ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Sulhu Da Ƴan Bindiga A Katsina

by Zaharadden Umar
12 months ago
Katsina

Ƙaramar Hukumar Faskari a jihar Katsina ta bi sahun sauran ƙananan hukumomi wajen shirya taron zaman sulhu da ɓarayin daji domin samun zaman lafiya a wannan yanki.

Ita dai ƙaramar hukumar Faskari ita ce ta takwas da ta shiga wannan yarjejeniyar zaman lafiya da ɓarayin daji gwamnatin jihar Katsina ke cewa ba ruwan ta, amma dai zata dauki mataki akan duk wanda ya karya Yarjejeniyar.

Wannan zaman sulhu ya ɗauki hankali fiye da kowane musamman ganin wasu fuskokin manyan ɓarayin daji da suka halarci taron wanda masana ke cewa lallai a sanya hankali da tunani wajen yin wannan yarjejeniya.

ADVERTISEMENT

Daga cikin waɗanda aka ga fuskokin su akwai irin su Ado Aleiro ƴ an kuza da Kachalla Isiya Akwashi Garwa da Babaro wanda ake zargin ya jagoranci kisan massalata fiye da 30 a garin gidan Mantau a watan da ya gabata shine ya halarci taron.

  • ’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa
  • Yadda Ƙananan Hukumomi Ke Yin Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Katsina

Shi dai wannan taron an gudanar da shi a ranar lahadin da ta gabata 14 ga watan Satumba, 2025 a garin Hayin Gada Bilbis bisa waru sharuɗa da aka gindaya.

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

A ɓangaren al’umma an samu halartar shugaban ƙaramar hukumar Faskari Hon. Surajo Aliyu Daudawa da Ɗan Majalisa dokokin mai wakiltar ƙaramar hukumar Faskari injiniya Sama’ila Mu’azu Bawa.

Sauran sun haɗa da Hakimin Faskari da kuma na Mai Ruwa da wakilan al’umma da masu riƙe da masarautar gargajiya da sauran al’umma.

Sai kuma ɓangaren ɓarayin daji inda aka samu halartar manyan jiga-jigan da suka kwarai wajen tada zaune tsaye a yankin Funtua baƙi ɗaya.

Mutane iri su Ado Aleiro Ƴan Kuza da Kachalla Hassan Sarkin Fulani Mai Taru da Kachalla Isiya Akwashi Garwa  da Kachalla Sari da kuma Alhaji Abdullahi da sauran dakarun daji duk sun halarci wannan zaman sulhu.

Rahotanni sun bayyana cewa an cimma wasu sharuɗa kafin a kulla wannan yarjejeniya tsakanin al’ummar ƙaramar hukumar Faskari da kuma su shugabannin ƴ an bindiga kamar haka;

Su Fulani ko ɓarayin daji su daina kashe kowa ko sace jama’a domin yin garkuwa da su a nemi kuɗin fansa a ƙaramar hukumar Faskari

Sannan su Fulani sun amince kowa ya shiga daji ya yi aikin gona da kuma masu saran itacce ko zuwa zumunci a duk inda suke so an amince da haka sannan za su sako waɗanda suka yi garkuwa da su.

Suma a ɓangaen wakilan al’umma sun gindaya cewa an amince ɓarayin daji su shiga ko’ina a ƙaramar hukumar Faskari kamar yadda aba ake yi, amma ba tare da bindiga ko wani makami ba.

Kazalika an amincewa ɓarayin daji su ziyarci asibitoci domin duba lafiyar su ba tare da an tsangwame su ba, sannan su mayar da yaran su makarantar Boko

Abu na ƙarshe a cikin yarjejeniyar shi ne, an amincewa ɓarayin daji su cigaba da mu’amularsu ta yau da kullum kamar cin kasuwa, saye da sayarwa kamar kowa ba tare da wata fargaba ba.

Al’ummar da wannan iftila’i ya shafa sun amince da wannan yarjejeniya wanda suka ce ita ce hanya guda ɗaya da ta rage masu domin su zauna lafiya su da iyalansu.

Wasu kuma na sukar wannan sasanci da cewa to yanzu ina makomar waɗanda aka zalunta aka kashe masu ƴ an uwa da ɓarnata masu dukiyoyi? Suma a bangaren ɓarayin daji sun koka da irin ɓarnar da aka yi masu.

Fatan da ake da shi yanzu shine idan haka zai zama maslaha tsakanin al’umma da kuma ɓarayin daji to Allah ya tabbatar da ɗorewar lamarin a jihar Katsina da arewacin Nijeriya baƙi ɗaya

Katsina
Zaharadden Umar
+ postsBio
    This author does not have any more posts.

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
Next Post
Gwamnatin Tarayya Na Yunƙurin Kawar Da Shanu Daga Titunan Abuja

Gwamnatin Tarayya Na Yunƙurin Kawar Da Shanu Daga Titunan Abuja

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.