• English
  • Business News
Tuesday, May 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Na Nuna Sahihanci Ga Kasashen Afirka

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kasar Sin Na Nuna Sahihanci Ga Kasashen Afirka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Idan wani abokinka yana zuwa gidanka don gaishe ka, da nuna fatan alheri a farkon duk wata sabuwar shekara, cikin shekaru 33 a jere. Shin kauna da sahihanci da ya nuna maka za su burge ka?

A kwanan baya, ministan harkokin wajen kasar Sin Qin Gang ya yi ziyara a kasashen Habasha, da Gabon, da Angola, da Benin, gami da Masar, wadda ta kasance ziyara ta farko da jami’in ya yi, bayan da ya hau mukamin ministan wajen kasar Sin. Kana ya zama shekaru 33 a jere, da ministan waje na kasar Sin ya kai ziyara a nahiyar Afirka a farkon duk shekara. Hakan ya shaida dadadden zumuncin da ake da shi tsakanin kasar Sin da kasashen Afirka, da sahihancin da kasar Sin ta nuna ma abokanta dake nahiyar Afirka.

Wannan sahihanci, shi ne tushen hadin gwiwar Sin da Afirka, wanda ya tabbatar da yanayin hadin gwiwa na amfanar da juna, da haifar da ci gaba ga dukkan bangarorin kasashen Afirka da kasar Sin:

Tun daga shekarar 2000, kasar Sin ta gina layin dogo fiye da kilomita 6000, da hanyoyin mota na kilomita 6000, da tashoshin jiragen ruwa kimanin 20, da manyan tashoshin samar da wutar lantarki fiye da 80, a kasashen Afirka. Gami da ba da tallafin asibitoci fiye da 130, da makarantu fiye da 170, da dakunan wasannin motsa jiki 45, da ayyukan aikin gona fiye da 500 a nahiyar Afirka.

Kaza lika a kasuwannin kasar Sin, yanzu ana iya ganin gahawa, da kayayyakin hannu, da dai sauransu, wadanda aka samar da su a kasashen Afirka, wadanda suka taimakawa inganta zaman rayuwar Sinawa.

Labarai Masu Nasaba

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Taro Na 4 Na Ministocin Dandalin CCF 

Kasar Sin Ta Fitar Da Tambarin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Murkushe Harin Japan

Yayin da minista Qin Gang ke ziyara a kasar Habasha a wannan karo, ya halarci bikin kammala ginin babbar cibiyar hana yaduwar cututtuka ta nahiyar Afirka. Wannan aiki shi ma ya shaida sahihancin da kasar Sin ta nuna ma kasashen Afirka.

Yayin barkewar annobar cutar Ebola a yammacin Afirka a shekarar 2014 ma, kasar Sin ta samar da tallafi ga kasashen da annobar ta shafa, da kungiyar kasashen Afirka ta AU, ba tare da jinkiri ba. Daga baya kuma, Sin ta sanar da samar da gudummawar gina ginin babbar hedkwatar cibiyar hana yaduwar cututtuka ta nahiyar Afirka kyauta, don tallafawa kokarin kasashen nahiyar na kare lafiyar jama’arsu.

Yanzu hakan dai an mika wa kungiyar AU, manyan bangarori na wannan babban gini wanda fadinsa ya kai muraba’in mita dubu 90, wanda aka kashe dalar Amurka miliyan 80 wajen gina shi. Wannan babbar kyauta ta nuna yadda kasar Sin take samar wa kasashen Afirka da hakikanin taimakon da ake bukata, ba tare da gindaya wani sharadi ba. Kana duk wani alkawarin da kasar Sin ta yi, to, za ta cika shi.

Ban da wannan kuma, ana iya ganin sahihancin da kasar Sin ta nuna, bisa yadda ta ki yarda da yunkurin siyasantar da batun hadin gwiwa da kasashen Afirka. A lokacin da yake hira da manema labaru, tare da shugaban kwamitin kungiyar AU Moussa Faki Mahamat, Mista Qin Gang ya ce, “Afirka dandali ne na hadin gwiwar kasa da kasa, maimakon fagen takarar manyan kasashe. Idan dole ne a yi takara, to, ya dace a duba wace kasa ta fi samar da gudunmowa ga kokarin tabbatar da zaman lafiya da ci gaba a nahiyar Afirka, gami da taimakawa kasashen Afirka, samun karin wakilci da ikon fada a ji a fannin kula da al’amuran kasa da kasa. ” A cewarsa, duk wata kasa, idan ta nuna sahihanci, na tabbatar da samun zaman lafiya da ci gaban tattalin arziki a nahiyar Afirka, to, kasar Sin za ta mara mata baya.

Hakika kokarin hadin gwiwa da kasashen Afirka da kasar Sin take yi, ya riga ya janyo karin jari zuwa nahiyar Afirka, daga kasashen yamma. Yayin da wani masani dan Najeriya mai suna Ovigwe Eguegu ke hira da manema labaru a kwanan baya, ya ce, manyan shirye-shiryen zuba jari na “Huldar abokai ta gina kayayyakin more rayuwa da zuba jari ko (PGII)” na kungiyar G7, da shirin “Kofofin duniya” (Global Gateway) na kungiyar tarayyar Turai na EU, an gabatar da su ne, bayan da aka ga yadda shirin “Ziri daya da hanya daya ko (B&R)” na kasar Sin ke yin muhimmin tasiri a duniya.

