ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

by Sulaiman and CGTN Hausa
12 months ago
Amurka

Tun bayan komawa sabon zagaye na tattaunawar tattalin arziki da cinikayya tsakanin wakilan Sin da na Amurka a birnin Madrid na Sifaniya a karshen makon jiya, masharhanta da dama ke bayyana mahangarsu game da matsayar Sin dangane da zaman tattaunawar.

A mahangar da dama daga masu fashin baki, yayin zama na wannan karo ma kasar Sin za ta kara jaddada matsayinta na mai burin kare halastattun hakkokinta, da martaba tsarin cudanyar mabanbantan sassan duniya, tare da bukatar Amurka ta amince da gudanar da shawarwari bisa daidaito, da martaba juna, da dakile sabani, da karfafa hadin gwiwa, da hada hannu wajen bunkasa hada-hadar tattalin arziki ba tare da rufa-rufa ba.

Ko shakka babu alakar tattalin arziki da cinikayya dake tsakanin Sin da Amurka ta cimma moriyar juna ce. Don haka ne ma karkashin kudurorin da shugabannin kasashen biyu suka cimma, a baya tawagogin tattaunawa na Sin da Amurka, suka gudanar da zagaye uku na tattaunawa a Geneva, da Landan, da Stockholm, inda suka cimma sakamako mai gamsarwa da ya taka rawar gani wajen daidaita alakar kasashen biyu.

ADVERTISEMENT

Tabbas, muhimmancin alakar cinikayya tsakanin Sin da Amurka ta zarge batun cimma gajiyarsu su kadai, domin kuwa hakan na shafar daidaiton tattalin arzikin duniya baki daya. A bangarenta, kasar Sin na ta kokarin sauke nauyin dake wuyanta a fannin warware sabani, da kaucewa fito-na-fito ta hanyar karfafa hadin gwiwa.

Baya ga kasar Sin, sauran sassan kasa da kasa ma suna nuna gamsuwa da nasarorin da ake samu, dangane da shawarwarin da sassan biyu ke gudanarwa. Suna kuma karfafa wa sassan biyu gwiwar ci gaba da shawarwari, ta yadda za su karfafa daidaito a fannin jagorancin hada-hadar cinikayya a matakin kasa da kasa.

LABARAI MASU NASABA

Nazarin CGTN: Dole Ne Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Samar Da Tsaro Mai Dorewa

Mataimakin Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Taron Dandalin Xiangshan Da Ake Gudanarwa Kan Sha’anin Tsaro A Beijing

Har kullum, Sin za ta ci gaba da martaba ka’idojin kare hakkokin kamfanoninta. Duba da cewa manhajar TikTok ta shafe tsawon shekaru tana aiki a Amurka, ta kuma samar da dumbin ayyukan yi ga tarin Amurkawa, tare da bayar da gudummawa ga tattalin arzikin kasar, ya kamata gwamnatin kasar ta baiwa manhajar damar cin gajiya daidai da sauran makamantanta dake kasar. Kamar dai ko da yaushe, burin Sin shi ne wanzar da daidaito da cimma moriyar bai daya tare da Amurka.

 

 

Amurka
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Marafa Ya Yi Alƙawarin Murabus Idan Ya Kasa Magance Tsaro Cikin Shekaru Biyu
  • Sulaiman
    Hisbah Ta Cika Hannu Da Fitaccen Ɗan TikTok A Kano Kan Bidiyoyin Rashin Da’a
  • Sulaiman
    Tinubu Zai Shiga Tsakani A Rikicin Wike Da Gwamnonin APC
  • Sulaiman
    ’Yansanda Sun Ceto Mutane, Sun Daƙile Harin ’Yan Bindiga A Katsina
Amurka
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Manufar Sin Kan Raba Fasahar AI Ga Saura: Hakika Mai Bayarwa Ba Ya Rasawa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Fitar Da Ka’idojin Na’urar Kiwon Lafiya Ta Sadarwa Tsakanin Kwakwalwa Da Na’ura Mai Amfani Da AI
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Rokar Gravity-1 Na Kasar Sin Ya Harba Sabbin Taurarin Dan’adam Daga Teku
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Ya Taya Jami’ar Jilin Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa

MASU ALAKA

Nazarin CGTN: Dole Ne Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Samar Da Tsaro Mai Dorewa
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Dole Ne Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Samar Da Tsaro Mai Dorewa

September 16, 2026
Mataimakin Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Taron Dandalin Xiangshan Da Ake Gudanarwa Kan Sha’anin Tsaro A Beijing
Daga Birnin Sin

Mataimakin Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Taron Dandalin Xiangshan Da Ake Gudanarwa Kan Sha’anin Tsaro A Beijing

September 16, 2026
Lee Ka Chiu: Shirin Shekaru 5 Na Farko Na Raya Yankin Musamman Na Hong Kong Ya Dace Da Muradun Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Lee Ka Chiu: Shirin Shekaru 5 Na Farko Na Raya Yankin Musamman Na Hong Kong Ya Dace Da Muradun Kasar Sin

September 16, 2026
Next Post
‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

'Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma'adinai Ba Bisa Ƙa'ida Ba A Neja

LABARAI MASU NASABA

Marafa Ya Yi Alƙawarin Murabus Idan Ya Kasa Magance Tsaro Cikin Shekaru Biyu

Marafa Ya Yi Alƙawarin Murabus Idan Ya Kasa Magance Tsaro Cikin Shekaru Biyu

September 17, 2026
An Ci TikTok Tarar Fam Miliyan £12.7 Kan Karya Dokar Kananan Yara A Burtaniya

Hisbah Ta Cika Hannu Da Fitaccen Ɗan TikTok A Kano Kan Bidiyoyin Rashin Da’a

September 17, 2026
Tinubu Zai Shiga Tsakani A Rikicin Wike Da Gwamnonin APC

Tinubu Zai Shiga Tsakani A Rikicin Wike Da Gwamnonin APC

September 17, 2026
Kawayen amarya

’Yansanda Sun Ceto Mutane, Sun Daƙile Harin ’Yan Bindiga A Katsina

September 17, 2026
Aisha Buhari Ta Ziyarci Atiku

Aisha Buhari Ta Ziyarci Atiku

September 17, 2026
Nazarin CGTN: Dole Ne Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Samar Da Tsaro Mai Dorewa

Nazarin CGTN: Dole Ne Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Samar Da Tsaro Mai Dorewa

September 16, 2026
Haɓaka Tattalin Arzikin Zamfara: Gwamna Lawal Zai Halarci Babban Taron MDD A New York

Haɓaka Tattalin Arzikin Zamfara: Gwamna Lawal Zai Halarci Babban Taron MDD A New York

September 16, 2026
Mataimakin Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Taron Dandalin Xiangshan Da Ake Gudanarwa Kan Sha’anin Tsaro A Beijing

Mataimakin Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Taron Dandalin Xiangshan Da Ake Gudanarwa Kan Sha’anin Tsaro A Beijing

September 16, 2026
Wani Mai Taɓin Ƙwaƙwalwa Ya Kashe Soja A Legas

Sojoji Sun Hallaka Wani Jagoran ’Yan Ta’adda A Katsina

September 16, 2026
Lee Ka Chiu: Shirin Shekaru 5 Na Farko Na Raya Yankin Musamman Na Hong Kong Ya Dace Da Muradun Kasar Sin

Lee Ka Chiu: Shirin Shekaru 5 Na Farko Na Raya Yankin Musamman Na Hong Kong Ya Dace Da Muradun Kasar Sin

September 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.