuba kan dan kasar daya kuma nawa ne, ta shirya za ta kashe a kan kowanne dan Nijeriya daya.

karin fashin baki kan kasafin kudin na kasar na 2025 da ADSR ta yi, ya nuna cewa, jimlarsa da aka amince ya kai Naira tiriliyan 81.3.

Wannan ya hada da na Gwamnatin Tarayya da ya kai Naira tiriliyan 54.99 da kuma na jihohi da ya kai Naira tiriliyan 26.30, wanda hakan ya nuna cewa, an samu karin da ya kai na kaso 51.9, idan aka kwatanta da na shekarar 2024.

Kazalika, kasafin kudin na Gwamnatin Tarayya ya karu zuwa kaso The 56.9, inda kuma na gwamnatocin jihohin kasar, ya karu da kaso 42.4, musamman idan aka kwatanta da shekarar 2024.

Shugaban kasa Bola Tinubu, ta hanyar majalisar kasa ya kara yawan adadin kasafin kudin na bana daga Naira tiriliyan 49.7 zuwa Naira tiriliyan 54.2.

Bola ya yi hakan ne, domin ya kara bunkasa kashe kudade a kan manyan ayyuka, musamman duba da dakatar da tallafin jin kai, da da kasar Amurka, ke bai wa Nijeriya.

Sai dai, masu fashin bakin sun nuna damuwar su kan cewa, karain sama da Naira biliyan 700 a cikin kasafin kudin na shekarar 2025 da gwamnatin shugaba Bola Tinubu ta yi, ba zai samar da wasu sauye-sauyen azo a gani ba a kan tattalin arzikin kasar, musamman duba da ci gaba da biyan kudin ruwa na dimbin bashin da ake ci gaba da bin Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DalaKudi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sharhi Kan Dabarun Kiwon Bijimin Sa

Next Post

Nau’in Abinci Biyar Da Ke Lalata Hanta

Related

A Tsammaci Garambawul Ga Dokar Zabe Kafin Zaben 2027 — Shugaban INEC
Siyasa

A Tsammaci Garambawul Ga Dokar Zabe Kafin Zaben 2027 — Shugaban INEC

8 hours ago
NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC
Siyasa

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

1 day ago
Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya Gargaɗi Magoya Bayansa
Labarai

Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya Gargaɗi Magoya Bayansa

4 days ago
Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027
Siyasa

Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027

4 days ago
NNPP Ta Yi Asarar Ɗan Majalisa A Kano, Ya Koma APC
Siyasa

NNPP Ta Yi Asarar Ɗan Majalisa A Kano, Ya Koma APC

4 days ago
Uwargidan Jonathan Ta Bayyana Goyon Bayanta Ga Remi Tinubu
Siyasa

Uwargidan Jonathan Ta Bayyana Goyon Bayanta Ga Remi Tinubu

5 days ago
Next Post
Nau’in Abinci Biyar Da Ke Lalata Hanta

Nau’in Abinci Biyar Da Ke Lalata Hanta

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Lawal Ya Jaddada Aniyar Inganta Kiwon Lafiya A Jihar Zamfara

Gwamna Lawal Ya Jaddada Aniyar Inganta Kiwon Lafiya A Jihar Zamfara

May 16, 2025
Shugaban Senegal: Ana Fatan Ci Gaba Da Zurfafa Zumuncin Dake Tsakanin Sin Da Senegal

Shugaban Senegal: Ana Fatan Ci Gaba Da Zurfafa Zumuncin Dake Tsakanin Sin Da Senegal

May 16, 2025
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Daina Kassara Kamfanonin Fasaha Da Na AI Na Sin

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Daina Kassara Kamfanonin Fasaha Da Na AI Na Sin

May 16, 2025
JAMB Ta Ƙaddamar Da Binciken Gaggawa Kan Sakamakon Jarrabawar Bana Bayan Jerin Ƙorafe-Ƙorafe 

JAMB Ta Ƙaddamar Da Binciken Gaggawa Kan Sakamakon Jarrabawar Bana Bayan Jerin Ƙorafe-Ƙorafe 

May 16, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Ƙoƙarin Farfaɗo Da Sashin Raba Wutar Lantarki A Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Na Ƙoƙarin Farfaɗo Da Sashin Raba Wutar Lantarki A Nijeriya

May 16, 2025
CMG Ya Gabatar Da Fasahar Tsara Shirye-Shiryen Bidiyo Da Rediyo Bisa Fasahar Sadarwa Ta 5G A ITU

CMG Ya Gabatar Da Fasahar Tsara Shirye-Shiryen Bidiyo Da Rediyo Bisa Fasahar Sadarwa Ta 5G A ITU

May 16, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 2, Sun Ƙwato Shanun Sata 1,000 A Taraba

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 2, Sun Ƙwato Shanun Sata 1,000 A Taraba

May 16, 2025
Xi Jinping Ya Jaddada Wajibcin Koyi Da Nagartattun Halayen Wasu Mutane Masu Bukata Ta Musamman

Xi Jinping Ya Jaddada Wajibcin Koyi Da Nagartattun Halayen Wasu Mutane Masu Bukata Ta Musamman

May 16, 2025
Kasar Sin Ta Cimma Burinta A Fannin Kulla Yarjejeniyoyin Fasaha Kafin Lokacin Da Ta Tsara

Kasar Sin Ta Cimma Burinta A Fannin Kulla Yarjejeniyoyin Fasaha Kafin Lokacin Da Ta Tsara

May 16, 2025
Firaministan Sin: Tattalin Arzikin Sin Na Habaka Yadda Ya Kamata Yayin Da Kasar Ke Samun Ci Gaba

Firaministan Sin: Tattalin Arzikin Sin Na Habaka Yadda Ya Kamata Yayin Da Kasar Ke Samun Ci Gaba

May 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.