• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Ba Ta Taba Mantawa Da Aminanta Kasashen Afirka Ba

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kasar Sin Ba Ta Taba Mantawa Da Aminanta Kasashen Afirka Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da shugabannin kasashe mambobin kungiyar G20 ke can suna tattauna batutuwa dake jan hankalin duniya, kamar farfadowar tattalin arzikin duniya da inganta tsarin kiwon lafiya da batun sauyin yanayi da sauya akala zuwa ga amfani da na’urori na zamani, har ma da batun samar da isasshen abinci da makamashi da makamantansu, a taron kungiyar dake zama na 17 a tsibirin Bali dake kasar Indonesia.

Kungiyar G20 da aka kafa a shekarar 1999, ta zama wani muhimmin dandalin hadin gwiwar kasashen duniya a fannin raya hada-hadar kudade da tattalin arziki. Kuma yanzu haka tana da kasashe mambobi 19 gami da kungiyar tarayyar Turai (EU).

  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Aike Da Sammaci Ga Wasu Jakadun Kasashen Turai Da Kungiyar EU Don Nuna Rashin Jin Dadinta

A yayin da bangarorin kasa da kasa ke fatan ganin manyan kasashe masu sukuni za su karfafa tsarin gudanarwa a fannin manufofin cudanyar bangaori daban-daban da kara bude kofa da tafiya tare da kowa da hadin gwiwar moriyar bai daya, shi kuwa shugaba Xi Jinping na kasar Sin, ya bayyana goyon bayan shigar da kungiyar Tarayyar Afirka (AU) ne a cikin kungiyar ta G20.

Wannan batu da shugaba Xi ya gabatar ya kara tabbatar da cewa, kasashen Sin da Afirka sun zama abin da Malam Bahaushe ke cewa, “’yan uwa rabin jiki”. Kuma a duk lokacin da bangaren Sin ya ga abin da zai shafi moriyar kasashen Afirka musamman kasashen masu tasowa, ya kan yi kokarin nusar da duniya bukatar kare muradunsu tare da mara musu baya, wajen ganin an cimma burin da ake fata, matakin dake kara jaddada sahihancin hadin gwiwar sassan biyu.

Sanin kowa ne cewa, kasashen duniya musamman masu tasowa, wanda kasashen Afirka ke ciki, suna fuskantar kalubale na koma bayan tattalin arziki. Wannan ne ma ya sa shugaba Xi ya gabatar da shawarar kafa dangantakar abokantakar neman farfado da tattalin arziki da dora muhimmanci ga aikin neman ci gaba da raya al’umma. Sabanin yadda wasu kasashe ke neman kafa kansa ba tare da la’akari da ragowar kasashe ba, wai kowa ya kar kifi gorarsa. Shi kuwa shugaba Xi, cewa ya yi, ya dace irin wadannan kasashe su taimakawa sauran kasashe, da ba su karin damammakin da suke bukata. Wato ka so wa dan uwanka, abin da kake so a kanka.

Labarai Masu Nasaba

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Baya ga kayayyakin more rayuwa da kasashen Afirka suka amfana da su karkashin hadin gwiwar sassan biyu, wato Sin da Afirka. Daga lokaci zuwa lokaci ko dai a taruka ko dandalolin kasa da kasa, bangaren Sin kan yi kokarin kare muradun kasashe masu tasowa baki daya. Kasar Sin ba ta taba mantawa da aminanta kasashe Afirka ba. Abin da ke kara tabbatar da sahihancin alakar sassan biyu. (Ibrahim Yaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

ASUU: Gwamnati Ta Kafe Kan Kudurinta Kan Malaman Jami’o’i Na ‘Ba Aiki Ba Biyan Albashi’

Next Post

Sin Za Ta Ci Gaba Da Hada Hannu Da Mambobin G20 Game Da Tsarin Tattalin Arziki Na Zamani

Related

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama
Daga Birnin Sin

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

16 hours ago
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14
Daga Birnin Sin

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

17 hours ago
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12
Daga Birnin Sin

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

18 hours ago
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana
Daga Birnin Sin

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

19 hours ago
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

20 hours ago
Manyan Jami’an JKS Sun Ziyarci Jami’ai Da Mazauna Birnin Lhasa
Daga Birnin Sin

Manyan Jami’an JKS Sun Ziyarci Jami’ai Da Mazauna Birnin Lhasa

21 hours ago
Next Post
Sin Za Ta Ci Gaba Da Hada Hannu Da Mambobin G20 Game Da Tsarin Tattalin Arziki Na Zamani

Sin Za Ta Ci Gaba Da Hada Hannu Da Mambobin G20 Game Da Tsarin Tattalin Arziki Na Zamani

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

August 23, 2025
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

August 23, 2025
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

August 23, 2025
Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

August 23, 2025
Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

August 23, 2025
Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga

Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Kama Waɗanda Suka Kashe Masallata A Malumfashi 

August 23, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

August 23, 2025
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

August 23, 2025
2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

August 23, 2025
Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.