ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Na Neman Ci Gaba Ta Hanyar Lumana Domin Amfanin Daukacin Bil Adama

by CMG Hausa
3 years ago
Kasar Sin

A yayin taron wakilan jamiyyar kwaminis ta kasar Sin JKS karo na 20 da ya gabata cikin shekarar da ta shude, shugaban kasar Xi Jinping ya taba alli game da yadda JKS ta shafe gwamman shekaru tun kafuwarta, tana aiki tukuru wajen tabbatar da nasarar bunkasa kasa ta hanyar lumana, da ingiza ci gaban rayuwar daukacin alummun duniya.

Ko shakka babu, ga duk mai bibiyar tarihi, ya kwana da sanin cewa, tashe-tashen hankula da yake-yake, ko zaman doya da man ja, wadanda suka wakana tsakanin kasashe daban daban, ba su taba haifar da da mai ido ba. Don haka ne ma shaidun gani da ido, ke dada tabbatar da muradun kasar Sin na bin hanyoyin zaman lafiya domin samun ci gaba, wanda hakan ya zama babban jigo a manufofin diflomasiyyar kasar.

  • Wang Yi Ya Jagoranci Taron Manyan Wakilai Game Da Nazarin Matakan Aiwatar Da Manufofin Taron Ministocin FOCAC Na 8

A mahangar kasar Sin, zaman lafiya da ci gaba, tamkar dan juma ne da dan jummai, wato dai muhimman tagwaye ne da ba za a iya raba su ba, don haka mahukuntan kasar ke kara kaimi ga dukkanin hanyoyin raya dangantaka da sauran sassan duniya cikin lumana. Alal misali, Sin ta gabatarwa duniya da shawarar nan ta “ziri daya da hanya daya”, da dandalin raya hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka na FOCAC, ta kuma fadada jarin waje da take zubawa a kasashen Afirka, domin tallafa musu wajen bunkasa tattalin arzikinsu. Wadannan da ma karin wasu manufofin na samar da gata ga kasashe masu tasowa, sun sa akasarin sassan kasa da kasa na kallon kasar Sin a matsayin babbar kawa, kuma aminiyar huldar kasashe masu tasowa, musamman a fannonin samar da ababen more rayuwa, da cinikayya, da zuba jari da hadin gwiwar raya sassan tattalin arziki.

ADVERTISEMENT

Bugu da kari, kasar Sin na goyon bayan gudanar da cudanyar dukkanin sassan kasa da kasa, da hada-hadar cinikayya maras shinge, da tsaron kasa da kasa, da ayyukan wanzar da zaman lafiya. Tana kuma kaucewa yin mummunar takara ko neman yin babakere, sabanin yadda wasu manyan kasashe musamman na yammacin duniya ke nacewa hakan.

Ko shakka babu, manufofin kasar Sin na wanzar da ci gaba ta hanyar lumana domin cin gajiyar daukacin bil adama, za su ci gaba da haifar da gajiya da dukkanin sassan kasa da kasa, ta yadda za a gudu tare a tsira tare. (Saminu Hassan)

LABARAI MASU NASABA

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara
Daga Birnin Sin

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka
Daga Birnin Sin

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025
Next Post
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

'Yansanda Sun Kashe 'Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 2 A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.