ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasafin Kudi Na 2025: Kowanne Ɗan Ƙasa Ɗaya Zai Kashe Ƙasa Da $2.15 – Rahoto

by Abubakar Abba
1 year ago
Kudi

Idan aka yi nazari kan daukacin kasafin kudin Gwamnatin Tarayya da na jihohi na 2025, an lisaffa kasafin ne, kan dala 0.63, wanda kuma ya kai kasa da dala 2.15, da dan Nijeriya daya, zai iya kashe wa.

Wannan ya faru ne, kamar yadda Bankin Duniya ya ayyana cewa, talakan kasar, na cikin matsin talauci.

  • Yadda Rasuwar Galadima Abbas Ta Haɗa Kawuna ‘Yan Siyasar Kano Masu Hamayya Da Juna
  • Ofishin Siyasa Na Kwamitin Tsakiyar Jks Ya Kira Taron Nazarin Ayyukan Kiyaye Muhallin Halittu Da Sauransu

Hakazalika, wannan babban koma baya ne, musamman duba da yadda aka yi hasashen cewa, Nijeriya ce, kan gaba wajen fama da talauci.

ADVERTISEMENT

An fitar da wannan bayanain ne, bisa wani sabon rahoto da wani Kamfanin yin bincike kan tattalin arziki na ADSR ya fitar a kan kasafin kudin na Gwamnatin Tarayya da kuma jihohi wanda duk dan Nijeriya daya, zai iya amfana wanda ya kai tsakanin daga dala 0.43 zuwa dala 0.21.

daukacin wannan adadin, ya kai kasa da daga kasa da dala 0.56 zuwa dala 0.36, sabainin na shekarar 2024.

LABARAI MASU NASABA

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

“An tsara kasafin kudin na Gwamnatin Tarayya da na jihohin da dan Nijeriya daya zai amfana, musamman saboda talaucin da kasar ke ciki, bai wuce kasa da dala 2.15,”. Inji masu fashin bakin.

Kazalika, rahoton ya sanar da cewa, wannan ya nuna cewa, kasafin kudin na Gwamnatin Tarayya da na jihohin, ba za su iya biyan bukatun ‘yan kasar ba, musamman kan abinda ya shafi samun abinci, kula da kiwon lafiya da kuma samun ilimin zamani.

Kasafin kudin na Gwamnatin da dan Nijeriya day zai iya amfana, ya kai Naira 235,706, wanda hakan ke nuna cewa, kowanne dan Nijeriya daya, a kullum, zai iya kashe Naira 645.8, musamman idna har, kasafin kudin ya isa ga daukacin ‘yan kasar.

Hakazalika, a matakin jihohi kuwa, kasafin kudin, kowanne dan Nijeriya daya, a cikin shekara daya, zai iya kashe Naira 115,500, inda kuma a rana daya, kasafin ya kai Naira 317.

“Gaba dayan kasafin kudin na kasa, idan an rabawa ‘yan kasar, kowanne mutum daya, a cikin shekara daya, zai samu Naira 348,481 a cikin kasafin kudin na 2025, amma a nan, ana nufin idan kowanne dan kasar daya, zai iya samun Naira 955 a kullum daga cikin kasafin kudin,”. Acewar rahoton.

Kasafin kudin na 2025 a kan duk dan Nijeriya daya, ya nuna nawa ne, yawan jarin da Gwamantin Tarayya ta zuba kan dan kasar daya kuma nawa ne, ta shirya za ta kashe a kan kowanne dan Nijeriya daya.

karin fashin baki kan kasafin kudin na kasar na 2025 da ADSR ta yi, ya nuna cewa, jimlarsa da aka amince ya kai Naira tiriliyan 81.3.

Wannan ya hada da na Gwamnatin Tarayya da ya kai Naira tiriliyan 54.99 da kuma na jihohi da ya kai Naira tiriliyan 26.30, wanda hakan ya nuna cewa, an samu karin da ya kai na kaso 51.9, idan aka kwatanta da na shekarar 2024.

Kazalika, kasafin kudin na Gwamnatin Tarayya ya karu zuwa kaso The 56.9, inda kuma na gwamnatocin jihohin kasar, ya karu da kaso 42.4, musamman idan aka kwatanta da shekarar 2024.

Shugaban kasa Bola Tinubu, ta hanyar majalisar kasa ya kara yawan adadin kasafin kudin na bana daga Naira tiriliyan 49.7 zuwa Naira tiriliyan 54.2.

Bola ya yi hakan ne, domin ya kara bunkasa kashe kudade a kan manyan ayyuka, musamman duba da dakatar da tallafin jin kai, da da kasar Amurka, ke bai wa Nijeriya.

Sai dai, masu fashin bakin sun nuna damuwar su kan cewa, karain sama da Naira biliyan 700 a cikin kasafin kudin na shekarar 2025 da gwamnatin shugaba Bola Tinubu ta yi, ba zai samar da wasu sauye-sauyen azo a gani ba a kan tattalin arzikin kasar, musamman duba da ci gaba da biyan kudin ruwa na dimbin bashin da ake ci gaba da bin Nijeriya.

Kudi
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

MASU ALAKA

2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa
Siyasa

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

June 22, 2026
Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
Siyasa

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

June 22, 2026
ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027
Siyasa

ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

June 21, 2026
Next Post
Nau’in Abinci Biyar Da Ke Lalata Hanta

Nau’in Abinci Biyar Da Ke Lalata Hanta

LABARAI MASU NASABA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.