• English
  • Business News
Saturday, July 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Na Goyon Bayan Siriya Wajen Lalubo Hanyar Sake Gina Kasar Ta Hanyar Tattaunawa Da Bangarorin Da Abin Ya Shafa

by CGTN Hausa and Sulaiman
7 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Kasar Sin Na Goyon Bayan Siriya Wajen Lalubo Hanyar Sake Gina Kasar Ta Hanyar Tattaunawa Da Bangarorin Da Abin Ya Shafa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya bayyana a yau Jumma’a cewa, kasarsa tana goyon bayan Siriya wajen tabbatar da zaman lafiya tun da wuri, kuma tana goyon bayan kasar wajen samar da shirin sake gina kasar, da zai dace da muradun al’ummar kasar ta hanyar tattaunawa da bangarorin da abin ya shafa. 

 

Wang ya bayyana hakan ne a lokacin da aka yi masa tambaya game da ra’ayin kasar Sin kan halin da ake ciki a kasar Siriya, yayin wani taron manema labarai na hadin gwiwa tare da ministan harkokin wajen Masar Badr Abdelatty, bayan tattaunawarsu kan manyan tsare-tsare na Sin da Masar a Beijing.

  • Xi Ya Gabatar Da Muhimmin Jawabi A Babban Taron Ayyukan Tattalin Arziki Na Tsakiya
  • Tinubu Zai Gabatar Da Kasafin Kuɗin 2025 Da Ya Kai ₦47.9trn

Wang ya kara da cewa, kamata ya yi a nan gaba kasar Siriya ta yi tsayin daka wajen nuna adawa da duk wani nau’in ta’addanci da masu tsattsauran ra’ayi. Kuma a halin da ake ciki, ya kamata kasashen duniya su kiyaye ’yancin kan Siriya da cikakken yankinta, da mutunta al’adunta na gargajiya da addini, tare da baiwa al’ummar kasar damar yanke shawarwari bisa kashin kansu.

 

Labarai Masu Nasaba

In Sin Da Turai Sun Yi Hadin Gwiwa, Duniya Ba Za Ta Tsunduma Cikin Yanayi Na Hargitsi Ba

Sin Za Ta Gaggauta Aikin Raya Sana’o’in Samar Da Wutar Lantarki Daga Zafin Rana

Wang ya kuma yi karin haske kan matsayin kasar Sin game da tashe-tashen hankula a yankin gabas ta tsakiya. Yana mai cewa babban aikin da aka sanya gaba shi ne tsagaita bude wuta nan da nan, da dakatar da tashin hankali, da sassauta matsalar jin kai. Kana babbar hanyar samar da mafita ita ce sasantawa ta hanyar siyasa da sake dawo da shawarwari da tattaunawa, kuma muhimmiyar ka’idar ita ce goyon bayan ’yancin kai da kauce wa tsoma baki daga waje.

 

A ranar 13 ga wata ne Wang Yi, ya jagoranci taron tattaunawa kan manyan tsare-tsare na ministocin harkokin wajen Sin da Masar tare da Badr Abdelatty a birnin Beijing, inda ya bayyana cewa, kasar Sin a shirye take ta karfafa tuntubar juna da hadin gwiwa bisa manyan tsare-tsare da kasar Masar, don ba da gudummawa tare wajen kiyaye zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin, da sa kaimi ga ci gaban duniya baki daya. (Mohammed Yahaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Yi Watsi Da Ƙara A Kan LEADERSHIP

Next Post

Da Ɗumi-dumi: Sakataren Gwamnatin Bauchi Ya Yi Murabus

Related

In Sin Da Turai Sun Yi Hadin Gwiwa, Duniya Ba Za Ta Tsunduma Cikin Yanayi Na Hargitsi Ba
Daga Birnin Sin

In Sin Da Turai Sun Yi Hadin Gwiwa, Duniya Ba Za Ta Tsunduma Cikin Yanayi Na Hargitsi Ba

12 hours ago
Sin Za Ta Gaggauta Aikin Raya Sana’o’in Samar Da Wutar Lantarki Daga Zafin Rana
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Gaggauta Aikin Raya Sana’o’in Samar Da Wutar Lantarki Daga Zafin Rana

12 hours ago
Shugaban Kwamitin AU: Kasar Sin Aminiya Ce Da Za A Iya Dogaro Da Ita
Daga Birnin Sin

Shugaban Kwamitin AU: Kasar Sin Aminiya Ce Da Za A Iya Dogaro Da Ita

13 hours ago
Ma’aikatar Cinikayya Ta Sin Ta Yi Karin Haske Game Da Soke Takunkumin Da Amurka Ta Kakabawa Sin
Daga Birnin Sin

Ma’aikatar Cinikayya Ta Sin Ta Yi Karin Haske Game Da Soke Takunkumin Da Amurka Ta Kakabawa Sin

14 hours ago
Sin Da Ghana Za Su Karfafa Hadin Gwiwarsu
Daga Birnin Sin

Sin Da Ghana Za Su Karfafa Hadin Gwiwarsu

15 hours ago
Sin: Tsawaitar Rikicin Ukraine Ba Zai Amfani Kowa Ba
Daga Birnin Sin

Sin: Tsawaitar Rikicin Ukraine Ba Zai Amfani Kowa Ba

16 hours ago
Next Post
Da Ɗumi-dumi: Sakataren Gwamnatin Bauchi Ya Yi Murabus

Da Ɗumi-dumi: Sakataren Gwamnatin Bauchi Ya Yi Murabus

LABARAI MASU NASABA

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

July 5, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

July 5, 2025
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

July 5, 2025
Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya

Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya

July 5, 2025
Tinubu Ya Kaddamar Da Sabon Shirin Aikin Noma Don Samar Da Wadataccen Abinci

Tinubu Ya Kaddamar Da Sabon Shirin Aikin Noma Don Samar Da Wadataccen Abinci

July 5, 2025
Abin Da Ya Sa ‘Yan Nijeriya Ba Su Mori Dimokuradiyya Ba Har Yanzu –Jega

Shirin Tinubu Kan Kiwon Dabbobi Zai Samar Da Ayyukan Yi Miliyan 5 Ga Matasa – Jega

July 5, 2025
Ana Tuhumar Tsohon Ɗan Wasan Arsenal Thomas Partey Da Laifin Fyaɗe A Ƙasar Ingila

Ana Tuhumar Tsohon Ɗan Wasan Arsenal Thomas Partey Da Laifin Fyaɗe A Ƙasar Ingila

July 5, 2025
‘Yan Kasuwa Na Kalubalantar Rage Faranshin Man Dangote

‘Yan Kasuwa Na Kalubalantar Rage Faranshin Man Dangote

July 5, 2025
In Sin Da Turai Sun Yi Hadin Gwiwa, Duniya Ba Za Ta Tsunduma Cikin Yanayi Na Hargitsi Ba

In Sin Da Turai Sun Yi Hadin Gwiwa, Duniya Ba Za Ta Tsunduma Cikin Yanayi Na Hargitsi Ba

July 4, 2025
Sin Za Ta Gaggauta Aikin Raya Sana’o’in Samar Da Wutar Lantarki Daga Zafin Rana

Sin Za Ta Gaggauta Aikin Raya Sana’o’in Samar Da Wutar Lantarki Daga Zafin Rana

July 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.