Sai dai kasashen yamma sun ki yarda da sahihancin kasar Sin, har ma kafofin watsa labarun su na cewa wai kasar Sin, ta jefa kasashen Afirka cikin “tarkon bashi”. Dangane da wannan zargi, Mista Qin Gang ya mayar da martani ta hakikanan bayanai.

A cewarsa, kasar Sin ta yi kokarin halartar shirin dakatar da biyan bashi karkashin laimar kungiyar G20, inda ta kulla yarjejeniya, ko kuma cimma ra’ayi tare da kasashe 19 dake nahiyar Afirka, a fannin dakatar da biyan bashi, lamarin da ya sanya kasar zama mafi samar da sakamako a wannan fanni, cikin mambobin kungiyar G20.

A sa’i daya kuma, wani rahoto daga bankin duniya ya nuna cewa, hukumomin hada-hadar kudi na kasa da kasa, da ‘yan kasuwa masu ba da bashi, suna rike da kashi 3 cikin kashi 4 na dukkan bashin da ake bin kasashen Afirka. Saboda haka Mista Qin ya bukaci wadannan hukumomi, da mutane da su kara taka rawa a fannin sassauta matsalar bashi a kasashen Afirka.

Hakika dalilin da ya sa kasashen yamma ba za su yarda da sahihanci na kasar Sin ba, shi ne domin akwai bambancin ra’ayi tsakaninsu. A ganin mutanen kasashen yamma, moriyar kai ta fi muhimmanci, amma tunanin da kasar Sin ta daukaka shi ne, kafa al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makoma ta bai daya. A ganin Sinawa, wasu manyan matsaloli sun shafi duniya baki daya, kana babu wata kasa da za ta iya kare kai, ba tare da hadin gwiwa da sauran kasashe ba. Saboda haka, ya kamata a lura da damuwar sauran kasashe, yayin da ake neman tabbatar da moriyar wata kasa, gami da ciyar da tattalin arzikin kasashe daban daban gaba, yayin da ake neman raya kai.

Wannan tunani shi ne ainihin dalilin da ya sa kasar Sin ke ta nuna cikakken sahihanci ga abokanta dake nahiyar Afirka. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Burina

Next Post

A Boye DSS Ta Ayyana Cafko Emefiele – Femi Falana

Related

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Taro Na 4 Na Ministocin Dandalin CCF 
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Taro Na 4 Na Ministocin Dandalin CCF 

2 hours ago
Kasar Sin Ta Fitar Da Tambarin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Murkushe Harin Japan
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Fitar Da Tambarin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Murkushe Harin Japan

2 hours ago
Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Da Ake Iya Sarrafawa Daga Nesa
Daga Birnin Sin

Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Da Ake Iya Sarrafawa Daga Nesa

18 hours ago
He Lifeng Ya Gana Da Babbar Jami’ar WTO Ngozi Okonjo-Iweala
Daga Birnin Sin

He Lifeng Ya Gana Da Babbar Jami’ar WTO Ngozi Okonjo-Iweala

20 hours ago
Ma’aikatar Kasuwanci: Sanarwar Da Sin Da Amurka Suka Fitar Muhimmin Mataki Ne Na Warware Sabaninsu
Daga Birnin Sin

Ma’aikatar Kasuwanci: Sanarwar Da Sin Da Amurka Suka Fitar Muhimmin Mataki Ne Na Warware Sabaninsu

21 hours ago
Nazarin CGTN: Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Latin Amurka Na Kara Samun Karbuwa Tsakanin Jama’a
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Latin Amurka Na Kara Samun Karbuwa Tsakanin Jama’a

23 hours ago
Next Post
Emefiele: Duk Mai Tunanin Sauro Ya Yi Kadan Bai Kwana Da Shi Ba Ne!

A Boye DSS Ta Ayyana Cafko Emefiele - Femi Falana

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

Gwamna Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

May 13, 2025
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Taro Na 4 Na Ministocin Dandalin CCF 

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Taro Na 4 Na Ministocin Dandalin CCF 

May 13, 2025
Kasar Sin Ta Fitar Da Tambarin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Murkushe Harin Japan

Kasar Sin Ta Fitar Da Tambarin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Murkushe Harin Japan

May 13, 2025
Wata Mata Ta Kashe Dan Hayar Da Ke Gidanta A Ondo

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban APC A Ondo, Sun Nemi N100m

May 13, 2025
Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya Gargaɗi Magoya Bayansa

Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya Gargaɗi Magoya Bayansa

May 13, 2025
Jami’ar Maryam Abacha Ta Rufe Ɗakunan Kwanan Ɗalibai Saboda Aikata Rashin Ɗa’a A Kano

Jami’ar Maryam Abacha Ta Rufe Ɗakunan Kwanan Ɗalibai Saboda Aikata Rashin Ɗa’a A Kano

May 13, 2025
China Da Amurka Sun Yarda Da Rage Harajin Kayayyakinsu Domin Sasanta Rikicin Kasuwanci

China Da Amurka Sun Yarda Da Rage Harajin Kayayyakinsu Domin Sasanta Rikicin Kasuwanci

May 13, 2025
Boko Haram Sun Kashe Mutum 12 A Wani Sabon Hari A Borno

Bam Ya Hallaka Ma’aikatan Hukumar Ilimi 2 A Hanyar Damboa-Maiduguri

May 13, 2025
Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027

Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027

May 13, 2025
Nijeriya Ta Biya Dukkanin Bashin IMF Na COVID-19

Nijeriya Ta Biya Dukkanin Bashin IMF Na COVID-19

May 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.