ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Ba Ta Taba Mantawa Da Aminanta Kasashen Afirka Ba

by CMG Hausa
4 years ago
Afirka

Yayin da shugabannin kasashe mambobin kungiyar G20 ke can suna tattauna batutuwa dake jan hankalin duniya, kamar farfadowar tattalin arzikin duniya da inganta tsarin kiwon lafiya da batun sauyin yanayi da sauya akala zuwa ga amfani da na’urori na zamani, har ma da batun samar da isasshen abinci da makamashi da makamantansu, a taron kungiyar dake zama na 17 a tsibirin Bali dake kasar Indonesia.

Kungiyar G20 da aka kafa a shekarar 1999, ta zama wani muhimmin dandalin hadin gwiwar kasashen duniya a fannin raya hada-hadar kudade da tattalin arziki. Kuma yanzu haka tana da kasashe mambobi 19 gami da kungiyar tarayyar Turai (EU).

  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Aike Da Sammaci Ga Wasu Jakadun Kasashen Turai Da Kungiyar EU Don Nuna Rashin Jin Dadinta

A yayin da bangarorin kasa da kasa ke fatan ganin manyan kasashe masu sukuni za su karfafa tsarin gudanarwa a fannin manufofin cudanyar bangaori daban-daban da kara bude kofa da tafiya tare da kowa da hadin gwiwar moriyar bai daya, shi kuwa shugaba Xi Jinping na kasar Sin, ya bayyana goyon bayan shigar da kungiyar Tarayyar Afirka (AU) ne a cikin kungiyar ta G20.

ADVERTISEMENT

Wannan batu da shugaba Xi ya gabatar ya kara tabbatar da cewa, kasashen Sin da Afirka sun zama abin da Malam Bahaushe ke cewa, “’yan uwa rabin jiki”. Kuma a duk lokacin da bangaren Sin ya ga abin da zai shafi moriyar kasashen Afirka musamman kasashen masu tasowa, ya kan yi kokarin nusar da duniya bukatar kare muradunsu tare da mara musu baya, wajen ganin an cimma burin da ake fata, matakin dake kara jaddada sahihancin hadin gwiwar sassan biyu.

Sanin kowa ne cewa, kasashen duniya musamman masu tasowa, wanda kasashen Afirka ke ciki, suna fuskantar kalubale na koma bayan tattalin arziki. Wannan ne ma ya sa shugaba Xi ya gabatar da shawarar kafa dangantakar abokantakar neman farfado da tattalin arziki da dora muhimmanci ga aikin neman ci gaba da raya al’umma. Sabanin yadda wasu kasashe ke neman kafa kansa ba tare da la’akari da ragowar kasashe ba, wai kowa ya kar kifi gorarsa. Shi kuwa shugaba Xi, cewa ya yi, ya dace irin wadannan kasashe su taimakawa sauran kasashe, da ba su karin damammakin da suke bukata. Wato ka so wa dan uwanka, abin da kake so a kanka.

LABARAI MASU NASABA

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

Baya ga kayayyakin more rayuwa da kasashen Afirka suka amfana da su karkashin hadin gwiwar sassan biyu, wato Sin da Afirka. Daga lokaci zuwa lokaci ko dai a taruka ko dandalolin kasa da kasa, bangaren Sin kan yi kokarin kare muradun kasashe masu tasowa baki daya. Kasar Sin ba ta taba mantawa da aminanta kasashe Afirka ba. Abin da ke kara tabbatar da sahihancin alakar sassan biyu. (Ibrahim Yaya)

Afirka
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya
Daga Birnin Sin

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari
Daga Birnin Sin

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 14, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
Next Post
Sin Za Ta Ci Gaba Da Hada Hannu Da Mambobin G20 Game Da Tsarin Tattalin Arziki Na Zamani

Sin Za Ta Ci Gaba Da Hada Hannu Da Mambobin G20 Game Da Tsarin Tattalin Arziki Na Zamani

LABARAI MASU NASABA

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

June 14, 2026
Gwamnati Ba Za Ta Saki ’Yan Ta’adda Ba Duk Da Kisan Tsohon Kakakin DHQ — Tinubu

Gwamnati Ba Za Ta Saki ’Yan Ta’adda Ba Duk Da Kisan Tsohon Kakakin DHQ — Tinubu

June 14, 2026
Yadda Ake Wainar Masara Da Miyar Yaji

Yadda Ake Wainar Masara Da Miyar Yaji

June 14, 2026
Hanyoyin Hada Humra Mai Kamshi

Hanyoyin Hada Humra Mai Kamshi

June 14, 2026
Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026
Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 14, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.