• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Ba Ta Taba Mantawa Da Aminanta Kasashen Afirka Ba

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kasar Sin Ba Ta Taba Mantawa Da Aminanta Kasashen Afirka Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da shugabannin kasashe mambobin kungiyar G20 ke can suna tattauna batutuwa dake jan hankalin duniya, kamar farfadowar tattalin arzikin duniya da inganta tsarin kiwon lafiya da batun sauyin yanayi da sauya akala zuwa ga amfani da na’urori na zamani, har ma da batun samar da isasshen abinci da makamashi da makamantansu, a taron kungiyar dake zama na 17 a tsibirin Bali dake kasar Indonesia.

Kungiyar G20 da aka kafa a shekarar 1999, ta zama wani muhimmin dandalin hadin gwiwar kasashen duniya a fannin raya hada-hadar kudade da tattalin arziki. Kuma yanzu haka tana da kasashe mambobi 19 gami da kungiyar tarayyar Turai (EU).

  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Aike Da Sammaci Ga Wasu Jakadun Kasashen Turai Da Kungiyar EU Don Nuna Rashin Jin Dadinta

A yayin da bangarorin kasa da kasa ke fatan ganin manyan kasashe masu sukuni za su karfafa tsarin gudanarwa a fannin manufofin cudanyar bangaori daban-daban da kara bude kofa da tafiya tare da kowa da hadin gwiwar moriyar bai daya, shi kuwa shugaba Xi Jinping na kasar Sin, ya bayyana goyon bayan shigar da kungiyar Tarayyar Afirka (AU) ne a cikin kungiyar ta G20.

Wannan batu da shugaba Xi ya gabatar ya kara tabbatar da cewa, kasashen Sin da Afirka sun zama abin da Malam Bahaushe ke cewa, “’yan uwa rabin jiki”. Kuma a duk lokacin da bangaren Sin ya ga abin da zai shafi moriyar kasashen Afirka musamman kasashen masu tasowa, ya kan yi kokarin nusar da duniya bukatar kare muradunsu tare da mara musu baya, wajen ganin an cimma burin da ake fata, matakin dake kara jaddada sahihancin hadin gwiwar sassan biyu.

Sanin kowa ne cewa, kasashen duniya musamman masu tasowa, wanda kasashen Afirka ke ciki, suna fuskantar kalubale na koma bayan tattalin arziki. Wannan ne ma ya sa shugaba Xi ya gabatar da shawarar kafa dangantakar abokantakar neman farfado da tattalin arziki da dora muhimmanci ga aikin neman ci gaba da raya al’umma. Sabanin yadda wasu kasashe ke neman kafa kansa ba tare da la’akari da ragowar kasashe ba, wai kowa ya kar kifi gorarsa. Shi kuwa shugaba Xi, cewa ya yi, ya dace irin wadannan kasashe su taimakawa sauran kasashe, da ba su karin damammakin da suke bukata. Wato ka so wa dan uwanka, abin da kake so a kanka.

Labarai Masu Nasaba

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Baya ga kayayyakin more rayuwa da kasashen Afirka suka amfana da su karkashin hadin gwiwar sassan biyu, wato Sin da Afirka. Daga lokaci zuwa lokaci ko dai a taruka ko dandalolin kasa da kasa, bangaren Sin kan yi kokarin kare muradun kasashe masu tasowa baki daya. Kasar Sin ba ta taba mantawa da aminanta kasashe Afirka ba. Abin da ke kara tabbatar da sahihancin alakar sassan biyu. (Ibrahim Yaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

ASUU: Gwamnati Ta Kafe Kan Kudurinta Kan Malaman Jami’o’i Na ‘Ba Aiki Ba Biyan Albashi’

Next Post

Sin Za Ta Ci Gaba Da Hada Hannu Da Mambobin G20 Game Da Tsarin Tattalin Arziki Na Zamani

Related

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

16 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

17 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

19 hours ago
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

22 hours ago
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

23 hours ago
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

1 day ago
Next Post
Sin Za Ta Ci Gaba Da Hada Hannu Da Mambobin G20 Game Da Tsarin Tattalin Arziki Na Zamani

Sin Za Ta Ci Gaba Da Hada Hannu Da Mambobin G20 Game Da Tsarin Tattalin Arziki Na Zamani

LABARAI MASU NASABA

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Afirka

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.